< Zabura 119 >

1 Albarka ta tabbata ga waɗanda rayuwarsu ba ta da abin zargi, waɗanda suke tafiya bisa ga dokar Ubangiji.
Heureux ceux dont la voie est intègre, qui suivent la Loi de l’Eternel!
2 Albarka ta tabbata ga waɗanda suke kiyaye ƙa’idodinsa suke kuma nemansa da dukan zuciyarsu.
Heureux ceux qui respectent ses statuts, le recherchent de tout leur cœur,
3 Ba sa yin wani abin da ba daidai ba; suna tafiya a hanyoyinsa.
qui, se gardant bien de commettre aucune injustice, marchent dans ses voies!
4 Ka shimfiɗa farillan da dole a yi biyayya da su.
Tu as promulgué tes ordonnances, pour qu’on les observe strictement.
5 Kash, da a ce hanyoyina tsayayyu ne a yin biyayya da ƙa’idodinka mana!
Ah! puissent mes pas être fermes, pour que j’observe tes préceptes!
6 Da ba zan sha kunya ba sa’ad da na lura da dukan umarnanka.
Alors, je ne serai point déçu, en portant mes regards sur tous tes commandements.
7 Zan yabe ka da zuciya ta gaskiya yayinda nake koyon dokokinka masu adalci.
Je te rendrai grâce en toute droiture de cœur, en m’instruisant des règles de ta justice.
8 Zan yi biyayya da ƙa’idodinka; kada ka yashe ni ɗungum.
Tes statuts, je les observerai: ne m’abandonne en aucun temps.
9 Yaya matashi zai kiyaye hanyarsa da tsabta? Sai ta yin rayuwa bisa ga maganarka.
Comment le jeune homme rendra-t-il pure sa conduite? En se conformant à tes paroles.
10 Na neme ka da dukan zuciyata; kada ka bar ni in kauce daga umarnanka.
De tout mon cœur je m’enquiers de toi, ne me laisse pas dévier de tes prescriptions.
11 Na ɓoye maganarka a cikin zuciyata don kada in yi maka zunubi.
En mon sein j’ai déposé tes instructions, pour ne pas faillir à ton égard.
12 Yabo ya tabbata gare ka, ya Ubangiji; ka koya mini ƙa’idodinka.
Béni sois-tu, ô Eternel! Enseigne-moi tes préceptes.
13 Da leɓunana na ba da labarin dukan dokokin da suka fito bakinka.
De mes lèvres je proclame toutes les règles sorties de ta bouche.
14 Na yi farin ciki da bin farillanka yadda mutum yakan yi farin ciki da arziki mai yawa.
Dans le chemin tracé par tes témoignages je trouve ma joie, comme si c’était le comble de la richesse.
15 Na yi tunani a kan farillanka na kuma lura da hanyoyinka.
Je m’entretiens de tes commandements, et je contemple tes voies.
16 Na yi murna a cikin ƙa’idodinka; ba zan ƙyale maganarka ba.
Je me délecte de tes préceptes, et n’oublie point tes paroles.
17 Ka yi alheri ga bawanka, zan kuwa rayu; zan yi biyayya da maganarka.
Accorde tes bienfaits à ton serviteur, pour que je vive et observe tes paroles.
18 Ka buɗe idanuna don in iya gani abubuwan banmamaki a cikin dokarka.
Dessille-moi les yeux, pour que je puisse contempler les merveilles issues de ta Loi.
19 Ni baƙo ne a duniya; kada ka ɓoye mini umarnanka.
Je suis un simple étranger sur la terre, ne me tiens pas cachés tes commandements.
20 Zuciyata ta ƙosa saboda marmari don dokokinka koyaushe.
Mon âme est travaillée du désir de tes règlements, à toute époque.
21 Ka tsawata wa masu fariya, waɗanda suke la’anta waɗanda kuma suka kauce daga umarnanka.
Toi, tu réprouves les arrogants maudits, qui se fourvoient loin de tes commandements.
22 Ka cire mini ba’a da reni, gama ina kiyaye farillanka.
Affranchis-moi de la honte et du mépris, car je respecte tes témoignages.
23 Ko da yake masu mulki sun zauna tare suna ɓata mini suna, bawanka zai yi tunani a kan ƙa’idodinka.
Dussent même les grands prendre siège et déblatérer contre moi, ton serviteur méditera tes lois.
24 Farillanka ne abin farin cikina; su ne mashawartana.
Oui, tes témoignages sont mes délices, mes meilleurs conseillers.
25 An kwantar da ni ƙasa cikin ƙura; ka kiyaye raina bisa ga maganarka.
Mon âme est collée à la poussière, conserve-moi en vie, suivant ta parole.
26 Na ba da labari hanyoyina ka kuma amsa mini; ka koya mini ƙa’idodinka.
J’Ai exposé ma conduite, et tu m’as répondu; enseigne-moi tes lois.
27 Bari in gane koyarwar farillanka; sa’an nan zan yi tunani a kan abubuwan banmamakinka.
Laisse-moi comprendre le chemin de tes préceptes, et je réfléchirai à tes merveilles.
28 Raina ya gaji da baƙin ciki; ka ƙarfafa ni bisa ga maganarka.
Mon âme, de chagrin, se fond en larmes, redresse-moi, selon ta parole.
29 Ka kiyaye ni daga hanyoyin ruɗu; ka yi mini alheri ta wurin dokokinka.
Eloigne de moi le chemin du mensonge, gratifie-moi de ta Loi.
30 Na zaɓi hanyar gaskiya; na sa zuciyata a kan dokokinka.
J’Ai choisi la voie de la fidélité, placé tes règles sous mes regards.
31 Na riƙe farillanka kankan, ya Ubangiji; kada ka sa in sha kunya.
Je suis attaché à tes statuts, Seigneur, ne m’inflige aucune déception.
32 Ina gudu a kan hanyar umarnanka, gama ka’yantar da zuciyata.
Je suivrai avec empressement le chemin de tes préceptes, car tu élargis mon cœur.
33 Ka koya mini Ya Ubangiji, don in bi ƙa’idodinka; sa’an nan zan kiyaye su har ƙarshe.
Enseigne-moi le chemin de tes préceptes, je veux en suivre les traces.
34 Ka ba ni ganewa, zan kuwa kiyaye dokarka in kuma yi biyayya da ita da dukan zuciyata.
Donne-moi l’intelligence pour que je garde ta loi et l’observe de tout mon cœur.
35 Ka bi da ni a hanyar umarnanka, gama a can zan sami farin ciki.
Dirige-moi dans le sentier de tes commandements, car j’y trouve ma satisfaction.
36 Ka juye zuciyata wajen farillanka ba wajen riba ta sonkai ba.
Incline mon cœur vers tes vérités, et non vers un vain lucre.
37 Ka juye idanuna daga abubuwa marasa amfani; ka kiyaye raina bisa ga maganarka.
Détourne mes yeux de la vue des choses frivoles, fais-moi vivre dans tes voies.
38 Ka cika alkawarinka ga bawanka, saboda a ji tsoronka.
Accomplis ton dire en faveur de ton serviteur, car il amène à te révérer.
39 Ka kawar da shan kunyar da nake tsoro, gama dokokinka nagari ne.
Ecarte de moi la honte que je redoute, car tes jugements sont précieux.
40 Ina marmarin farillanka ƙwarai! Ka kiyaye raina cikin adalcinka.
Voici, j’ai la passion de tes préceptes, fais-moi vivre par ta justice.
41 Bari ƙaunarka marar ƙarewa ta zo gare ni, ya Ubangiji, cetonka bisa ga alkawarinka;
Que tes bontés descendent sur moi, Eternel, ton salut, tel que tu l’as promis.
42 sa’an nan zan amsa wa masu cin mutuncina, gama na dogara ga maganarka.
Je pourrai ainsi répliquer à qui m’outrage, car j’ai confiance en ta parole.
43 Kada ka ƙwace maganarka daga bakina, gama na sa zuciyata a dokokinka.
Ne supprime jamais une parole de vérité de ma bouche, car je mets mon attente en tes jugements.
44 Kullayaumi zan yi biyayya da dokokinka, har abada abadin.
Je veux observer ta Loi constamment, à tout jamais.
45 Zan yi ta yawo a sake gama na nemi farillanka.
Ainsi je circulerai bien au large, car j’aurai eu le souci de tes préceptes.
46 Zan yi maganar farillanka a gaban sarakuna ba kuwa za a kunyata ni ba,
Je ferai de tes vérités l’objet de mes discours, en face des rois, sans aucune fausse honte.
47 gama ina farin ciki da umarnanka saboda ina ƙaunarsu.
Et je ferai mes délices de tes commandements, qui me sont bien chers.
48 Na ɗaga hannuwana ga umarnanka, waɗanda nake ƙauna, ina kuma tunani a kan ƙa’idodinka.
Je tendrai mes mains vers tes commandements, que j’aime, et consacrerai mes méditations à tes préceptes.
49 Tuna da maganarka ga bawanka, gama ka ba ni bege.
Rappelle-toi, en faveur de ton serviteur, la promesse où tu as voulu que je mette mon attente.
50 Ta’aziyyata cikin wahalata ita ce alkawarinka yana kiyaye raina.
C’Est là ma consolation dans la misère, que ta parole me rende la vie.
51 Masu fariya suna yi mini ba’a ba tare da an hana su ba, amma ban rabu da dokar ba.
Des arrogants m’ont raillé au possible: je n’ai point dévié de ta Loi.
52 Na tuna da dokokinka na tun dā, ya Ubangiji, na kuwa sami ta’aziyya a cikinsu.
Je me remémore tes jugements de jadis, ô Eternel, et j’y trouve du réconfort.
53 Fushi ya kama ni saboda mugaye, waɗanda suka keta dokokinka.
Un violent frisson m’avait saisi à cause des méchants, qui abandonnent ta Loi.
54 Ƙa’idodinka su ne kan waƙata a duk inda na sauka.
Mais tes préceptes sont devenus pour moi un sujet de cantiques dans ma demeure passagère.
55 Da dare na tuna da sunanka, ya Ubangiji, zan kuwa kiyaye dokarka.
Je me souviens de ton nom pendant la nuit, Seigneur, et j’observe ta Loi.
56 Wannan shi ne na saba yi, ina yin biyayya da farillanka.
C’Est là mon bonheur à moi, de m’attacher à tes préceptes.
57 Kai ne rabona, ya Ubangiji; na yi alkawarin in kiyaye maganarka.
"C’Est mon lot à moi, ô Eternel, me suis-je dit, d’observer tes paroles."
58 Na nemi fuskarka da dukan zuciyata; ka yi mini alheri bisa ga alkawarinka.
Je t’implore de tout mon cœur, sois-moi propice, selon ta promesse.
59 Na lura da hanyoyina na kuma mayar da matakaina ga farillanka.
J’Ai médité sur mes voies, et ramené mes pas vers tes statuts.
60 Zan gaggauta ba zan ɓata lokaci ba in yi biyayya da umarnanka.
Je me suis empressé, sans perdre un moment, d’observer tes commandements.
61 Ko da yake mugaye sun ɗaura ni da igiyoyi, ba zan manta da dokokinka ba.
Les liens des méchants m’avaient enserré: je n’ai point oublié ta Loi.
62 Da tsakar dare nakan tashi in gode maka saboda dokokinka masu adalci.
Au milieu de la nuit je me lève pour te rendre grâce, à cause de tes équitables jugements.
63 Ni aboki ne ga duk mai tsoronka, ga duk wanda yake bin farillanka.
Je suis l’allié de tous ceux qui te révèrent et qui pratiquent tes lois.
64 Duniya ta cika da ƙaunarka, ya Ubangiji; ka koya mini ƙa’idodinka.
De ta grâce, Eternel, la terre est remplie: enseigne-moi tes préceptes.
65 Ka yi wa bawanka alheri bisa ga maganarka, ya Ubangiji.
Tu as traité avec bienveillance ton serviteur, ô Eternel, conformément à ta parole.
66 Ka koya mini sani da kuma hukunci mai kyau, gama na gaskata a umarnanka.
Enseigne-moi ces choses précieuses: le jugement et la science, car j’ai foi en tes commandements.
67 Kafin in sha wahala na kauce, amma yanzu ina biyayya da maganarka.
Avant que je fusse humilié, je m’égarais; maintenant, je suis attentif à tes discours.
68 Kai nagari ne, kuma abin da kake yi yana da kyau; ka koya mini ƙa’idodinka.
Tu es bon et tu exerces le bien, instruis-moi dans tes préceptes.
69 Ko da yake masu fariya sun shafe ni da ƙarairayi, na kiyaye farillanka da dukan zuciyata.
Des orgueilleux inventent des mensonges contre moi, et moi, de tout cœur, j’observe tes ordonnances.
70 Zukatansu sun yi tauri da kuma marasa tausayi amma ina farin ciki a dokarka.
Leur cœur est bouché comme par la graisse: moi, je fais mes délices de ta Loi.
71 Ya yi kyau da na sha wahala don in koyi ƙa’idodinka.
C’Est un avantage pour moi d’avoir connu la misère, pour mieux apprendre tes préceptes.
72 Doka daga bakinka ya fi mini daraja fiye da azurfa da zinariya guda dubu.
Plus précieux est pour moi l’enseignement de ta bouche que des monceaux de pièces d’or et d’argent.
73 Hannuwanka ne suka yi suka kuma siffanta ni; ka ba ni ganewa don in koyi umarnanka.
Ce sont tes mains qui m’ont formé et organisé, donne-moi l’intelligence pour que j’apprenne à connaître tes commandements.
74 Bari waɗanda suke tsoronka su yi farin ciki sa’ad da suke gan ni, gama na sa zuciyata a maganarka.
Ceux qui te craignent, en me voyant, seront dans la joie, car j’espère en ta parole.
75 Ya Ubangiji na sani, cewa dokokinka masu adalci ne, kuma cikin aminci ka hore ni.
Je sais, ô Seigneur, que tes arrêts sont toute justice, et que c’est en équité que tu m’as humilié.
76 Bari ƙaunarka marar ƙarewa tă yi mini ta’aziyya, bisa ga alkawarinka ga bawanka.
Que ta grâce s’applique donc à me consoler, comme tu l’avais promis à ton serviteur.
77 Bari tausayinka yă zo mini don in rayu, gama dokarka ce farin cikina.
Que ta miséricorde s’étende sur moi et que je vive, puisque ta Loi fait mes délices.
78 Bari masu girman kai su sha kunya saboda abubuwa marasa kyau da suke yi mini ba dalili; amma zan yi tunani a kan farillanka.
Que les orgueilleux soient déçus, pour m’avoir maltraité gratuitement; moi, je méditerai tes préceptes.
79 Bari waɗanda suke tsoronka su juya gare ni, waɗanda suka gane da farillanka.
Que tes adorateurs reviennent à moi, et ceux qui connaissent tes vérités.
80 Bari zuciyata ta kasance marar abin zargi wajen ƙa’idodinka, don kada in sha kunya.
Que mon cœur soit sincèrement attaché à tes lois, afin que je n’aie point à rougir.
81 Raina ya tafke da marmari don cetonka, amma na sa zuciyata a maganarka.
Mon âme languit après ton secours, c’est en ta parole que je mets mon espoir.
82 Idanuna sun gaji, suna jiran alkawarinka; Na ce, “Yaushe za ka ta’azantar da ni?”
Mes yeux se consument dans l’attente de ta parole, tandis que je dis: "Quand me consoleras-tu?"
83 Ko da yake ni kamar salkar ruwan inabi ne a cikin hayaƙi, ban manta da ƙa’idodinka ba.
Car je suis comme une outre dans des flots de fumée: tes préceptes, je ne les ai point oubliés.
84 Har yaushe bawanka zai yi ta jira? Yaushe za ka hukunta masu tsananta mini?
Que dureront les jours de ton serviteur? Quand feras-tu justice de mes persécuteurs?
85 Masu girman kai sun haƙa mini rami, sun ƙetare dokarka.
Des pervers m’ont creusé des fosses, au mépris de ta Loi.
86 Dukan umarnanka abin dogara ne; ka taimake ni, gama mutane suna tsananta mini ba dalili.
Tous tes commandements sont loyauté parfaite, eux me pourchassent sans motif: viens à mon aide.
87 Sun kusa gama da ni a duniya, amma ban bar bin farillanka ba.
Peu s’en faut qu’ils ne m’aient anéanti sur terre, alors que moi, je n’ai point délaissé tes préceptes.
88 Ka kiyaye raina bisa ga ƙaunarka, zan kuwa yi biyayya da farillan bakinka.
Fidèle à ta bonté, conserve-moi en vie, et je respecterai le témoignage de ta bouche.
89 Maganarka, ya Ubangiji madawwamiya ce; tana nan daram a cikin sammai.
Pour l’éternité, Seigneur, ta parole demeure immuable dans les cieux.
90 Amincinka yana cin gaba cikin dukan zamanai; ka kafa duniya ta kuma dawwama.
D’Âge en âge dure ta fidélité: tu as affermi la terre, et elle est inébranlable.
91 Dokokinka sun dawwama har yă zuwa yau, gama dukan abubuwa suna maka hidima.
Selon tes lois, les êtres subsistent aujourd’hui, car ils sont tous tes serviteurs.
92 Da ba don dokarka ce farin cikina ba, da na hallaka a cikin azabana.
Si ta Loi n’avait fait mes délices, j’aurais succombé dans ma misère.
93 Ba zan taɓa manta da farillanka ba, gama ta wurinsu ne ka kiyaye raina.
Jamais je n’oublierai tes préceptes, car par eux tu m’assures la vie.
94 Ka cece ni, gama ni naka ne; na yi ƙoƙarin neman farillanka.
Je suis à toi, prête-moi secours, car je m’enquiers de tes ordres.
95 Mugaye suna jira su hallaka ni, amma zan yi ta tunani a kan farillanka.
Des méchants me guettent pour me perdre: je cherche à pénétrer le sens de tes prescriptions.
96 Ga duk cikakke na ga kāsawa; amma umarnanka ba su da iyaka.
A tout bien j’ai vu des limites: ta Loi est infiniment vaste.
97 Kash, ga yadda nake ƙaunar dokarka! Ina tunani a kanta dukan yini.
Combien j’aime ta Loi! Tout le temps elle est l’objet de mes méditations.
98 Umarnanka suna sa in zama mai hikima fiye da abokan gābana, gama kullum suna tare da ni.
Tes commandements me rendent plus sage que mes ennemis, car ils sont pour moi un bien inépuisable.
99 Ina da ganewa sosai fiye da dukan malamaina, gama ina tunani a kan farillanka.
Je suis plus avisé que tous mes précepteurs, car tes vérités sont le thème de mes réflexions.
100 Ina da ganewa fiye da dattawa, gama ina biyayya da farillanka.
J’Ai plus d’expérience que les vieillards, car je respecte tes préceptes.
101 Na kiyaye ƙafafuna daga kowace muguwar hanya domin in yi biyayya da maganarka.
J’Ai tenu mes pas éloignés de tout mauvais chemin, en vue d’observer tes paroles.
102 Ban rabu da dokokinka ba, gama kai da kanka ne ka koya mini.
Je n’ai point dévié de tes règles, car c’est toi qui m’as instruit.
103 Ɗanɗanon maganarka akwai zaki, sun ma fi zuma zaki a bakina!
Que tes paroles sont douces à mon palais! Le miel l’est moins à ma bouche.
104 Na sami ganewa daga farillanka; saboda haka ina ƙin kowace hanyar da ba daidai ba.
J’Ai puisé mon savoir dans tes préceptes, c’est pourquoi je hais toute voie mensongère.
105 Maganarka fitila ce ga ƙafafuna haske kuma a kan hanyata.
Ta parole est un flambeau qui éclaire mes pas, une lumière qui rayonne sur ma route.
106 Na yi rantsuwa na kuma tabbatar da shi, cewa zan bi dokokinka masu adalci.
J’Ai fait le serment, et je le tiendrai, d’observer les règles de ta justice.
107 Na sha wahala sosai; ka kiyaye raina, ya Ubangiji, bisa ga maganarka.
Je suis extrêmement accablé, Eternel, conserve-moi en vie selon ta parole.
108 Ka karɓi yabon bakina da nake yi da yardar rai, ya Ubangiji, ka kuwa koya mini dokokinka.
Agrée de grâce, Seigneur, les vœux de ma bouche, et enseigne-moi tes lois.
109 Ko da yake kullum ina riƙe da raina a hannuwana, ba zan manta da dokarka ba.
Mon âme court sans cesse des dangers, et je n’ai point oublié ta loi.
110 Mugaye sun kafa mini tarko, amma ban kauce daga farillanka ba.
Des méchants me dressent des pièges, pourtant je ne dévie point de tes préceptes.
111 Farillanka su ne gādona har abada; su ne farin cikin zuciyata.
Je reste pour toujours en possession de tes vérités, car elles sont la joie de mon cœur.
112 Zuciyata ta shirya a kan kiyaye ƙa’idodinka har ƙarshe.
J’Ai incliné mon cœur à accomplir tes lois à tout jamais, jusqu’à la fin dernière.
113 Na ƙi mutane masu baki biyu, amma ina ƙauna dokarka.
Je hais les gens à double face, mais ta Loi, je l’aime.
114 Kai ne mafakata da garkuwata; na sa zuciyata a maganarka.
Tu es mon abri et mon bouclier, j’espère en ta parole.
115 Ku rabu da ni, ku masu aikata mugunta, don in kiyaye umarnan Allahna!
Loin de moi, ô malfaiteurs! Je veux observer les commandements de mon Dieu.
116 Ka raya ni bisa ga alkawarinka, zan kuwa rayu; kada ka bari a gwale sa zuciyata.
Soutiens-moi selon ta promesse pour que je vive, et ne laisse pas mon espoir se changer en déception.
117 Ka riƙe ni za a kuma cece ni; kullayaumi zan ɗauka ƙa’idodinka da muhimmanci.
Accorde-moi ton appui pour que je sois sauvé, je me tournerai sans cesse vers tes lois.
118 Ka ki dukan waɗanda suka kauce daga ƙa’idodinka, gama yaudararsu banza ne.
Tu foules aux pieds ceux qui errent loin de tes préceptes, car leurs ruses habiles ne sont que mensonge.
119 Dukan mugayen duniya ka zubar kamar datti; saboda haka nake ƙaunar farillanka.
Comme des scories, tu élimines tous les méchants sur terre, c’est pourquoi j’aime tes vérités.
120 Naman jikina na rawan jiki don tsoronka; na cika da tsoron dokokinka.
Ma chair frissonne de la terreur que tu inspires, et je redoute tes jugements.
121 Na aikata abin da yake mai adalci da kuma daidai; kada ka ni a hannun masu danne ni.
J’Ai pratiqué la justice et l’équité, ne m’abandonne pas à mes oppresseurs.
122 Ka tabbatar da lafiyar bawanka; kada ka bar masu girman kai su danne ni.
Interviens pour le bonheur de ton serviteur, que des arrogants ne m’accablent point.
123 Idanuna sun gaji, da jiran cetonka, da jiran alkawarinka mai adalci.
Mes yeux languissent après ton secours, et après ta parole de salut.
124 Ka yi da bawanka bisa ga ƙaunarka ka kuma koya mini ƙa’idodinka.
Traite ton serviteur selon ta grâce, et enseigne-moi tes préceptes.
125 Ni bawanka ne, ka ba ni fahimi don in gane farillanka.
Je suis ton serviteur, donne-moi la sagacité, pour que je comprenne tes vérités.
126 Lokaci ya yi da za ka yi wani abu, ya Ubangiji; ana karya dokarka.
Le temps est venu d’agir pour l’Eternel: on a violé ta Loi.
127 Saboda ina ƙaunar umarnanka fiye da zinariya, kai, fiye da zinariya zalla,
C’Est pourquoi j’aime tes commandements, plus que l’or et le métal fin.
128 saboda kuma ina lura da dukan farillanka da kyau, na ƙi kowace hanyar da ba daidai ba.
C’Est pourquoi je reconnais la parfaite droiture de tous tes préceptes, et déteste toute voie mensongère.
129 Farillanka masu banmamaki ne; saboda haka nake yin biyayya da su.
Merveilleux sont tes statuts, aussi mon âme les garde-t-elle avec soin.
130 Fassarar maganganunka sukan ba da haske; sukan ba da ganewa ga marar ilimi.
La révélation de tes paroles projette de la lumière, donne de l’intelligence aux simples.
131 Ina hakkin da bakina a buɗe, ina marmarin umarnanka.
J’Ouvre largement la bouche pour aspirer, car j’ai la passion de tes commandements.
132 Ka juye wurina ka kuma yi mini jinƙai, yadda kullum ka yi wa waɗanda suke ƙaunar sunanka.
Tourne-toi vers moi et sois-moi propice, comme tu le fais pour ceux qui aiment ton nom.
133 Ka bi da sawuna bisa ga maganarka; kada ka bar zunubi yă mallake ni.
Affermis mes pas par tes discours, qu’aucune mauvaise passion ne prenne le dessus sur moi.
134 Ka fanshe ni daga mutane masu danniya, don in yi biyayya da farillanka.
Délivre-moi de l’oppression des hommes, pour que je puisse observer tes préceptes.
135 Ka sa fuskarka ta haskaka a kan bawanka ka kuma koya mini ƙa’idodinka.
Fais luire ta face sur ton serviteur, et enseigne-moi tes préceptes.
136 Hawaye suna malalowa daga idanuna kamar rafi, gama ba a biyayya da dokarka.
Mes yeux ont versé des torrents de larmes, parce qu’on n’observe pas ta Loi.
137 Mai adalci ne kai, ya Ubangiji, dokokinka kuma daidai ne.
Tu es juste, ô Seigneur, et équitables sont tes jugements.
138 Farillan da ka shimfiɗa masu adalci ne; su kuma abin dogara ne ƙwarai.
Tu as imposé tes justes ordonnances: elles sont tout à fait infaillibles.
139 Kishina ya cinye ni ɗungum, gama abokan gābana sun yi biris da maganganunka.
Je suis consumé par mon zèle jaloux, car mes adversaires oublient tes paroles.
140 An gwada alkawuranka sarai, bawanka kuwa yana ƙaunarsu.
Ta parole est infiniment épurée, elle est chère à ton serviteur.
141 Ko da yake ni ba kome ba ne an kuwa rena ni, ba na manta da farillanka.
Je suis chétif et méprisé: tes préceptes, je ne les ai point oubliés.
142 Adalcinka dawwammame ne dokar kuma gaskiya ce.
Ta justice est éternellement équitable, et ta Loi est vérité.
143 Wahala da damuwa suna a kaina, amma umarnanka su ne farin cikina.
La détresse et l’angoisse m’ont atteint: tes commandements sont mes délices.
144 Farillanka daidai ne har abada; ka ba ni ganewa don in rayu.
Tes statuts sont à jamais équitables, permets-moi de les comprendre, pour que je vive.
145 Na yi kira da dukan zuciyata; ka amsa mini, ya Ubangiji, zan kuwa yi biyayya da ƙa’idodinka.
Je t’invoque de tout cœur, exauce-moi, Seigneur! Je veux observer tes préceptes.
146 Na yi kira gare ka; ka cece ni zan kuwa kiyaye farillanka.
Je t’appelle, viens à mon secours, et je garderai tes statuts.
147 Na tashi kafin fitowar rana na kuma yi kukan neman taimako; na sa zuciyata a maganarka.
Dès l’aurore je m’empresse d’implorer, j’espère en ta parole.
148 Ban rufe idanuna ba dukan dare, don in yi tunani a kan alkawuranka.
Mes yeux devancent les veilles de la nuit, pour méditer ta parole.
149 Ka ji muryata bisa ga ƙaunarka; ka kiyaye raina, ya Ubangiji, bisa ga dokokinka.
Daigne écouter ma voix, selon ta bonté, Eternel; fais-moi vivre selon l’arrêt de ta justice.
150 Waɗanda suke ƙirƙiro mugayen dabaru suna nan kusa, amma suna nesa da dokarka.
Ils m’approchent, ceux qui courent après l’infamie, il s’éloignent de ta Loi.
151 Duk da haka kana kusa, ya Ubangiji, kuma dukan umarnanka gaskiya ne.
Toi, Seigneur, tu es près de moi, tous tes commandements sont vérité.
152 Tun tuni na koyi daga farillanka cewa ka kafa su su kasance har abada.
Dès longtemps j’avais connaissance de tes statuts, car tu les as établis pour l’éternité.
153 Ka dubi wahalata ka cece ni, gama ban manta da dokarka ba.
Vois ma misère et tire-moi du danger, car je n’ai pas oublié ta Loi.
154 Ka kāre manufata ka kuma fanshe ni, ka cece rai na kamar yadda ka alkawarta!
Prends en main ma cause et délivre-moi, fais-moi vivre pour me consacrer à ta parole.
155 Ceto yana nesa da mugaye, gama ba sa neman ƙa’idodinka.
Le salut est loin des méchants, car ils ne se soucient pas de tes préceptes.
156 Tausayinka da girma yake, ya Ubangiji; ka kiyaye raina bisa ga dokokinka.
Grande est ta miséricorde, Eternel, fais-moi vivre selon l’arrêt de ta justice.
157 Maƙiya masu yawa ne suke tsananta mini, amma ban rabu da farillanka ba.
Nombreux sont mes persécuteurs et mes ennemis; je n’ai point dévié de tes statuts.
158 Na dubi marasa aminci da ƙyama, gama ba sa yin biyayya da maganarka.
J’Ai observé les traîtres et j’en ai été écœuré, car ils ne respectent pas ta parole.
159 Dubi yadda nake ƙaunar farillanka; ka kiyaye raina, ya Ubangiji, bisa ga ƙaunarka.
Vois comme j’aime tes prescriptions, Seigneur, selon ta bonté, fais-moi vivre.
160 Dukan maganganunka gaskiya ne; dukan dokokinka masu adalci madawwami ne.
L’Ensemble de tes paroles est vérité, éternels sont tous les arrêts de ta justice.
161 Masu mulki suna tsananta mini ba dalili, amma zuciyata na rawan jiki game da maganarka.
Des grands me persécutent gratuitement, et mon cœur tremble devant ta parole.
162 Ina farin ciki da alkawarinka kamar yadda wani kan sami ganima mai girma.
Je me réjouis de tes promesses, comme quelqu’un qui a trouvé un riche butin.
163 Na ƙi ina kuma ƙyamar ƙarya amma ina ƙaunar dokarka.
Je hais le mensonge, je l’ai en horreur, c’est ta Loi que j’aime.
164 Sau bakwai a rana ina yabonka saboda dokokinka masu adalci.
Sept fois par jour je célèbre tes louanges, en raison de tes justes arrêts.
165 Waɗanda suke ƙaunar dokarka suna da babban salama, kuma babu abin da zai sa su yi tuntuɓe.
Un grand bonheur attend ceux qui aiment ta Loi: pour eux point de cause de chute.
166 Ina jiran cetonka, ya Ubangiji, ina kuma bin umarnanka.
J’Ai pleine confiance en ton secours, Seigneur, et j’accomplis tes commandements.
167 Ina biyayya da farillanka, gama ina ƙaunarsu ƙwarai.
Mon âme observe tes témoignages, je les aime infiniment.
168 Ina biyayya da farillanka da kuma koyarwarka, gama dukan hanyoyina sanannu ne gare ka.
J’Observe tes prescriptions et tes statuts, car toutes mes voies sont sous tes regards.
169 Bari kukata ta zo gare ka, ya Ubangiji; ka ba ni ganewa bisa ga maganarka.
Que mon hymne arrive jusqu’à toi, Eternel, fais-moi comprendre le sens de ta parole.
170 Bari roƙona yă zo gabanka; ka cece ni bisa ga alkawarinka.
Que ma supplication vienne devant toi, sauve-moi selon ta promesse.
171 Bari leɓunana su cika da yabonka, gama ka koya mini ƙa’idodinka.
Mes lèvres laisseront s’échapper tes louanges, car tu m’enseignes tes préceptes.
172 Bari harshena yă rera game da maganarka, gama dukan umarnanka masu adalci ne.
Ma langue chantera ta parole, car tous tes commandements sont équité.
173 Bari hannunka yă kasance a shirye don yă taimake ni, gama na zaɓi farillanka.
Puisse ta main s’appliquer à me secourir, puisque j’ai fait choix de tes prescriptions!
174 Ina marmarin cetonka, ya Ubangiji, dokarka kuwa ita ce farin cikina.
J’Aspire à ton secours, Eternel, et ta Loi fait mes délices.
175 Bari in rayu don in yabe ka, bari kuma dokokinka su raya ni.
Que mon âme vive pour te louer, que tes jugements soient mon soutien.
176 Na kauce kamar ɓatacciyar tunkiya. Ka nemi bawanka, gama ban manta da umarnanka ba.
J’Erre comme une brebis égarée; mets-toi à la recherche de ton serviteur! Car je n’ai pas oublié tes commandements.

< Zabura 119 >