< Zabura 119 >

1 Albarka ta tabbata ga waɗanda rayuwarsu ba ta da abin zargi, waɗanda suke tafiya bisa ga dokar Ubangiji.
[ALEPH.] How happy the men of blameless life, who walk in the law of Yahweh.
2 Albarka ta tabbata ga waɗanda suke kiyaye ƙa’idodinsa suke kuma nemansa da dukan zuciyarsu.
How happy they who observe his testimonies, with a whole heart, they seek him.
3 Ba sa yin wani abin da ba daidai ba; suna tafiya a hanyoyinsa.
Yea, they have not wrought perversity, In his ways, have they walked.
4 Ka shimfiɗa farillan da dole a yi biyayya da su.
Thou, hast commanded thy precepts, that they should be diligently kept.
5 Kash, da a ce hanyoyina tsayayyu ne a yin biyayya da ƙa’idodinka mana!
Oh would that my ways might be settled! that I might keep thy statutes.
6 Da ba zan sha kunya ba sa’ad da na lura da dukan umarnanka.
Then, shall I not be ashamed, when I have respect unto all thy commandments.
7 Zan yabe ka da zuciya ta gaskiya yayinda nake koyon dokokinka masu adalci.
I will thank thee with uprightness of heart, when I have learned thy righteous regulations.
8 Zan yi biyayya da ƙa’idodinka; kada ka yashe ni ɗungum.
Thy statutes, will I keep, Do not thou forsake me utterly.
9 Yaya matashi zai kiyaye hanyarsa da tsabta? Sai ta yin rayuwa bisa ga maganarka.
[BETH.] Wherewithal can a young man keep pure his way? By taking heed, according to thy word.
10 Na neme ka da dukan zuciyata; kada ka bar ni in kauce daga umarnanka.
With all my heart, have I sought thee, Suffer me not to be led astray from thy commandments.
11 Na ɓoye maganarka a cikin zuciyata don kada in yi maka zunubi.
In my heart, have I treasured what thou hast said, to the end I may not sin against thee.
12 Yabo ya tabbata gare ka, ya Ubangiji; ka koya mini ƙa’idodinka.
Blessed art thou, O Yahweh—Teach me thy statutes.
13 Da leɓunana na ba da labarin dukan dokokin da suka fito bakinka.
With my lips, have I recounted All the regulations of thy mouth.
14 Na yi farin ciki da bin farillanka yadda mutum yakan yi farin ciki da arziki mai yawa.
In the way of thy testimonies, have I rejoiced, Like as over all riches.
15 Na yi tunani a kan farillanka na kuma lura da hanyoyinka.
In thy precepts, will I meditate, that I may discern thy paths.
16 Na yi murna a cikin ƙa’idodinka; ba zan ƙyale maganarka ba.
In thy statutes, will I find my dear delight, I will not forget thy word.
17 Ka yi alheri ga bawanka, zan kuwa rayu; zan yi biyayya da maganarka.
[GIMEL.] Bestow thy bounties upon thy servant—let me live, That I may observe thy word.
18 Ka buɗe idanuna don in iya gani abubuwan banmamaki a cikin dokarka.
Unveil thou mine eyes, that I may discern Wondrous things out of thy law.
19 Ni baƙo ne a duniya; kada ka ɓoye mini umarnanka.
A sojourner, am, I, in the earth, Do not hide from me, thy commandments.
20 Zuciyata ta ƙosa saboda marmari don dokokinka koyaushe.
My soul is crushed with longing for thy just decisions at all times.
21 Ka tsawata wa masu fariya, waɗanda suke la’anta waɗanda kuma suka kauce daga umarnanka.
Thou hast rebuked the proud as accursed, who stray from thy commandments.
22 Ka cire mini ba’a da reni, gama ina kiyaye farillanka.
Roll from off me, reproach and contempt, For, thy testimonies, have I observed.
23 Ko da yake masu mulki sun zauna tare suna ɓata mini suna, bawanka zai yi tunani a kan ƙa’idodinka.
Even rulers have taken their seat, against me, have talked, Thy servant, will still meditate in thy statutes.
24 Farillanka ne abin farin cikina; su ne mashawartana.
Yea, thy testimonies, are my dear delight, My counsellors.
25 An kwantar da ni ƙasa cikin ƙura; ka kiyaye raina bisa ga maganarka.
[DALETH.] My soul, cleaveth to the dust, Give me life, according to thy word.
26 Na ba da labari hanyoyina ka kuma amsa mini; ka koya mini ƙa’idodinka.
My ways, I recounted, and thou didst answer me, Teach me thy statutes.
27 Bari in gane koyarwar farillanka; sa’an nan zan yi tunani a kan abubuwan banmamakinka.
The way of thy precepts, cause thou me to understand, and I will indeed meditate in thy wonders.
28 Raina ya gaji da baƙin ciki; ka ƙarfafa ni bisa ga maganarka.
My soul weepeth itself away, for grief, Confirm thou me, according to thy word.
29 Ka kiyaye ni daga hanyoyin ruɗu; ka yi mini alheri ta wurin dokokinka.
The way of falsehood, take thou from me, and, with thy law, O favour me.
30 Na zaɓi hanyar gaskiya; na sa zuciyata a kan dokokinka.
The way of faithfulness, have I chosen, Thy regulations, have I deemed right.
31 Na riƙe farillanka kankan, ya Ubangiji; kada ka sa in sha kunya.
I have kept close to thy testimonies, O Yahweh! do not put me to shame.
32 Ina gudu a kan hanyar umarnanka, gama ka’yantar da zuciyata.
The way of thy commandments, will I run, for thou wilt enlarge my heart.
33 Ka koya mini Ya Ubangiji, don in bi ƙa’idodinka; sa’an nan zan kiyaye su har ƙarshe.
[HE.] Point out to me, O Yahweh, the way of thy statutes, that I may observe it unto the end.
34 Ka ba ni ganewa, zan kuwa kiyaye dokarka in kuma yi biyayya da ita da dukan zuciyata.
Give me understanding, that I may observe thy law, that I may keep it with a whole heart.
35 Ka bi da ni a hanyar umarnanka, gama a can zan sami farin ciki.
Guide me in the path of thy commandments, for, therein, do I find pleasure.
36 Ka juye zuciyata wajen farillanka ba wajen riba ta sonkai ba.
Incline my heart unto thy testimonies, and not unto unjust gain.
37 Ka juye idanuna daga abubuwa marasa amfani; ka kiyaye raina bisa ga maganarka.
Turn away mine eyes, from beholding vanity, In thy way, give me life.
38 Ka cika alkawarinka ga bawanka, saboda a ji tsoronka.
Establish, unto thy servant, thy word, which pertaineth to the reverence of thee.
39 Ka kawar da shan kunyar da nake tsoro, gama dokokinka nagari ne.
Cause to pass away my reproach, that I have feared, for, thy regulations, are good.
40 Ina marmarin farillanka ƙwarai! Ka kiyaye raina cikin adalcinka.
Lo! I have longed for thy precepts, In thy righteousness, give me life.
41 Bari ƙaunarka marar ƙarewa ta zo gare ni, ya Ubangiji, cetonka bisa ga alkawarinka;
[WAW.] And let thy lovingkindness reach me, O Yahweh, thy salvation, according to thy word.
42 sa’an nan zan amsa wa masu cin mutuncina, gama na dogara ga maganarka.
So shall I have something to answer him that reproacheth me, That I have trusted in thy word.
43 Kada ka ƙwace maganarka daga bakina, gama na sa zuciyata a dokokinka.
And do not snatch away from my mouth the word of truth in any wise, because, for thy regulation, have I waited.
44 Kullayaumi zan yi biyayya da dokokinka, har abada abadin.
That I may keep thy law continually, to times age-abiding and beyond.
45 Zan yi ta yawo a sake gama na nemi farillanka.
That I may walk to and fro in a large place, because, thy precepts, have I sought.
46 Zan yi maganar farillanka a gaban sarakuna ba kuwa za a kunyata ni ba,
That I may speak of thy testimonies before kings, and not be ashamed.
47 gama ina farin ciki da umarnanka saboda ina ƙaunarsu.
That I may find dear delight in thy commandments, which I have loved.
48 Na ɗaga hannuwana ga umarnanka, waɗanda nake ƙauna, ina kuma tunani a kan ƙa’idodinka.
That I may lift up my hands unto thy commandments, which I have loved, and may meditate in thy statutes.
49 Tuna da maganarka ga bawanka, gama ka ba ni bege.
[ZAYIN.] Remember the word unto thy servant, upon which thou hast caused me to hope.
50 Ta’aziyyata cikin wahalata ita ce alkawarinka yana kiyaye raina.
This, is my comfort in mine affliction, that, thy word, hath given me life.
51 Masu fariya suna yi mini ba’a ba tare da an hana su ba, amma ban rabu da dokar ba.
Insolent men, have derided me exceedingly, From thy law, have I not swerved.
52 Na tuna da dokokinka na tun dā, ya Ubangiji, na kuwa sami ta’aziyya a cikinsu.
I have remembered thy regulations, [which have come down] from age-past times, O Yahweh, and have consoled myself.
53 Fushi ya kama ni saboda mugaye, waɗanda suka keta dokokinka.
A raging heat, hath seized me, by reason of the lawless, who forsake thy law.
54 Ƙa’idodinka su ne kan waƙata a duk inda na sauka.
Songs, have thy statutes become to me, in my house of sojourn.
55 Da dare na tuna da sunanka, ya Ubangiji, zan kuwa kiyaye dokarka.
I have remembered, in the night, thy Name, O Yahweh, and have kept thy law.
56 Wannan shi ne na saba yi, ina yin biyayya da farillanka.
This, have I had, because, thy precepts, have I observed.
57 Kai ne rabona, ya Ubangiji; na yi alkawarin in kiyaye maganarka.
[HETH.] My portion, is Yahweh, I have promised that I would keep thy words.
58 Na nemi fuskarka da dukan zuciyata; ka yi mini alheri bisa ga alkawarinka.
I have sought the smile of thy face with all my heart, Show me favour, according to thy word.
59 Na lura da hanyoyina na kuma mayar da matakaina ga farillanka.
I have thought upon my ways, and have turned my feet unto thy testimonies.
60 Zan gaggauta ba zan ɓata lokaci ba in yi biyayya da umarnanka.
I have hastened, and not delayed, to keep thy commandments.
61 Ko da yake mugaye sun ɗaura ni da igiyoyi, ba zan manta da dokokinka ba.
The meshes of the lawless, have surrounded me, Thy law, have I not forgotten.
62 Da tsakar dare nakan tashi in gode maka saboda dokokinka masu adalci.
At midnight, I arise to give thanks unto thee, For thy righteous regulations.
63 Ni aboki ne ga duk mai tsoronka, ga duk wanda yake bin farillanka.
Companion, am I, to all who revere thee, and to them who keep thy precepts.
64 Duniya ta cika da ƙaunarka, ya Ubangiji; ka koya mini ƙa’idodinka.
Of thy lovingkindness, O Yahweh, the earth, is full, Thy statutes, teach thou me.
65 Ka yi wa bawanka alheri bisa ga maganarka, ya Ubangiji.
[TETH.] Well, hast thou dealt with thy servant, O Yahweh, according to thy word.
66 Ka koya mini sani da kuma hukunci mai kyau, gama na gaskata a umarnanka.
Good judgment and knowledge, teach thou me, For, in thy commandments, have I trusted.
67 Kafin in sha wahala na kauce, amma yanzu ina biyayya da maganarka.
Before I was afflicted, I myself was going astray, but, now, thy word, have I kept.
68 Kai nagari ne, kuma abin da kake yi yana da kyau; ka koya mini ƙa’idodinka.
Good, thou art, and doing good, Teach me thy statutes.
69 Ko da yake masu fariya sun shafe ni da ƙarairayi, na kiyaye farillanka da dukan zuciyata.
Insolent men have plastered falsehood over me, I, with a whole heart, will observe thy precepts.
70 Zukatansu sun yi tauri da kuma marasa tausayi amma ina farin ciki a dokarka.
Gross, like fat, is their heart, I, in thy law, have found dear delight.
71 Ya yi kyau da na sha wahala don in koyi ƙa’idodinka.
It is, well for me, that I was afflicted, That I might learn thy statutes.
72 Doka daga bakinka ya fi mini daraja fiye da azurfa da zinariya guda dubu.
Better to me, is the law of thy mouth, than thousands of gold and silver.
73 Hannuwanka ne suka yi suka kuma siffanta ni; ka ba ni ganewa don in koyi umarnanka.
[YODH.] Thine own hands, have made me, and formed me. Give me understanding, that I may learn thy commandments.
74 Bari waɗanda suke tsoronka su yi farin ciki sa’ad da suke gan ni, gama na sa zuciyata a maganarka.
They who revere thee, shall see me and rejoice, that, for thy word, I waited.
75 Ya Ubangiji na sani, cewa dokokinka masu adalci ne, kuma cikin aminci ka hore ni.
I know, O Yahweh, that righteous are thy regulations, and, in faithfulness, didst thou afflict me.
76 Bari ƙaunarka marar ƙarewa tă yi mini ta’aziyya, bisa ga alkawarinka ga bawanka.
Let thy lovingkindness, I beseech thee, serve to comfort me, according to thy word to thy servant.
77 Bari tausayinka yă zo mini don in rayu, gama dokarka ce farin cikina.
Let thy compassions reach me, that I may live, for, thy law, is my dear delight.
78 Bari masu girman kai su sha kunya saboda abubuwa marasa kyau da suke yi mini ba dalili; amma zan yi tunani a kan farillanka.
Let insolent men, be ashamed, because, by means of falsehood, they have dealt with me perversely, I, will meditate in thy precepts.
79 Bari waɗanda suke tsoronka su juya gare ni, waɗanda suka gane da farillanka.
Let them who revere thee, turn unto me, even they who know thy testimonies.
80 Bari zuciyata ta kasance marar abin zargi wajen ƙa’idodinka, don kada in sha kunya.
Let my heart be thorough in thy statutes, that I may not be ashamed.
81 Raina ya tafke da marmari don cetonka, amma na sa zuciyata a maganarka.
[KAPH.] My soul, hath languished for thy salvation, For thy word, have I hoped.
82 Idanuna sun gaji, suna jiran alkawarinka; Na ce, “Yaushe za ka ta’azantar da ni?”
Mine eyes have failed for thy word, saying, When wilt thou comfort me?
83 Ko da yake ni kamar salkar ruwan inabi ne a cikin hayaƙi, ban manta da ƙa’idodinka ba.
Though I have been like a wine-skin in the smoke, thy statutes, have I not forgotten.
84 Har yaushe bawanka zai yi ta jira? Yaushe za ka hukunta masu tsananta mini?
How few are the days of thy servant! When wilt thou execute sentence on my persecutors?
85 Masu girman kai sun haƙa mini rami, sun ƙetare dokarka.
Insolent men digged for me pits, men who are not according to thy law.
86 Dukan umarnanka abin dogara ne; ka taimake ni, gama mutane suna tsananta mini ba dalili.
All thy commandments, are faithful, With falsehood, have they persecuted me, O help me!
87 Sun kusa gama da ni a duniya, amma ban bar bin farillanka ba.
A little more, and they had consumed me in the earth, but, I, forsake not thy precepts.
88 Ka kiyaye raina bisa ga ƙaunarka, zan kuwa yi biyayya da farillan bakinka.
According to thy lovingkindness, give thou me life, so will I keep the testimonies of thy mouth.
89 Maganarka, ya Ubangiji madawwamiya ce; tana nan daram a cikin sammai.
[LAMED.] Age-abidingly, O Yahweh, hath thy word been set up in the heavens.
90 Amincinka yana cin gaba cikin dukan zamanai; ka kafa duniya ta kuma dawwama.
To generation after generation, is thy faithfulness, Thou hast established the earth, and it standeth.
91 Dokokinka sun dawwama har yă zuwa yau, gama dukan abubuwa suna maka hidima.
By thy regulations, do they stand to-day, for, all, are thy servants.
92 Da ba don dokarka ce farin cikina ba, da na hallaka a cikin azabana.
Had not thy law been my dear delight, then, had I perished in mine affliction.
93 Ba zan taɓa manta da farillanka ba, gama ta wurinsu ne ka kiyaye raina.
Unto times age-abiding, will I not forget thy precepts, For, by them, hast thou given me life.
94 Ka cece ni, gama ni naka ne; na yi ƙoƙarin neman farillanka.
Thine, am I, —oh save me! For, thy precepts, have I sought.
95 Mugaye suna jira su hallaka ni, amma zan yi ta tunani a kan farillanka.
For me, have the lawless waited, to destroy me, Thy testimonies, will I diligently consider.
96 Ga duk cikakke na ga kāsawa; amma umarnanka ba su da iyaka.
To all perfection, have I seen an end, Broad is thy commandment, exceedingly.
97 Kash, ga yadda nake ƙaunar dokarka! Ina tunani a kanta dukan yini.
[MEM.] Oh how I love thy law! All the day, is it my (meditation)
98 Umarnanka suna sa in zama mai hikima fiye da abokan gābana, gama kullum suna tare da ni.
Beyond mine enemies, will thy commandment make me wise, for, age-abidingly, shall it be mine.
99 Ina da ganewa sosai fiye da dukan malamaina, gama ina tunani a kan farillanka.
Beyond all my teachers, have I shown discretion, for, thy testimonies, are my (meditation)
100 Ina da ganewa fiye da dattawa, gama ina biyayya da farillanka.
Beyond the elders, will I show understanding, for, thy precepts, have I observed.
101 Na kiyaye ƙafafuna daga kowace muguwar hanya domin in yi biyayya da maganarka.
From every way of wickedness, have I withheld my feet, that I might keep thy word.
102 Ban rabu da dokokinka ba, gama kai da kanka ne ka koya mini.
From thy regulations, have I not turned aside, for, thou, hast directed me.
103 Ɗanɗanon maganarka akwai zaki, sun ma fi zuma zaki a bakina!
How smooth to my palate is thy speech, More than honey, to my mouth.
104 Na sami ganewa daga farillanka; saboda haka ina ƙin kowace hanyar da ba daidai ba.
Out of thy precepts, will I get understanding, For this cause, do I hate every false way.
105 Maganarka fitila ce ga ƙafafuna haske kuma a kan hanyata.
[NUN.] A lamp to my feet, is thy word, and a light to my path.
106 Na yi rantsuwa na kuma tabbatar da shi, cewa zan bi dokokinka masu adalci.
I sware, and have fulfilled, To keep thy righteous regulations.
107 Na sha wahala sosai; ka kiyaye raina, ya Ubangiji, bisa ga maganarka.
I have been afflicted exceedingly, —O Yahweh, give me life according to thy word.
108 Ka karɓi yabon bakina da nake yi da yardar rai, ya Ubangiji, ka kuwa koya mini dokokinka.
The freewill offerings of my mouth, accept, I pray thee, O Yahweh, And, thy regulations, teach thou me.
109 Ko da yake kullum ina riƙe da raina a hannuwana, ba zan manta da dokarka ba.
My life, is in my hand continually, Yet, thy law, have I not forgotten.
110 Mugaye sun kafa mini tarko, amma ban kauce daga farillanka ba.
The lawless have set a snare for me, Yet, from thy precepts, have I not strayed.
111 Farillanka su ne gādona har abada; su ne farin cikin zuciyata.
As an inheritance have I taken thy testimonies unto times age-abiding, for, the joy of my heart, they are.
112 Zuciyata ta shirya a kan kiyaye ƙa’idodinka har ƙarshe.
I have inclined my heart to perform thy statutes, Age-abidingly, to the end.
113 Na ƙi mutane masu baki biyu, amma ina ƙauna dokarka.
[SAMECH.] Half-hearted ones, do I hate, but, thy law, do I love.
114 Kai ne mafakata da garkuwata; na sa zuciyata a maganarka.
My hiding-place and my buckler, thou art, For thy word, have I waited.
115 Ku rabu da ni, ku masu aikata mugunta, don in kiyaye umarnan Allahna!
Depart from me, ye evil-doers, —that I may observe the commandments of my God.
116 Ka raya ni bisa ga alkawarinka, zan kuwa rayu; kada ka bari a gwale sa zuciyata.
Uphold me according to thy word, that I may live, and do not shame me out of my hope!
117 Ka riƙe ni za a kuma cece ni; kullayaumi zan ɗauka ƙa’idodinka da muhimmanci.
Sustain me, that I may be saved, and may find dear delight in thy statutes continually.
118 Ka ki dukan waɗanda suka kauce daga ƙa’idodinka, gama yaudararsu banza ne.
Thou hast made light of all who stray from thy statutes, for their fraud is, falsehood.
119 Dukan mugayen duniya ka zubar kamar datti; saboda haka nake ƙaunar farillanka.
Dross, have I accounted all the lawless of the earth, therefore do I love thy testimonies.
120 Naman jikina na rawan jiki don tsoronka; na cika da tsoron dokokinka.
My flesh, bristled up from dread of thee, and, of thy regulations, stand I in fear.
121 Na aikata abin da yake mai adalci da kuma daidai; kada ka ni a hannun masu danne ni.
[AYIN.] I have done justice and righteousness, —Do not leave me to mine oppressors.
122 Ka tabbatar da lafiyar bawanka; kada ka bar masu girman kai su danne ni.
Be thou surety for thy servant for good, Let not insolent men oppress me.
123 Idanuna sun gaji, da jiran cetonka, da jiran alkawarinka mai adalci.
Mine eyes, have become dim for thy salvation, and for thy righteous word.
124 Ka yi da bawanka bisa ga ƙaunarka ka kuma koya mini ƙa’idodinka.
Deal with thy servant according to thy lovingkindness, and, thy statutes, teach thou me.
125 Ni bawanka ne, ka ba ni fahimi don in gane farillanka.
Thy servant, I am—give me understanding, so shall I get to know thy testimonies.
126 Lokaci ya yi da za ka yi wani abu, ya Ubangiji; ana karya dokarka.
It is time that Yahweh should work, They have frustrated thy law!
127 Saboda ina ƙaunar umarnanka fiye da zinariya, kai, fiye da zinariya zalla,
For this cause, do I love thy commandments, More than gold, yea than fine gold!
128 saboda kuma ina lura da dukan farillanka da kyau, na ƙi kowace hanyar da ba daidai ba.
For this cause, all thy precepts concerning all things, I deem right, Every way of falsehood, I hate.
129 Farillanka masu banmamaki ne; saboda haka nake yin biyayya da su.
[PE.] Wonderful are thy testimonies, For this cause, hath my soul observed them.
130 Fassarar maganganunka sukan ba da haske; sukan ba da ganewa ga marar ilimi.
The opening of thy words, sheddeth light, Giving understanding to the simple.
131 Ina hakkin da bakina a buɗe, ina marmarin umarnanka.
My mouth, have I opened wide, and panted, because, for thy commandments, have I longed.
132 Ka juye wurina ka kuma yi mini jinƙai, yadda kullum ka yi wa waɗanda suke ƙaunar sunanka.
Turn thyself unto me, and show me favour, —As is befitting, to the lovers of thy Name.
133 Ka bi da sawuna bisa ga maganarka; kada ka bar zunubi yă mallake ni.
My steps, direct thou by thy word, and let no iniquity, have dominion over me.
134 Ka fanshe ni daga mutane masu danniya, don in yi biyayya da farillanka.
Set me free from the oppression of man, so will I keep thy precepts.
135 Ka sa fuskarka ta haskaka a kan bawanka ka kuma koya mini ƙa’idodinka.
Thy face, light thou up on thy servant, and teach me thy statutes.
136 Hawaye suna malalowa daga idanuna kamar rafi, gama ba a biyayya da dokarka.
Streams of water, have run down mine eyes, because men have not kept thy law.
137 Mai adalci ne kai, ya Ubangiji, dokokinka kuma daidai ne.
[ZADHE.] Righteous art thou, O Yahweh, —and, equitable, are thy regulations.
138 Farillan da ka shimfiɗa masu adalci ne; su kuma abin dogara ne ƙwarai.
Thou hast righteously commanded thy testimonies, yea in great faithfulness.
139 Kishina ya cinye ni ɗungum, gama abokan gābana sun yi biris da maganganunka.
My zeal, hath put an end to me, for mine adversaries have forgotten thy words.
140 An gwada alkawuranka sarai, bawanka kuwa yana ƙaunarsu.
Refined is thy word, to the uttermost, and, thy servant loveth it.
141 Ko da yake ni ba kome ba ne an kuwa rena ni, ba na manta da farillanka.
Small, am I, and despised, Thy precepts, have I not forgotten.
142 Adalcinka dawwammame ne dokar kuma gaskiya ce.
Thy righteousness, is righteous to times age-abiding, and, thy law, is truth.
143 Wahala da damuwa suna a kaina, amma umarnanka su ne farin cikina.
Straitness and distress, have befallen me, Thy commandments, are my dear delights.
144 Farillanka daidai ne har abada; ka ba ni ganewa don in rayu.
Righteous are thy testimonies, unto times age-abiding, Give me understanding, that I may live.
145 Na yi kira da dukan zuciyata; ka amsa mini, ya Ubangiji, zan kuwa yi biyayya da ƙa’idodinka.
[KOPH.] I have cried out with all my heart, answer me, O Yahweh; Thy statutes, will I observe.
146 Na yi kira gare ka; ka cece ni zan kuwa kiyaye farillanka.
I have cried out unto thee, oh save me, That I may keep thy testimonies.
147 Na tashi kafin fitowar rana na kuma yi kukan neman taimako; na sa zuciyata a maganarka.
I forestalled the twilight, and cried for help, For thy word, I waited.
148 Ban rufe idanuna ba dukan dare, don in yi tunani a kan alkawuranka.
Mine eyes forestalled the night-watches, To meditate in thy word.
149 Ka ji muryata bisa ga ƙaunarka; ka kiyaye raina, ya Ubangiji, bisa ga dokokinka.
My voice, O hear, according to thy lovingkindness, O Yahweh! according to thy wont, give me life.
150 Waɗanda suke ƙirƙiro mugayen dabaru suna nan kusa, amma suna nesa da dokarka.
They have drawn near, who pursue villainy, From thy law, have they gone far away.
151 Duk da haka kana kusa, ya Ubangiji, kuma dukan umarnanka gaskiya ne.
Near art thou, O Yahweh, and, all thy commandments, are truth.
152 Tun tuni na koyi daga farillanka cewa ka kafa su su kasance har abada.
Long, have I known, from thy testimonies, That, to times age-abiding, thou didst establish them.
153 Ka dubi wahalata ka cece ni, gama ban manta da dokarka ba.
[RESH.] Behold mine affliction, and rescue me, For, thy law, have I not forgotten.
154 Ka kāre manufata ka kuma fanshe ni, ka cece rai na kamar yadda ka alkawarta!
Plead my cause, and redeem me, By thy word, give me life
155 Ceto yana nesa da mugaye, gama ba sa neman ƙa’idodinka.
Far from the lawless, is salvation, For, thy statutes, have they not sought.
156 Tausayinka da girma yake, ya Ubangiji; ka kiyaye raina bisa ga dokokinka.
Thy compassions, are great, O Yahweh, According to thy regulations, give me life.
157 Maƙiya masu yawa ne suke tsananta mini, amma ban rabu da farillanka ba.
Many, are my persecutors and mine adversaries, From thy testimonies, have I not swerved.
158 Na dubi marasa aminci da ƙyama, gama ba sa yin biyayya da maganarka.
I have seen traitors, and felt loathing, Because, thy word, they kept not.
159 Dubi yadda nake ƙaunar farillanka; ka kiyaye raina, ya Ubangiji, bisa ga ƙaunarka.
See thou that, thy precepts, I have loved, O Yahweh, according to thy lovingkindness, give me life.
160 Dukan maganganunka gaskiya ne; dukan dokokinka masu adalci madawwami ne.
The sum of thy word, is truth, and, age-abiding, is every one of thy righteous regulations.
161 Masu mulki suna tsananta mini ba dalili, amma zuciyata na rawan jiki game da maganarka.
[SHIN.] Rulers, have persecuted me, without cause, But, of thy word, hath my heart stood in awe.
162 Ina farin ciki da alkawarinka kamar yadda wani kan sami ganima mai girma.
Joyful am I over thy word, Like the finder of spoil in abundance.
163 Na ƙi ina kuma ƙyamar ƙarya amma ina ƙaunar dokarka.
Falsehood, I hate and abhor, Thy law, do I love.
164 Sau bakwai a rana ina yabonka saboda dokokinka masu adalci.
Seven times in the day, have I praised thee, For thy righteous regulations.
165 Waɗanda suke ƙaunar dokarka suna da babban salama, kuma babu abin da zai sa su yi tuntuɓe.
Blessing in abundance, have the lovers of thy law, and nothing to make them stumble.
166 Ina jiran cetonka, ya Ubangiji, ina kuma bin umarnanka.
I have looked for thy salvation, O Yahweh, and, thy commandments, have I done.
167 Ina biyayya da farillanka, gama ina ƙaunarsu ƙwarai.
My soul hath kept thy testimonies, yea I have loved them greatly.
168 Ina biyayya da farillanka da kuma koyarwarka, gama dukan hanyoyina sanannu ne gare ka.
I have kept thy precepts, and thy testimonies, For, all my ways, are before thee.
169 Bari kukata ta zo gare ka, ya Ubangiji; ka ba ni ganewa bisa ga maganarka.
[TAU] Let my shouting come near before thee, O Yahweh, According to thy word, give me understanding.
170 Bari roƙona yă zo gabanka; ka cece ni bisa ga alkawarinka.
Let my supplication come in before thee, According to thy word, deliver me.
171 Bari leɓunana su cika da yabonka, gama ka koya mini ƙa’idodinka.
My lips, shall pour out, praise, When thou shalt teach me thy statutes.
172 Bari harshena yă rera game da maganarka, gama dukan umarnanka masu adalci ne.
My tongue, shall respond, with thy word, For, all thy commandments, are righteous.
173 Bari hannunka yă kasance a shirye don yă taimake ni, gama na zaɓi farillanka.
Be thy hand ready to help me, For, thy statutes, have I chosen.
174 Ina marmarin cetonka, ya Ubangiji, dokarka kuwa ita ce farin cikina.
I have longed for thy salvation, O Yahweh, and, thy law, is my dear delight.
175 Bari in rayu don in yabe ka, bari kuma dokokinka su raya ni.
Let my soul live, that it may praise thee, So shall thy regulation help me.
176 Na kauce kamar ɓatacciyar tunkiya. Ka nemi bawanka, gama ban manta da umarnanka ba.
I have strayed like a wandering sheep, O seek thy servant, For, thy commandments, have I not forgotten.

< Zabura 119 >