< Zabura 119 >

1 Albarka ta tabbata ga waɗanda rayuwarsu ba ta da abin zargi, waɗanda suke tafiya bisa ga dokar Ubangiji.
ALEPH. Happy are they that are upright in the way, who walk in the law of the LORD.
2 Albarka ta tabbata ga waɗanda suke kiyaye ƙa’idodinsa suke kuma nemansa da dukan zuciyarsu.
Happy are they that keep His testimonies, that seek Him with the whole heart.
3 Ba sa yin wani abin da ba daidai ba; suna tafiya a hanyoyinsa.
Yea, they do no unrighteousness; they walk in His ways.
4 Ka shimfiɗa farillan da dole a yi biyayya da su.
Thou hast ordained Thy precepts, that we should observe them diligently.
5 Kash, da a ce hanyoyina tsayayyu ne a yin biyayya da ƙa’idodinka mana!
Oh that my ways were directed to observe Thy statutes!
6 Da ba zan sha kunya ba sa’ad da na lura da dukan umarnanka.
Then should I not be ashamed, when I have regard unto all Thy commandments.
7 Zan yabe ka da zuciya ta gaskiya yayinda nake koyon dokokinka masu adalci.
I will give thanks unto Thee with uprightness of heart, when I learn Thy righteous ordinances.
8 Zan yi biyayya da ƙa’idodinka; kada ka yashe ni ɗungum.
I will observe Thy statutes; O forsake me not utterly.
9 Yaya matashi zai kiyaye hanyarsa da tsabta? Sai ta yin rayuwa bisa ga maganarka.
BETH. Wherewithal shall a young man keep his way pure? By taking heed thereto according to Thy word.
10 Na neme ka da dukan zuciyata; kada ka bar ni in kauce daga umarnanka.
With my whole heart have I sought Thee; O let me not err from Thy commandments.
11 Na ɓoye maganarka a cikin zuciyata don kada in yi maka zunubi.
Thy word have I laid up in my heart, that I might not sin against Thee.
12 Yabo ya tabbata gare ka, ya Ubangiji; ka koya mini ƙa’idodinka.
Blessed art Thou, O LORD; teach me Thy statutes.
13 Da leɓunana na ba da labarin dukan dokokin da suka fito bakinka.
With my lips have I told all the ordinances of Thy mouth.
14 Na yi farin ciki da bin farillanka yadda mutum yakan yi farin ciki da arziki mai yawa.
I have rejoiced in the way of Thy testimonies, as much as in all riches.
15 Na yi tunani a kan farillanka na kuma lura da hanyoyinka.
I will meditate in Thy precepts, and have respect unto Thy ways.
16 Na yi murna a cikin ƙa’idodinka; ba zan ƙyale maganarka ba.
I will delight myself in Thy statutes; I will not forget Thy word.
17 Ka yi alheri ga bawanka, zan kuwa rayu; zan yi biyayya da maganarka.
GIMEL. Deal bountifully with Thy servant that I may live, and I will observe Thy word.
18 Ka buɗe idanuna don in iya gani abubuwan banmamaki a cikin dokarka.
Open Thou mine eyes, that I may behold wondrous things out of Thy law.
19 Ni baƙo ne a duniya; kada ka ɓoye mini umarnanka.
I am a sojourner in the earth; hide not Thy commandments from me.
20 Zuciyata ta ƙosa saboda marmari don dokokinka koyaushe.
My soul breaketh for the longing that it hath unto Thine ordinances at all times.
21 Ka tsawata wa masu fariya, waɗanda suke la’anta waɗanda kuma suka kauce daga umarnanka.
Thou hast rebuked the proud that are cursed, that do err from Thy commandments.
22 Ka cire mini ba’a da reni, gama ina kiyaye farillanka.
Take away from me reproach and contempt; for I have kept Thy testimonies.
23 Ko da yake masu mulki sun zauna tare suna ɓata mini suna, bawanka zai yi tunani a kan ƙa’idodinka.
Even though princes sit and talk against me, thy servant doth meditate in Thy statutes.
24 Farillanka ne abin farin cikina; su ne mashawartana.
Yea, Thy testimonies are my delight, they are my counsellors.
25 An kwantar da ni ƙasa cikin ƙura; ka kiyaye raina bisa ga maganarka.
DALETH. My soul cleaveth unto the dust; quicken Thou me according to Thy word.
26 Na ba da labari hanyoyina ka kuma amsa mini; ka koya mini ƙa’idodinka.
I told of my ways, and Thou didst answer me; teach me Thy statutes.
27 Bari in gane koyarwar farillanka; sa’an nan zan yi tunani a kan abubuwan banmamakinka.
Make me to understand the way of Thy precepts, that I may talk of Thy wondrous works.
28 Raina ya gaji da baƙin ciki; ka ƙarfafa ni bisa ga maganarka.
My soul melteth away for heaviness; sustain me according unto Thy word.
29 Ka kiyaye ni daga hanyoyin ruɗu; ka yi mini alheri ta wurin dokokinka.
Remove from me the way of falsehood; and grant me Thy law graciously.
30 Na zaɓi hanyar gaskiya; na sa zuciyata a kan dokokinka.
I have chosen the way of faithfulness; Thine ordinances have I set before me.
31 Na riƙe farillanka kankan, ya Ubangiji; kada ka sa in sha kunya.
I cleave unto Thy testimonies; O LORD, put me not to shame.
32 Ina gudu a kan hanyar umarnanka, gama ka’yantar da zuciyata.
I will run the way of Thy commandments, for Thou dost enlarge my heart.
33 Ka koya mini Ya Ubangiji, don in bi ƙa’idodinka; sa’an nan zan kiyaye su har ƙarshe.
HE. Teach me, O LORD, the way of Thy statutes; and I will keep it at every step.
34 Ka ba ni ganewa, zan kuwa kiyaye dokarka in kuma yi biyayya da ita da dukan zuciyata.
Give me understanding, that I keep Thy law and observe it with my whole heart.
35 Ka bi da ni a hanyar umarnanka, gama a can zan sami farin ciki.
Make me to tread in the path of Thy commandments; for therein do I delight.
36 Ka juye zuciyata wajen farillanka ba wajen riba ta sonkai ba.
Incline my heart unto Thy testimonies, and not to covetousness.
37 Ka juye idanuna daga abubuwa marasa amfani; ka kiyaye raina bisa ga maganarka.
Turn away mine eyes from beholding vanity, and quicken me in Thy ways.
38 Ka cika alkawarinka ga bawanka, saboda a ji tsoronka.
Confirm Thy word unto Thy servant, which pertaineth unto the fear of Thee.
39 Ka kawar da shan kunyar da nake tsoro, gama dokokinka nagari ne.
Turn away my reproach which I dread; for Thine ordinances are good.
40 Ina marmarin farillanka ƙwarai! Ka kiyaye raina cikin adalcinka.
Behold, I have longed after Thy precepts; quicken me in Thy righteousness.
41 Bari ƙaunarka marar ƙarewa ta zo gare ni, ya Ubangiji, cetonka bisa ga alkawarinka;
VAV. Let Thy mercies also come unto me, O LORD, even Thy salvation, according to Thy word;
42 sa’an nan zan amsa wa masu cin mutuncina, gama na dogara ga maganarka.
That I may have an answer for him that taunteth me; for I trust in Thy word.
43 Kada ka ƙwace maganarka daga bakina, gama na sa zuciyata a dokokinka.
And take not the word of truth utterly out of my mouth; for I hope in Thine ordinances;
44 Kullayaumi zan yi biyayya da dokokinka, har abada abadin.
So shall I observe Thy law continually for ever and ever;
45 Zan yi ta yawo a sake gama na nemi farillanka.
And I will walk at ease, for I have sought Thy precepts;
46 Zan yi maganar farillanka a gaban sarakuna ba kuwa za a kunyata ni ba,
I will also speak of Thy testimonies before kings, and will not be ashamed.
47 gama ina farin ciki da umarnanka saboda ina ƙaunarsu.
And I will delight myself in Thy commandments, which I have loved.
48 Na ɗaga hannuwana ga umarnanka, waɗanda nake ƙauna, ina kuma tunani a kan ƙa’idodinka.
I will lift up my hands also unto Thy commandments, which I have loved; and I will meditate in Thy statutes.
49 Tuna da maganarka ga bawanka, gama ka ba ni bege.
ZAIN. Remember the word unto Thy servant, because Thou hast made me to hope.
50 Ta’aziyyata cikin wahalata ita ce alkawarinka yana kiyaye raina.
This is my comfort in my affliction, that Thy word hath quickened me.
51 Masu fariya suna yi mini ba’a ba tare da an hana su ba, amma ban rabu da dokar ba.
The proud have had me greatly in derision; yet have I not turned aside from Thy law.
52 Na tuna da dokokinka na tun dā, ya Ubangiji, na kuwa sami ta’aziyya a cikinsu.
I have remembered Thine ordinances which are of old, O LORD, and have comforted myself.
53 Fushi ya kama ni saboda mugaye, waɗanda suka keta dokokinka.
Burning indignation hath taken hold upon me, because of the wicked that forsake Thy law.
54 Ƙa’idodinka su ne kan waƙata a duk inda na sauka.
Thy statutes have been my songs in the house of my pilgrimage.
55 Da dare na tuna da sunanka, ya Ubangiji, zan kuwa kiyaye dokarka.
I have remembered Thy name, O LORD, in the night, and have observed Thy law.
56 Wannan shi ne na saba yi, ina yin biyayya da farillanka.
This I have had, that I have kept Thy precepts.
57 Kai ne rabona, ya Ubangiji; na yi alkawarin in kiyaye maganarka.
HETH. My portion is the LORD, I have said that I would observe Thy words.
58 Na nemi fuskarka da dukan zuciyata; ka yi mini alheri bisa ga alkawarinka.
I have entreated Thy favour with my whole heart; be gracious unto me according to Thy word.
59 Na lura da hanyoyina na kuma mayar da matakaina ga farillanka.
I considered my ways, and turned my feet unto Thy testimonies.
60 Zan gaggauta ba zan ɓata lokaci ba in yi biyayya da umarnanka.
I made haste, and delayed not, to observe Thy commandments.
61 Ko da yake mugaye sun ɗaura ni da igiyoyi, ba zan manta da dokokinka ba.
The bands of the wicked have enclosed me; but I have not forgotten Thy law.
62 Da tsakar dare nakan tashi in gode maka saboda dokokinka masu adalci.
At midnight I will rise to give thanks unto Thee because of Thy righteous ordinances.
63 Ni aboki ne ga duk mai tsoronka, ga duk wanda yake bin farillanka.
I am a companion of all them that fear Thee, and of them that observe Thy precepts.
64 Duniya ta cika da ƙaunarka, ya Ubangiji; ka koya mini ƙa’idodinka.
The earth, O LORD, is full of Thy mercy; teach me Thy statutes.
65 Ka yi wa bawanka alheri bisa ga maganarka, ya Ubangiji.
TETH. Thou hast dealt well with Thy servant, O LORD, according unto Thy word.
66 Ka koya mini sani da kuma hukunci mai kyau, gama na gaskata a umarnanka.
Teach me good discernment and knowledge; for I have believed Thy commandments.
67 Kafin in sha wahala na kauce, amma yanzu ina biyayya da maganarka.
Before I was afflicted, I did err; but now I observe Thy word.
68 Kai nagari ne, kuma abin da kake yi yana da kyau; ka koya mini ƙa’idodinka.
Thou art good, and doest good; teach me Thy statutes.
69 Ko da yake masu fariya sun shafe ni da ƙarairayi, na kiyaye farillanka da dukan zuciyata.
The proud have forged a lie against me; but I with my whole heart will keep Thy precepts.
70 Zukatansu sun yi tauri da kuma marasa tausayi amma ina farin ciki a dokarka.
Their heart is gross like fat; but I delight in Thy law.
71 Ya yi kyau da na sha wahala don in koyi ƙa’idodinka.
It is good for me that I have been afflicted, in order that I might learn Thy statutes.
72 Doka daga bakinka ya fi mini daraja fiye da azurfa da zinariya guda dubu.
The law of Thy mouth is better unto me than thousands of gold and silver.
73 Hannuwanka ne suka yi suka kuma siffanta ni; ka ba ni ganewa don in koyi umarnanka.
JOD. Thy hands have made me and fashioned me; give me understanding, that I may learn Thy commandments.
74 Bari waɗanda suke tsoronka su yi farin ciki sa’ad da suke gan ni, gama na sa zuciyata a maganarka.
They that fear Thee shall see me and be glad, because I have hope in Thy word.
75 Ya Ubangiji na sani, cewa dokokinka masu adalci ne, kuma cikin aminci ka hore ni.
I know, O LORD, that Thy judgments are righteous, and that in faithfulness Thou hast afflicted me.
76 Bari ƙaunarka marar ƙarewa tă yi mini ta’aziyya, bisa ga alkawarinka ga bawanka.
Let, I pray Thee, Thy lovingkindness be ready to comfort me, according to Thy promise unto Thy servant.
77 Bari tausayinka yă zo mini don in rayu, gama dokarka ce farin cikina.
Let Thy tender mercies come unto me, that I may live; for Thy law is my delight.
78 Bari masu girman kai su sha kunya saboda abubuwa marasa kyau da suke yi mini ba dalili; amma zan yi tunani a kan farillanka.
Let the proud be put to shame, for they have distorted my cause with falsehood; but I will meditate in Thy precepts.
79 Bari waɗanda suke tsoronka su juya gare ni, waɗanda suka gane da farillanka.
Let those that fear Thee return unto me, and they that know Thy testimonies.
80 Bari zuciyata ta kasance marar abin zargi wajen ƙa’idodinka, don kada in sha kunya.
Let my heart be undivided in Thy statutes, in order that I may not be put to shame.
81 Raina ya tafke da marmari don cetonka, amma na sa zuciyata a maganarka.
CAPH. My soul pineth for Thy salvation; in Thy word do I hope.
82 Idanuna sun gaji, suna jiran alkawarinka; Na ce, “Yaushe za ka ta’azantar da ni?”
Mine eyes fail for Thy word, saying: 'When wilt Thou comfort me?'
83 Ko da yake ni kamar salkar ruwan inabi ne a cikin hayaƙi, ban manta da ƙa’idodinka ba.
For I am become like a wine-skin in the smoke; yet do I not forget Thy statutes.
84 Har yaushe bawanka zai yi ta jira? Yaushe za ka hukunta masu tsananta mini?
How many are the days of Thy servant? When wilt Thou execute judgment on them that persecute me?
85 Masu girman kai sun haƙa mini rami, sun ƙetare dokarka.
The proud have digged pits for me, which is not according to Thy law.
86 Dukan umarnanka abin dogara ne; ka taimake ni, gama mutane suna tsananta mini ba dalili.
All Thy commandments are faithful; they persecute me for nought; help Thou me.
87 Sun kusa gama da ni a duniya, amma ban bar bin farillanka ba.
They had almost consumed me upon earth; but as for me, I forsook not Thy precepts.
88 Ka kiyaye raina bisa ga ƙaunarka, zan kuwa yi biyayya da farillan bakinka.
Quicken me after Thy lovingkindness, and I will observe the testimony of Thy mouth.
89 Maganarka, ya Ubangiji madawwamiya ce; tana nan daram a cikin sammai.
LAMED. For ever, O LORD, Thy word standeth fast in heaven.
90 Amincinka yana cin gaba cikin dukan zamanai; ka kafa duniya ta kuma dawwama.
Thy faithfulness is unto all generations; Thou hast established the earth, and it standeth.
91 Dokokinka sun dawwama har yă zuwa yau, gama dukan abubuwa suna maka hidima.
They stand this day according to Thine ordinances; for all things are Thy servants.
92 Da ba don dokarka ce farin cikina ba, da na hallaka a cikin azabana.
Unless Thy law had been my delight, I should then have perished in mine affliction.
93 Ba zan taɓa manta da farillanka ba, gama ta wurinsu ne ka kiyaye raina.
I will never forget Thy precepts; for with them Thou hast quickened me.
94 Ka cece ni, gama ni naka ne; na yi ƙoƙarin neman farillanka.
I am Thine, save me; for I have sought Thy precepts.
95 Mugaye suna jira su hallaka ni, amma zan yi ta tunani a kan farillanka.
The wicked have waited for me to destroy me; but I will consider Thy testimonies.
96 Ga duk cikakke na ga kāsawa; amma umarnanka ba su da iyaka.
I have seen an end to every purpose; but Thy commandment is exceeding broad.
97 Kash, ga yadda nake ƙaunar dokarka! Ina tunani a kanta dukan yini.
MEM. O how love I Thy law! It is my meditation all the day.
98 Umarnanka suna sa in zama mai hikima fiye da abokan gābana, gama kullum suna tare da ni.
Thy commandments make me wiser than mine enemies: for they are ever with me.
99 Ina da ganewa sosai fiye da dukan malamaina, gama ina tunani a kan farillanka.
I have more understanding than all my teachers; for Thy testimonies are my (meditation)
100 Ina da ganewa fiye da dattawa, gama ina biyayya da farillanka.
I understand more than mine elders, because I have keep Thy precepts.
101 Na kiyaye ƙafafuna daga kowace muguwar hanya domin in yi biyayya da maganarka.
I have refrained my feet from every evil way, in order that I might observe Thy word.
102 Ban rabu da dokokinka ba, gama kai da kanka ne ka koya mini.
I have not turned aside from Thine ordinances; for Thou hast instructed me.
103 Ɗanɗanon maganarka akwai zaki, sun ma fi zuma zaki a bakina!
How sweet are Thy words unto my palate! yea, sweeter than honey to my mouth!
104 Na sami ganewa daga farillanka; saboda haka ina ƙin kowace hanyar da ba daidai ba.
From Thy precepts I get understanding; therefore I hate every false way.
105 Maganarka fitila ce ga ƙafafuna haske kuma a kan hanyata.
NUN. Thy word is a lamp unto my feet, and a light unto my path.
106 Na yi rantsuwa na kuma tabbatar da shi, cewa zan bi dokokinka masu adalci.
I have sworn, and have confirmed it, to observe Thy righteous ordinances.
107 Na sha wahala sosai; ka kiyaye raina, ya Ubangiji, bisa ga maganarka.
I am afflicted very much; quicken me, O LORD, according unto Thy word.
108 Ka karɓi yabon bakina da nake yi da yardar rai, ya Ubangiji, ka kuwa koya mini dokokinka.
Accept, I beseech Thee, the freewill-offerings of my mouth, O LORD, and teach me Thine ordinances.
109 Ko da yake kullum ina riƙe da raina a hannuwana, ba zan manta da dokarka ba.
My soul is continually in my hand; yet have I not forgotten Thy law.
110 Mugaye sun kafa mini tarko, amma ban kauce daga farillanka ba.
The wicked have laid a snare for me; yet went I not astray from Thy precepts.
111 Farillanka su ne gādona har abada; su ne farin cikin zuciyata.
Thy testimonies have I taken as a heritage for ever; for they are the rejoicing of my heart.
112 Zuciyata ta shirya a kan kiyaye ƙa’idodinka har ƙarshe.
I have inclined my heart to perform Thy statutes, for ever, at every step.
113 Na ƙi mutane masu baki biyu, amma ina ƙauna dokarka.
SAMECH. I hate them that are of a double mind; but Thy law do I love.
114 Kai ne mafakata da garkuwata; na sa zuciyata a maganarka.
Thou art my covert and my shield; in Thy word do I hope.
115 Ku rabu da ni, ku masu aikata mugunta, don in kiyaye umarnan Allahna!
Depart from me, ye evildoers; that I may keep the commandments of my God.
116 Ka raya ni bisa ga alkawarinka, zan kuwa rayu; kada ka bari a gwale sa zuciyata.
Uphold me according unto Thy word, that I may live; and put me not to shame in my hope.
117 Ka riƙe ni za a kuma cece ni; kullayaumi zan ɗauka ƙa’idodinka da muhimmanci.
Support Thou me, and I shall be saved; and I will occupy myself with Thy statutes continually.
118 Ka ki dukan waɗanda suka kauce daga ƙa’idodinka, gama yaudararsu banza ne.
Thou hast made light of all them that err from Thy statutes; for their deceit is vain.
119 Dukan mugayen duniya ka zubar kamar datti; saboda haka nake ƙaunar farillanka.
Thou puttest away all the wicked of the earth like dross; therefore I love Thy testimonies.
120 Naman jikina na rawan jiki don tsoronka; na cika da tsoron dokokinka.
My flesh shuddereth for fear of Thee; and I am afraid of Thy judgments.
121 Na aikata abin da yake mai adalci da kuma daidai; kada ka ni a hannun masu danne ni.
AIN. I have done justice and righteousness; leave me not to mine oppressors.
122 Ka tabbatar da lafiyar bawanka; kada ka bar masu girman kai su danne ni.
Be surety for Thy servant for good; let not the proud oppress me.
123 Idanuna sun gaji, da jiran cetonka, da jiran alkawarinka mai adalci.
Mine eyes fail for Thy salvation, and for Thy righteous word.
124 Ka yi da bawanka bisa ga ƙaunarka ka kuma koya mini ƙa’idodinka.
Deal with Thy servant according unto Thy mercy, and teach me Thy statutes.
125 Ni bawanka ne, ka ba ni fahimi don in gane farillanka.
I am Thy servant, give me understanding, that I may know Thy testimonies.
126 Lokaci ya yi da za ka yi wani abu, ya Ubangiji; ana karya dokarka.
It is time for the LORD to work; they have made void Thy law.
127 Saboda ina ƙaunar umarnanka fiye da zinariya, kai, fiye da zinariya zalla,
Therefore I love Thy commandments above gold, yea, above fine gold.
128 saboda kuma ina lura da dukan farillanka da kyau, na ƙi kowace hanyar da ba daidai ba.
Therefore I esteem all Thy precepts concerning all things to be right; every false way I hate.
129 Farillanka masu banmamaki ne; saboda haka nake yin biyayya da su.
PE. Thy testimonies are wonderful; therefore doth my soul keep them.
130 Fassarar maganganunka sukan ba da haske; sukan ba da ganewa ga marar ilimi.
The opening of Thy words giveth light; it giveth understanding unto the simple.
131 Ina hakkin da bakina a buɗe, ina marmarin umarnanka.
I opened wide my mouth, and panted; for I longed for Thy commandments.
132 Ka juye wurina ka kuma yi mini jinƙai, yadda kullum ka yi wa waɗanda suke ƙaunar sunanka.
Turn Thee towards me, and be gracious unto me, as is Thy wont to do unto those that love Thy name.
133 Ka bi da sawuna bisa ga maganarka; kada ka bar zunubi yă mallake ni.
Order my footsteps by Thy word; and let not any iniquity have dominion over me.
134 Ka fanshe ni daga mutane masu danniya, don in yi biyayya da farillanka.
Redeem me from the oppression of man, and I will observe Thy precepts.
135 Ka sa fuskarka ta haskaka a kan bawanka ka kuma koya mini ƙa’idodinka.
Make Thy face to shine upon Thy servant; and teach me Thy statutes.
136 Hawaye suna malalowa daga idanuna kamar rafi, gama ba a biyayya da dokarka.
Mine eyes run down with rivers of water, because they observe not Thy law.
137 Mai adalci ne kai, ya Ubangiji, dokokinka kuma daidai ne.
TZADE. Righteous art Thou, O LORD, and upright are Thy judgments.
138 Farillan da ka shimfiɗa masu adalci ne; su kuma abin dogara ne ƙwarai.
Thou hast commanded Thy testimonies in righteousness and exceeding faithfulness.
139 Kishina ya cinye ni ɗungum, gama abokan gābana sun yi biris da maganganunka.
My zeal hath undone me, because mine adversaries have forgotten Thy words.
140 An gwada alkawuranka sarai, bawanka kuwa yana ƙaunarsu.
Thy word is tried to the uttermost, and Thy servant loveth it.
141 Ko da yake ni ba kome ba ne an kuwa rena ni, ba na manta da farillanka.
I am small and despised; yet have I not forgotten Thy precepts.
142 Adalcinka dawwammame ne dokar kuma gaskiya ce.
Thy righteousness is an everlasting righteousness, and Thy law is the truth.
143 Wahala da damuwa suna a kaina, amma umarnanka su ne farin cikina.
Trouble and anguish have overtaken me; yet Thy commandments are my delight.
144 Farillanka daidai ne har abada; ka ba ni ganewa don in rayu.
Thy testimonies are righteous for ever; give me understanding, and I shall live.
145 Na yi kira da dukan zuciyata; ka amsa mini, ya Ubangiji, zan kuwa yi biyayya da ƙa’idodinka.
KOPH. I have called with my whole heart; answer me, O LORD; I will keep Thy statutes.
146 Na yi kira gare ka; ka cece ni zan kuwa kiyaye farillanka.
I have called Thee, save me, and I will observe Thy testimonies.
147 Na tashi kafin fitowar rana na kuma yi kukan neman taimako; na sa zuciyata a maganarka.
I rose early at dawn, and cried; I hoped in Thy word.
148 Ban rufe idanuna ba dukan dare, don in yi tunani a kan alkawuranka.
Mine eyes forestalled the night-watches, that I might meditate in Thy word.
149 Ka ji muryata bisa ga ƙaunarka; ka kiyaye raina, ya Ubangiji, bisa ga dokokinka.
Hear my voice according unto Thy lovingkindness; quicken me, O LORD, as Thou art wont.
150 Waɗanda suke ƙirƙiro mugayen dabaru suna nan kusa, amma suna nesa da dokarka.
They draw nigh that follow after wickedness; they are far from Thy law.
151 Duk da haka kana kusa, ya Ubangiji, kuma dukan umarnanka gaskiya ne.
Thou art nigh, O LORD; and all Thy commandments are truth.
152 Tun tuni na koyi daga farillanka cewa ka kafa su su kasance har abada.
Of old have I known from Thy testimonies that Thou hast founded them for ever.
153 Ka dubi wahalata ka cece ni, gama ban manta da dokarka ba.
RESH. O see mine affliction, and rescue me; for I do not forget Thy law.
154 Ka kāre manufata ka kuma fanshe ni, ka cece rai na kamar yadda ka alkawarta!
Plead Thou my cause, and redeem me; quicken me according to Thy word.
155 Ceto yana nesa da mugaye, gama ba sa neman ƙa’idodinka.
Salvation is far from the wicked; for they seek not Thy statutes.
156 Tausayinka da girma yake, ya Ubangiji; ka kiyaye raina bisa ga dokokinka.
Great are Thy compassions, O LORD; quicken me as Thou art wont.
157 Maƙiya masu yawa ne suke tsananta mini, amma ban rabu da farillanka ba.
Many are my persecutors and mine adversaries; yet have I not turned aside from Thy testimonies.
158 Na dubi marasa aminci da ƙyama, gama ba sa yin biyayya da maganarka.
I beheld them that were faithless, and strove with them; because they observed not Thy word.
159 Dubi yadda nake ƙaunar farillanka; ka kiyaye raina, ya Ubangiji, bisa ga ƙaunarka.
O see how I love Thy precepts; quicken me, O LORD, according to Thy lovingkindness.
160 Dukan maganganunka gaskiya ne; dukan dokokinka masu adalci madawwami ne.
The beginning of Thy word is truth; and all Thy righteous ordinance endureth for ever.
161 Masu mulki suna tsananta mini ba dalili, amma zuciyata na rawan jiki game da maganarka.
SCHIN. Princes have persecuted me without a cause; but my heart standeth in awe of Thy words.
162 Ina farin ciki da alkawarinka kamar yadda wani kan sami ganima mai girma.
I rejoice at Thy word, as one that findeth great spoil.
163 Na ƙi ina kuma ƙyamar ƙarya amma ina ƙaunar dokarka.
I hate and abhor falsehood; Thy law do I love.
164 Sau bakwai a rana ina yabonka saboda dokokinka masu adalci.
Seven times a day do I praise Thee, because of Thy righteous ordinances.
165 Waɗanda suke ƙaunar dokarka suna da babban salama, kuma babu abin da zai sa su yi tuntuɓe.
Great peace have they that love Thy law; and there is no stumbling for them.
166 Ina jiran cetonka, ya Ubangiji, ina kuma bin umarnanka.
I have hoped for Thy salvation, O LORD, and have done Thy commandments.
167 Ina biyayya da farillanka, gama ina ƙaunarsu ƙwarai.
My soul hath observed Thy testimonies; and I love them exceedingly.
168 Ina biyayya da farillanka da kuma koyarwarka, gama dukan hanyoyina sanannu ne gare ka.
I have observed Thy precepts and Thy testimonies; for all my ways are before Thee.
169 Bari kukata ta zo gare ka, ya Ubangiji; ka ba ni ganewa bisa ga maganarka.
TAV. Let my cry come near before Thee, O LORD; give me understanding according to Thy word.
170 Bari roƙona yă zo gabanka; ka cece ni bisa ga alkawarinka.
Let my supplication come before Thee; deliver me according to Thy word.
171 Bari leɓunana su cika da yabonka, gama ka koya mini ƙa’idodinka.
Let my lips utter praise: because Thou teachest me Thy statutes.
172 Bari harshena yă rera game da maganarka, gama dukan umarnanka masu adalci ne.
Let my tongue sing of Thy word; for all Thy commandments are righteousness.
173 Bari hannunka yă kasance a shirye don yă taimake ni, gama na zaɓi farillanka.
Let Thy hand be ready to help me; for I have chosen Thy precepts.
174 Ina marmarin cetonka, ya Ubangiji, dokarka kuwa ita ce farin cikina.
I have longed for Thy salvation, O LORD; and Thy law is my delight.
175 Bari in rayu don in yabe ka, bari kuma dokokinka su raya ni.
Let my soul live, and it shall praise Thee; and let Thine ordinances help me.
176 Na kauce kamar ɓatacciyar tunkiya. Ka nemi bawanka, gama ban manta da umarnanka ba.
I have gone astray like a lost sheep; seek Thy servant; for I have not forgotten Thy commandments.

< Zabura 119 >