< Zabura 119 >

1 Albarka ta tabbata ga waɗanda rayuwarsu ba ta da abin zargi, waɗanda suke tafiya bisa ga dokar Ubangiji.
ALEPH. Blessed are the perfect in the way, who walk in the law of Jehovah.
2 Albarka ta tabbata ga waɗanda suke kiyaye ƙa’idodinsa suke kuma nemansa da dukan zuciyarsu.
Blessed are they that observe his testimonies, that seek him with the whole heart;
3 Ba sa yin wani abin da ba daidai ba; suna tafiya a hanyoyinsa.
Who also do no unrighteousness: they walk in his ways.
4 Ka shimfiɗa farillan da dole a yi biyayya da su.
Thou hast enjoined thy precepts, to be kept diligently.
5 Kash, da a ce hanyoyina tsayayyu ne a yin biyayya da ƙa’idodinka mana!
Oh that my ways were directed to keep thy statutes!
6 Da ba zan sha kunya ba sa’ad da na lura da dukan umarnanka.
Then shall I not be ashamed, when I have respect unto all thy commandments.
7 Zan yabe ka da zuciya ta gaskiya yayinda nake koyon dokokinka masu adalci.
I will give thee thanks with uprightness of heart, when I shall have learned thy righteous judgments.
8 Zan yi biyayya da ƙa’idodinka; kada ka yashe ni ɗungum.
I will keep thy statutes: forsake me not utterly.
9 Yaya matashi zai kiyaye hanyarsa da tsabta? Sai ta yin rayuwa bisa ga maganarka.
BETH. Wherewithal shall a young man cleanse his path? by taking heed according to thy word.
10 Na neme ka da dukan zuciyata; kada ka bar ni in kauce daga umarnanka.
With my whole heart have I sought thee: let me not wander from thy commandments.
11 Na ɓoye maganarka a cikin zuciyata don kada in yi maka zunubi.
Thy word have I hid in my heart, that I might not sin against thee.
12 Yabo ya tabbata gare ka, ya Ubangiji; ka koya mini ƙa’idodinka.
Blessed art thou, Jehovah! teach me thy statutes.
13 Da leɓunana na ba da labarin dukan dokokin da suka fito bakinka.
With my lips have I declared all the judgments of thy mouth.
14 Na yi farin ciki da bin farillanka yadda mutum yakan yi farin ciki da arziki mai yawa.
I have rejoiced in the way of thy testimonies, as [much as] in all wealth.
15 Na yi tunani a kan farillanka na kuma lura da hanyoyinka.
I will meditate upon thy precepts, and have respect unto thy paths.
16 Na yi murna a cikin ƙa’idodinka; ba zan ƙyale maganarka ba.
I delight myself in thy statutes; I will not forget thy word.
17 Ka yi alheri ga bawanka, zan kuwa rayu; zan yi biyayya da maganarka.
GIMEL. Deal bountifully with thy servant [and] I shall live; and I will keep thy word.
18 Ka buɗe idanuna don in iya gani abubuwan banmamaki a cikin dokarka.
Open mine eyes, and I shall behold wondrous things out of thy law.
19 Ni baƙo ne a duniya; kada ka ɓoye mini umarnanka.
I am a stranger in the land; hide not thy commandments from me.
20 Zuciyata ta ƙosa saboda marmari don dokokinka koyaushe.
My soul breaketh for longing after thy judgments at all times.
21 Ka tsawata wa masu fariya, waɗanda suke la’anta waɗanda kuma suka kauce daga umarnanka.
Thou hast rebuked the proud [that are] cursed, who wander from thy commandments.
22 Ka cire mini ba’a da reni, gama ina kiyaye farillanka.
Roll off from me reproach and contempt; for I observe thy testimonies.
23 Ko da yake masu mulki sun zauna tare suna ɓata mini suna, bawanka zai yi tunani a kan ƙa’idodinka.
Princes also did sit [and] talk together against me: thy servant doth meditate in thy statutes.
24 Farillanka ne abin farin cikina; su ne mashawartana.
Thy testimonies also are my delight [and] my counsellors.
25 An kwantar da ni ƙasa cikin ƙura; ka kiyaye raina bisa ga maganarka.
DALETH. My soul cleaveth unto the dust: quicken me according to thy word.
26 Na ba da labari hanyoyina ka kuma amsa mini; ka koya mini ƙa’idodinka.
I have declared my ways, and thou hast answered me: teach me thy statutes.
27 Bari in gane koyarwar farillanka; sa’an nan zan yi tunani a kan abubuwan banmamakinka.
Make me to understand the way of thy precepts, and I will meditate upon thy wondrous works.
28 Raina ya gaji da baƙin ciki; ka ƙarfafa ni bisa ga maganarka.
My soul melteth for sadness: strengthen me according to thy word.
29 Ka kiyaye ni daga hanyoyin ruɗu; ka yi mini alheri ta wurin dokokinka.
Remove from me the way of falsehood, and graciously grant me thy law.
30 Na zaɓi hanyar gaskiya; na sa zuciyata a kan dokokinka.
I have chosen the way of faithfulness; thy judgments have I set [before me].
31 Na riƙe farillanka kankan, ya Ubangiji; kada ka sa in sha kunya.
I cleave unto thy testimonies; Jehovah, let me not be ashamed.
32 Ina gudu a kan hanyar umarnanka, gama ka’yantar da zuciyata.
I will run the way of thy commandments when thou shalt enlarge my heart.
33 Ka koya mini Ya Ubangiji, don in bi ƙa’idodinka; sa’an nan zan kiyaye su har ƙarshe.
HE. Teach me, O Jehovah, the way of thy statutes, and I will observe it [unto] the end.
34 Ka ba ni ganewa, zan kuwa kiyaye dokarka in kuma yi biyayya da ita da dukan zuciyata.
Give me understanding, and I will observe thy law; and I will keep it with [my] whole heart.
35 Ka bi da ni a hanyar umarnanka, gama a can zan sami farin ciki.
Make me to walk in the path of thy commandments; for therein do I delight.
36 Ka juye zuciyata wajen farillanka ba wajen riba ta sonkai ba.
Incline my heart unto thy testimonies, and not to gain.
37 Ka juye idanuna daga abubuwa marasa amfani; ka kiyaye raina bisa ga maganarka.
Turn away mine eyes from beholding vanity; quicken me in thy way.
38 Ka cika alkawarinka ga bawanka, saboda a ji tsoronka.
Establish thy word unto thy servant, who is [devoted] to thy fear.
39 Ka kawar da shan kunyar da nake tsoro, gama dokokinka nagari ne.
Turn away my reproach which I fear; for thy judgments are good.
40 Ina marmarin farillanka ƙwarai! Ka kiyaye raina cikin adalcinka.
Behold, I have longed after thy precepts: quicken me in thy righteousness.
41 Bari ƙaunarka marar ƙarewa ta zo gare ni, ya Ubangiji, cetonka bisa ga alkawarinka;
VAU. And let thy loving-kindness come unto me, O Jehovah, — thy salvation according to thy word.
42 sa’an nan zan amsa wa masu cin mutuncina, gama na dogara ga maganarka.
So shall I have wherewith to answer him that reproacheth me; for I confide in thy word.
43 Kada ka ƙwace maganarka daga bakina, gama na sa zuciyata a dokokinka.
And take not the word of truth utterly out of my mouth; because I have hoped in thy judgments.
44 Kullayaumi zan yi biyayya da dokokinka, har abada abadin.
Then will I keep thy law continually, for ever and ever;
45 Zan yi ta yawo a sake gama na nemi farillanka.
And I will walk at liberty, for I have sought thy precepts;
46 Zan yi maganar farillanka a gaban sarakuna ba kuwa za a kunyata ni ba,
And I will speak of thy testimonies before kings, and will not be ashamed;
47 gama ina farin ciki da umarnanka saboda ina ƙaunarsu.
And I will delight myself in thy commandments, which I have loved;
48 Na ɗaga hannuwana ga umarnanka, waɗanda nake ƙauna, ina kuma tunani a kan ƙa’idodinka.
And I will lift up my hands unto thy commandments, which I have loved, and I will meditate in thy statutes.
49 Tuna da maganarka ga bawanka, gama ka ba ni bege.
ZAIN. Remember the word for thy servant, upon which thou hast caused me to hope.
50 Ta’aziyyata cikin wahalata ita ce alkawarinka yana kiyaye raina.
This is my comfort in mine affliction; for thy word hath quickened me.
51 Masu fariya suna yi mini ba’a ba tare da an hana su ba, amma ban rabu da dokar ba.
The proud have derided me beyond measure: I have not declined from thy law.
52 Na tuna da dokokinka na tun dā, ya Ubangiji, na kuwa sami ta’aziyya a cikinsu.
I remembered thy judgments of old, O Jehovah, and have comforted myself.
53 Fushi ya kama ni saboda mugaye, waɗanda suka keta dokokinka.
Burning indignation hath taken hold upon me because of the wicked who forsake thy law.
54 Ƙa’idodinka su ne kan waƙata a duk inda na sauka.
Thy statutes have been my songs in the house of my pilgrimage.
55 Da dare na tuna da sunanka, ya Ubangiji, zan kuwa kiyaye dokarka.
I have remembered thy name, O Jehovah, in the night, and have kept thy law.
56 Wannan shi ne na saba yi, ina yin biyayya da farillanka.
This I have had, because I have observed thy precepts.
57 Kai ne rabona, ya Ubangiji; na yi alkawarin in kiyaye maganarka.
CHETH. My portion, O Jehovah, I have said, is to keep thy words.
58 Na nemi fuskarka da dukan zuciyata; ka yi mini alheri bisa ga alkawarinka.
I have sought thy favour with [my] whole heart: be gracious unto me according to thy word.
59 Na lura da hanyoyina na kuma mayar da matakaina ga farillanka.
I have thought on my ways, and turned my feet unto thy testimonies.
60 Zan gaggauta ba zan ɓata lokaci ba in yi biyayya da umarnanka.
I have made haste, and not delayed, to keep thy commandments.
61 Ko da yake mugaye sun ɗaura ni da igiyoyi, ba zan manta da dokokinka ba.
The bands of the wicked have wrapped me round: I have not forgotten thy law.
62 Da tsakar dare nakan tashi in gode maka saboda dokokinka masu adalci.
At midnight I rise up to give thanks unto thee, because of thy righteous judgments.
63 Ni aboki ne ga duk mai tsoronka, ga duk wanda yake bin farillanka.
I am the companion of all that fear thee, and of them that keep thy precepts.
64 Duniya ta cika da ƙaunarka, ya Ubangiji; ka koya mini ƙa’idodinka.
The earth, O Jehovah, is full of thy loving-kindness: teach me thy statutes.
65 Ka yi wa bawanka alheri bisa ga maganarka, ya Ubangiji.
TETH. Thou hast dealt well with thy servant, O Jehovah, according to thy word.
66 Ka koya mini sani da kuma hukunci mai kyau, gama na gaskata a umarnanka.
Teach me good discernment and knowledge; for I have believed in thy commandments.
67 Kafin in sha wahala na kauce, amma yanzu ina biyayya da maganarka.
Before I was afflicted I went astray, but now I keep thy word.
68 Kai nagari ne, kuma abin da kake yi yana da kyau; ka koya mini ƙa’idodinka.
Thou art good, and doest good; teach me thy statutes.
69 Ko da yake masu fariya sun shafe ni da ƙarairayi, na kiyaye farillanka da dukan zuciyata.
The proud have forged falsehood against me: I will observe thy precepts with [my] whole heart.
70 Zukatansu sun yi tauri da kuma marasa tausayi amma ina farin ciki a dokarka.
Their heart is as fat as grease: as for me, I delight in thy law.
71 Ya yi kyau da na sha wahala don in koyi ƙa’idodinka.
It is good for me that I have been afflicted, that I might learn thy statutes.
72 Doka daga bakinka ya fi mini daraja fiye da azurfa da zinariya guda dubu.
The law of thy mouth is better unto me than thousands of gold and silver.
73 Hannuwanka ne suka yi suka kuma siffanta ni; ka ba ni ganewa don in koyi umarnanka.
YOD. Thy hands have made me and fashioned me: give me understanding, and I will learn thy commandments.
74 Bari waɗanda suke tsoronka su yi farin ciki sa’ad da suke gan ni, gama na sa zuciyata a maganarka.
They that fear thee will see me, and rejoice; because I have hoped in thy word.
75 Ya Ubangiji na sani, cewa dokokinka masu adalci ne, kuma cikin aminci ka hore ni.
I know, Jehovah, that thy Judgments are righteousness, and that in faithfulness thou hast afflicted me.
76 Bari ƙaunarka marar ƙarewa tă yi mini ta’aziyya, bisa ga alkawarinka ga bawanka.
Oh let thy loving-kindness be for my comfort, according to thy word unto thy servant.
77 Bari tausayinka yă zo mini don in rayu, gama dokarka ce farin cikina.
Let thy tender mercies come unto me, that I may live; for thy law is my delight.
78 Bari masu girman kai su sha kunya saboda abubuwa marasa kyau da suke yi mini ba dalili; amma zan yi tunani a kan farillanka.
Let the proud be ashamed; for they have acted perversely towards me with falsehood: as for me, I meditate in thy precepts.
79 Bari waɗanda suke tsoronka su juya gare ni, waɗanda suka gane da farillanka.
Let those that fear thee turn unto me, and those that know thy testimonies.
80 Bari zuciyata ta kasance marar abin zargi wajen ƙa’idodinka, don kada in sha kunya.
Let my heart be perfect in thy statutes, that I be not ashamed.
81 Raina ya tafke da marmari don cetonka, amma na sa zuciyata a maganarka.
CAPH. My soul fainteth for thy salvation; I hope in thy word.
82 Idanuna sun gaji, suna jiran alkawarinka; Na ce, “Yaushe za ka ta’azantar da ni?”
Mine eyes fail for thy word, saying, When wilt thou comfort me?
83 Ko da yake ni kamar salkar ruwan inabi ne a cikin hayaƙi, ban manta da ƙa’idodinka ba.
For I am become like a bottle in the smoke; I do not forget thy statutes.
84 Har yaushe bawanka zai yi ta jira? Yaushe za ka hukunta masu tsananta mini?
How many shall be the days of thy servant? when wilt thou execute judgment on them that persecute me?
85 Masu girman kai sun haƙa mini rami, sun ƙetare dokarka.
The proud have digged pits for me, which is not according to thy law.
86 Dukan umarnanka abin dogara ne; ka taimake ni, gama mutane suna tsananta mini ba dalili.
All thy commandments are faithfulness. They persecute me wrongfully: help thou me.
87 Sun kusa gama da ni a duniya, amma ban bar bin farillanka ba.
They had almost consumed me upon the earth; but as for me, I forsook not thy precepts.
88 Ka kiyaye raina bisa ga ƙaunarka, zan kuwa yi biyayya da farillan bakinka.
Quicken me according to thy loving-kindness, and I will keep the testimony of thy mouth.
89 Maganarka, ya Ubangiji madawwamiya ce; tana nan daram a cikin sammai.
LAMED. For ever, O Jehovah, thy word is settled in the heavens.
90 Amincinka yana cin gaba cikin dukan zamanai; ka kafa duniya ta kuma dawwama.
Thy faithfulness is from generation to generation: thou hast established the earth, and it standeth.
91 Dokokinka sun dawwama har yă zuwa yau, gama dukan abubuwa suna maka hidima.
By thine ordinances they stand this day; for all things are thy servants.
92 Da ba don dokarka ce farin cikina ba, da na hallaka a cikin azabana.
Unless thy law had been my delight, I should then have perished in mine affliction.
93 Ba zan taɓa manta da farillanka ba, gama ta wurinsu ne ka kiyaye raina.
I will never forget thy precepts; for by them thou hast quickened me.
94 Ka cece ni, gama ni naka ne; na yi ƙoƙarin neman farillanka.
I am thine, save me; for I have sought thy precepts.
95 Mugaye suna jira su hallaka ni, amma zan yi ta tunani a kan farillanka.
The wicked have awaited me to destroy me; [but] I attend unto thy testimonies.
96 Ga duk cikakke na ga kāsawa; amma umarnanka ba su da iyaka.
I have seen an end of all perfection: thy commandment is exceeding broad.
97 Kash, ga yadda nake ƙaunar dokarka! Ina tunani a kanta dukan yini.
MEM. Oh how I love thy law! it is my meditation all the day.
98 Umarnanka suna sa in zama mai hikima fiye da abokan gābana, gama kullum suna tare da ni.
Thy commandments make me wiser than mine enemies; for they are ever with me.
99 Ina da ganewa sosai fiye da dukan malamaina, gama ina tunani a kan farillanka.
I have more understanding than all my teachers; for thy testimonies are my (meditation)
100 Ina da ganewa fiye da dattawa, gama ina biyayya da farillanka.
I understand more than the aged, because I have observed thy precepts.
101 Na kiyaye ƙafafuna daga kowace muguwar hanya domin in yi biyayya da maganarka.
I have refrained my feet from every evil path, that I might keep thy word.
102 Ban rabu da dokokinka ba, gama kai da kanka ne ka koya mini.
I have not departed from thy judgments; for it is thou that hast taught me.
103 Ɗanɗanon maganarka akwai zaki, sun ma fi zuma zaki a bakina!
How sweet are thy words unto my taste! more than honey to my mouth!
104 Na sami ganewa daga farillanka; saboda haka ina ƙin kowace hanyar da ba daidai ba.
From thy precepts I get understanding; therefore I hate every false path.
105 Maganarka fitila ce ga ƙafafuna haske kuma a kan hanyata.
NUN. Thy word is a lamp unto my feet, and a light unto my path.
106 Na yi rantsuwa na kuma tabbatar da shi, cewa zan bi dokokinka masu adalci.
I have sworn, and I will perform it, that I will keep thy righteous judgments.
107 Na sha wahala sosai; ka kiyaye raina, ya Ubangiji, bisa ga maganarka.
I am afflicted very much; O Jehovah, quicken me according to thy word.
108 Ka karɓi yabon bakina da nake yi da yardar rai, ya Ubangiji, ka kuwa koya mini dokokinka.
Accept, I beseech thee, Jehovah, the voluntary-offerings of my mouth, and teach me thy judgments.
109 Ko da yake kullum ina riƙe da raina a hannuwana, ba zan manta da dokarka ba.
My life is continually in my hand; but I do not forget thy law.
110 Mugaye sun kafa mini tarko, amma ban kauce daga farillanka ba.
The wicked have laid a snare for me; but I have not wandered from thy precepts.
111 Farillanka su ne gādona har abada; su ne farin cikin zuciyata.
Thy testimonies have I taken as a heritage for ever; for they are the rejoicing of my heart.
112 Zuciyata ta shirya a kan kiyaye ƙa’idodinka har ƙarshe.
I have inclined my heart to perform thy statutes for ever, unto the end.
113 Na ƙi mutane masu baki biyu, amma ina ƙauna dokarka.
SAMECH. The double-minded have I hated; but thy law do I love.
114 Kai ne mafakata da garkuwata; na sa zuciyata a maganarka.
Thou art my hiding-place and my shield: I hope in thy word.
115 Ku rabu da ni, ku masu aikata mugunta, don in kiyaye umarnan Allahna!
Depart from me, ye evil-doers; and I will observe the commandments of my God.
116 Ka raya ni bisa ga alkawarinka, zan kuwa rayu; kada ka bari a gwale sa zuciyata.
Uphold me according to thy word, that I may live; and let me not be ashamed of my hope.
117 Ka riƙe ni za a kuma cece ni; kullayaumi zan ɗauka ƙa’idodinka da muhimmanci.
Hold thou me up, and I shall be safe; and I will have respect unto thy statutes continually.
118 Ka ki dukan waɗanda suka kauce daga ƙa’idodinka, gama yaudararsu banza ne.
Thou hast set at nought all them that wander from thy statutes; for their deceit is falsehood.
119 Dukan mugayen duniya ka zubar kamar datti; saboda haka nake ƙaunar farillanka.
Thou puttest away all the wicked of the earth [like] dross; therefore I love thy testimonies.
120 Naman jikina na rawan jiki don tsoronka; na cika da tsoron dokokinka.
My flesh shuddereth for fear of thee; and I am afraid of thy judgments.
121 Na aikata abin da yake mai adalci da kuma daidai; kada ka ni a hannun masu danne ni.
AIN. I have done judgment and justice: leave me not to mine oppressors.
122 Ka tabbatar da lafiyar bawanka; kada ka bar masu girman kai su danne ni.
Be surety for thy servant for good; let not the proud oppress me.
123 Idanuna sun gaji, da jiran cetonka, da jiran alkawarinka mai adalci.
Mine eyes fail for thy salvation, and for the word of thy righteousness.
124 Ka yi da bawanka bisa ga ƙaunarka ka kuma koya mini ƙa’idodinka.
Deal with thy servant according to thy loving-kindness, and teach me thy statutes.
125 Ni bawanka ne, ka ba ni fahimi don in gane farillanka.
I am thy servant; give me understanding that I may know thy testimonies.
126 Lokaci ya yi da za ka yi wani abu, ya Ubangiji; ana karya dokarka.
It is time for Jehovah to work: they have made void thy law.
127 Saboda ina ƙaunar umarnanka fiye da zinariya, kai, fiye da zinariya zalla,
Therefore I love thy commandments above gold, yea, above fine gold.
128 saboda kuma ina lura da dukan farillanka da kyau, na ƙi kowace hanyar da ba daidai ba.
Therefore I regard all [thy] precepts concerning all things to be right: I hate every false path.
129 Farillanka masu banmamaki ne; saboda haka nake yin biyayya da su.
PE. Thy testimonies are wonderful; therefore doth my soul observe them.
130 Fassarar maganganunka sukan ba da haske; sukan ba da ganewa ga marar ilimi.
The entrance of thy words giveth light, giving understanding unto the simple.
131 Ina hakkin da bakina a buɗe, ina marmarin umarnanka.
I opened my mouth wide and panted; for I longed for thy commandments.
132 Ka juye wurina ka kuma yi mini jinƙai, yadda kullum ka yi wa waɗanda suke ƙaunar sunanka.
Turn unto me, and be gracious unto me, as thou art wont to do unto those that love thy name.
133 Ka bi da sawuna bisa ga maganarka; kada ka bar zunubi yă mallake ni.
Establish my steps in thy word; and let not any iniquity have dominion over me.
134 Ka fanshe ni daga mutane masu danniya, don in yi biyayya da farillanka.
Deliver me from the oppression of man; and I will keep thy precepts.
135 Ka sa fuskarka ta haskaka a kan bawanka ka kuma koya mini ƙa’idodinka.
Make thy face to shine upon thy servant, and teach me thy statutes.
136 Hawaye suna malalowa daga idanuna kamar rafi, gama ba a biyayya da dokarka.
Mine eyes run down with streams of water, because they keep not thy law.
137 Mai adalci ne kai, ya Ubangiji, dokokinka kuma daidai ne.
TZADE. Righteous art thou, Jehovah, and upright are thy judgments.
138 Farillan da ka shimfiɗa masu adalci ne; su kuma abin dogara ne ƙwarai.
Thou hast commanded thy testimonies in righteousness and exceeding faithfulness.
139 Kishina ya cinye ni ɗungum, gama abokan gābana sun yi biris da maganganunka.
My zeal destroyeth me, because mine oppressors have forgotten thy words.
140 An gwada alkawuranka sarai, bawanka kuwa yana ƙaunarsu.
Thy word is exceeding pure, and thy servant loveth it.
141 Ko da yake ni ba kome ba ne an kuwa rena ni, ba na manta da farillanka.
I am little and despised: thy precepts have I not forgotten.
142 Adalcinka dawwammame ne dokar kuma gaskiya ce.
Thy righteousness is an everlasting righteousness, and thy law is truth.
143 Wahala da damuwa suna a kaina, amma umarnanka su ne farin cikina.
Trouble and anguish have taken hold upon me: thy commandments are my delights.
144 Farillanka daidai ne har abada; ka ba ni ganewa don in rayu.
The righteousness of thy testimonies is for ever: give me understanding, and I shall live.
145 Na yi kira da dukan zuciyata; ka amsa mini, ya Ubangiji, zan kuwa yi biyayya da ƙa’idodinka.
KOPH. I have called with [my] whole heart; answer me, O Jehovah: I will observe thy statutes.
146 Na yi kira gare ka; ka cece ni zan kuwa kiyaye farillanka.
I call upon thee; save me, and I will keep thy testimonies.
147 Na tashi kafin fitowar rana na kuma yi kukan neman taimako; na sa zuciyata a maganarka.
I anticipate the morning-dawn and I cry: I hope in thy word.
148 Ban rufe idanuna ba dukan dare, don in yi tunani a kan alkawuranka.
Mine eyes anticipate the night-watches, that I may meditate in thy word.
149 Ka ji muryata bisa ga ƙaunarka; ka kiyaye raina, ya Ubangiji, bisa ga dokokinka.
Hear my voice according to thy loving-kindness: O Jehovah, quicken me according to thy judgment.
150 Waɗanda suke ƙirƙiro mugayen dabaru suna nan kusa, amma suna nesa da dokarka.
They have drawn nigh that follow after mischief: they are far from thy law.
151 Duk da haka kana kusa, ya Ubangiji, kuma dukan umarnanka gaskiya ne.
Thou, Jehovah, art near, and all thy commandments are truth.
152 Tun tuni na koyi daga farillanka cewa ka kafa su su kasance har abada.
From thy testimonies, I have known of old that thou hast founded them for ever.
153 Ka dubi wahalata ka cece ni, gama ban manta da dokarka ba.
RESH. See mine affliction, and deliver me; for I have not forgotten thy law.
154 Ka kāre manufata ka kuma fanshe ni, ka cece rai na kamar yadda ka alkawarta!
Plead my cause, and redeem me: quicken me according to thy word.
155 Ceto yana nesa da mugaye, gama ba sa neman ƙa’idodinka.
Salvation is far from the wicked; for they seek not thy statutes.
156 Tausayinka da girma yake, ya Ubangiji; ka kiyaye raina bisa ga dokokinka.
Many are thy tender mercies, O Jehovah; quicken me according to thy judgments.
157 Maƙiya masu yawa ne suke tsananta mini, amma ban rabu da farillanka ba.
Many are my persecutors and mine oppressors; I have not declined from thy testimonies.
158 Na dubi marasa aminci da ƙyama, gama ba sa yin biyayya da maganarka.
I beheld them that deal treacherously, and was grieved; because they kept not thy word.
159 Dubi yadda nake ƙaunar farillanka; ka kiyaye raina, ya Ubangiji, bisa ga ƙaunarka.
See how I have loved thy precepts: quicken me, O Jehovah, according to thy loving-kindness.
160 Dukan maganganunka gaskiya ne; dukan dokokinka masu adalci madawwami ne.
The sum of thy word is truth, and every righteous judgment of thine is for ever.
161 Masu mulki suna tsananta mini ba dalili, amma zuciyata na rawan jiki game da maganarka.
SHIN. Princes have persecuted me without a cause; but my heart standeth in awe of thy word.
162 Ina farin ciki da alkawarinka kamar yadda wani kan sami ganima mai girma.
I have joy in thy word, as one that findeth great spoil.
163 Na ƙi ina kuma ƙyamar ƙarya amma ina ƙaunar dokarka.
I hate and abhor falsehood; thy law do I love.
164 Sau bakwai a rana ina yabonka saboda dokokinka masu adalci.
Seven times a day do I praise thee because of thy righteous judgments.
165 Waɗanda suke ƙaunar dokarka suna da babban salama, kuma babu abin da zai sa su yi tuntuɓe.
Great peace have they that love thy law, and nothing doth stumble them.
166 Ina jiran cetonka, ya Ubangiji, ina kuma bin umarnanka.
I have hoped for thy salvation, O Jehovah, and have done thy commandments.
167 Ina biyayya da farillanka, gama ina ƙaunarsu ƙwarai.
My soul hath kept thy testimonies, and I love them exceedingly.
168 Ina biyayya da farillanka da kuma koyarwarka, gama dukan hanyoyina sanannu ne gare ka.
I have kept thy precepts and thy testimonies; for all my ways are before thee.
169 Bari kukata ta zo gare ka, ya Ubangiji; ka ba ni ganewa bisa ga maganarka.
TAU. Let my cry come near before thee, Jehovah: give me understanding according to thy word.
170 Bari roƙona yă zo gabanka; ka cece ni bisa ga alkawarinka.
Let my supplication come before thee: deliver me according to thy word.
171 Bari leɓunana su cika da yabonka, gama ka koya mini ƙa’idodinka.
My lips shall pour forth praise when thou hast taught me thy statutes.
172 Bari harshena yă rera game da maganarka, gama dukan umarnanka masu adalci ne.
My tongue shall speak aloud of thy word; for all thy commandments are righteousness.
173 Bari hannunka yă kasance a shirye don yă taimake ni, gama na zaɓi farillanka.
Let thy hand be for my help; for I have chosen thy precepts.
174 Ina marmarin cetonka, ya Ubangiji, dokarka kuwa ita ce farin cikina.
I have longed for thy salvation, O Jehovah, and thy law is my delight.
175 Bari in rayu don in yabe ka, bari kuma dokokinka su raya ni.
Let my soul live, and it shall praise thee; and let thy judgments help me.
176 Na kauce kamar ɓatacciyar tunkiya. Ka nemi bawanka, gama ban manta da umarnanka ba.
I have gone astray like a lost sheep: seek thy servant; for I have not forgotten thy commandments.

< Zabura 119 >