< Zabura 119 >

1 Albarka ta tabbata ga waɗanda rayuwarsu ba ta da abin zargi, waɗanda suke tafiya bisa ga dokar Ubangiji.
Salige ere de fuldkomne i Vandel, de, som vandre i Herrens Lov.
2 Albarka ta tabbata ga waɗanda suke kiyaye ƙa’idodinsa suke kuma nemansa da dukan zuciyarsu.
Salige ere de, som bevare hans Vidnesbyrd, de, som søge ham af ganske Hjerte;
3 Ba sa yin wani abin da ba daidai ba; suna tafiya a hanyoyinsa.
og de, som ikke øve Uretfærdighed, men vandre paa hans Veje.
4 Ka shimfiɗa farillan da dole a yi biyayya da su.
Du har givet dine Bud, for at de nøje skulle holdes.
5 Kash, da a ce hanyoyina tsayayyu ne a yin biyayya da ƙa’idodinka mana!
Gid mine Veje maatte stadfæstes, at jeg kan holde dine Skikke;
6 Da ba zan sha kunya ba sa’ad da na lura da dukan umarnanka.
da skal jeg ikke beskæmmes, naar jeg ser hen til alle dine Bud.
7 Zan yabe ka da zuciya ta gaskiya yayinda nake koyon dokokinka masu adalci.
Jeg vil prise dig af et oprigtigt Hjerte, naar jeg lærer din Retfærdigheds Domme at kende.
8 Zan yi biyayya da ƙa’idodinka; kada ka yashe ni ɗungum.
Jeg vil holde dine Skikke, forlad mig ikke aldeles.
9 Yaya matashi zai kiyaye hanyarsa da tsabta? Sai ta yin rayuwa bisa ga maganarka.
Hvormed skal en ung holde sin Sti ren? Derved at han holder sig efter dit Ord.
10 Na neme ka da dukan zuciyata; kada ka bar ni in kauce daga umarnanka.
Jeg søgte dig af mit ganske Hjerte, lad mig ikke fare vild fra dine Bud!
11 Na ɓoye maganarka a cikin zuciyata don kada in yi maka zunubi.
Jeg gemte dit Ord i mit Hjerte, paa det jeg ikke skulde synde imod dig.
12 Yabo ya tabbata gare ka, ya Ubangiji; ka koya mini ƙa’idodinka.
Lovet være du, Herre! lær mig dine Skikke.
13 Da leɓunana na ba da labarin dukan dokokin da suka fito bakinka.
Jeg forkyndte med mine Læber alle din Munds retfærdige Domme.
14 Na yi farin ciki da bin farillanka yadda mutum yakan yi farin ciki da arziki mai yawa.
Jeg glædede mig ved dine Vidnesbyrds Vej som over alle Skatte.
15 Na yi tunani a kan farillanka na kuma lura da hanyoyinka.
Jeg vil grunde paa dine Befalinger og se til dine Stier.
16 Na yi murna a cikin ƙa’idodinka; ba zan ƙyale maganarka ba.
Jeg finder min Lyst i dine Skikke, jeg vir ikke glemme dit Ord.
17 Ka yi alheri ga bawanka, zan kuwa rayu; zan yi biyayya da maganarka.
Gør vel imod din Tjener, at jeg maa leve, og jeg vil holde dit Ord.
18 Ka buɗe idanuna don in iya gani abubuwan banmamaki a cikin dokarka.
Aabn mine Øjne, at jeg maa se de underfulde Ting i din Lov.
19 Ni baƙo ne a duniya; kada ka ɓoye mini umarnanka.
Jeg er fremmed paa Jorden, skjul ikke dine Bud for mig!
20 Zuciyata ta ƙosa saboda marmari don dokokinka koyaushe.
Min Sjæl er knust, saa at jeg længes efter dine Domme alle Tider.
21 Ka tsawata wa masu fariya, waɗanda suke la’anta waɗanda kuma suka kauce daga umarnanka.
Du skældte paa de hovmodige, de bleve forbandede, de, som fore vild fra dine Bud.
22 Ka cire mini ba’a da reni, gama ina kiyaye farillanka.
Vælt Forhaanelse og Foragt fra mig; thi jeg har bevaret dine Vidnesbyrd.
23 Ko da yake masu mulki sun zauna tare suna ɓata mini suna, bawanka zai yi tunani a kan ƙa’idodinka.
Endog Fyrster have sat sig ned og holdt Raad imod mig; men din Tjener grunder paa dine Skikke.
24 Farillanka ne abin farin cikina; su ne mashawartana.
Jeg finder min Lyst i dine Vidnesbyrd, de ere mit Raads Mænd.
25 An kwantar da ni ƙasa cikin ƙura; ka kiyaye raina bisa ga maganarka.
Min Sjæl hænger ved Støvet; hold mig i Live efter dit Ord!
26 Na ba da labari hanyoyina ka kuma amsa mini; ka koya mini ƙa’idodinka.
Jeg opregnede mine Veje, og du bønhørte mig; lær mig dine Skikke!
27 Bari in gane koyarwar farillanka; sa’an nan zan yi tunani a kan abubuwan banmamakinka.
Lad mig forstaa dine Befalingers Vej, og jeg vil grunde paa dine underfulde Gerninger.
28 Raina ya gaji da baƙin ciki; ka ƙarfafa ni bisa ga maganarka.
Min Sjæl svinder hen af Bedrøvelse; oprejs mig efter dit Ord!
29 Ka kiyaye ni daga hanyoyin ruɗu; ka yi mini alheri ta wurin dokokinka.
Vend Løgnens Vej fra mig, og skænk mig Naade i din Lov!
30 Na zaɓi hanyar gaskiya; na sa zuciyata a kan dokokinka.
Jeg udvalgte Trofastheds Vej; jeg satte dine Domme for mig.
31 Na riƙe farillanka kankan, ya Ubangiji; kada ka sa in sha kunya.
Jeg hang ved dine Vidnesbyrd; Herre! lad mig ikke beskæmmes.
32 Ina gudu a kan hanyar umarnanka, gama ka’yantar da zuciyata.
Jeg vil løbe dine Buds Vej; thi du giver mit Hjerte at aande frit.
33 Ka koya mini Ya Ubangiji, don in bi ƙa’idodinka; sa’an nan zan kiyaye su har ƙarshe.
Lær mig, Herre! dine Skikkes Vej, og jeg vil bevare den indtil Enden.
34 Ka ba ni ganewa, zan kuwa kiyaye dokarka in kuma yi biyayya da ita da dukan zuciyata.
Undervis mig, at jeg maa bevare din Lov og holde den af ganske Hjerte.
35 Ka bi da ni a hanyar umarnanka, gama a can zan sami farin ciki.
Led mig frem ad dine Buds Sti; thi til den har jeg Lyst;
36 Ka juye zuciyata wajen farillanka ba wajen riba ta sonkai ba.
Bøj mit Hjerte til dine Vidnesbyrd og ikke til ulovlig Vinding.
37 Ka juye idanuna daga abubuwa marasa amfani; ka kiyaye raina bisa ga maganarka.
Bortvend mine Øjne, at de ikke se til Forfængelighed; hold mig i Live paa din Vej!
38 Ka cika alkawarinka ga bawanka, saboda a ji tsoronka.
Opfyld for din Tjener dit Ord, som er knyttet til Frygt for dig.
39 Ka kawar da shan kunyar da nake tsoro, gama dokokinka nagari ne.
Bortvend min Forsmædelse, som jeg frygtede for; thi dine Domme ere gode.
40 Ina marmarin farillanka ƙwarai! Ka kiyaye raina cikin adalcinka.
Se, jeg har Længsel efter dine Befalinger; hold mig i Live ved din Retfærdighed!
41 Bari ƙaunarka marar ƙarewa ta zo gare ni, ya Ubangiji, cetonka bisa ga alkawarinka;
Lad din Miskundhed, o Herre! komme over mig, din Frelse, efter dit Ord.
42 sa’an nan zan amsa wa masu cin mutuncina, gama na dogara ga maganarka.
Og jeg vil svare den, som forhaaner mig, et Ord; thi jeg har sat min Lid til dit Ord.
43 Kada ka ƙwace maganarka daga bakina, gama na sa zuciyata a dokokinka.
Og tag ikke Sandheds Ord aldeles fra min Mund; thi jeg har ventet paa dine Domme.
44 Kullayaumi zan yi biyayya da dokokinka, har abada abadin.
Og jeg vil stedse holde din Lov, evindelig og altid.
45 Zan yi ta yawo a sake gama na nemi farillanka.
Og lad mig vandre i det fri; thi jeg har søgt dine Befalinger.
46 Zan yi maganar farillanka a gaban sarakuna ba kuwa za a kunyata ni ba,
Og jeg vil tale om dine Vidnesbyrd for Konger og skal ikke beskæmmes.
47 gama ina farin ciki da umarnanka saboda ina ƙaunarsu.
Og jeg vil søge min Lyst i dine Bud, hvilke jeg elsker.
48 Na ɗaga hannuwana ga umarnanka, waɗanda nake ƙauna, ina kuma tunani a kan ƙa’idodinka.
Og jeg vil opløfte mine Hænder til dine Bud, hvilke jeg elsker, og grunde paa dine Skikke.
49 Tuna da maganarka ga bawanka, gama ka ba ni bege.
Kom Ordet til din Tjener i Hu, efterdi du lod mig haabe.
50 Ta’aziyyata cikin wahalata ita ce alkawarinka yana kiyaye raina.
Dette er min Trøst i min Elendighed; thi dit Ord har holdt mig i Live.
51 Masu fariya suna yi mini ba’a ba tare da an hana su ba, amma ban rabu da dokar ba.
De hovmodige have spottet mig saa saare, jeg bøjede ikke af fra din Lov.
52 Na tuna da dokokinka na tun dā, ya Ubangiji, na kuwa sami ta’aziyya a cikinsu.
Herre! dine Domme af Evighed kom jeg i Hu og blev trøstet.
53 Fushi ya kama ni saboda mugaye, waɗanda suka keta dokokinka.
Der betog mig en heftig Harme over de ugudelige, som forlade din Lov.
54 Ƙa’idodinka su ne kan waƙata a duk inda na sauka.
Dine Bud have været mine Sange i min Udlændigheds Hus.
55 Da dare na tuna da sunanka, ya Ubangiji, zan kuwa kiyaye dokarka.
Om Natten kom jeg dit Navn i Hu, o Herre! og holdt din Lov.
56 Wannan shi ne na saba yi, ina yin biyayya da farillanka.
Dette skete mig; thi dine Befalinger har jeg holdt.
57 Kai ne rabona, ya Ubangiji; na yi alkawarin in kiyaye maganarka.
Jeg sagde: Herren er min Del, jeg vil holde dine Ord.
58 Na nemi fuskarka da dukan zuciyata; ka yi mini alheri bisa ga alkawarinka.
Jeg bad ydmygt for dit Ansigt af ganske Hjerte: Vær mig naadig efter dit Ord!
59 Na lura da hanyoyina na kuma mayar da matakaina ga farillanka.
Jeg betænkte mine Veje, og jeg vil vende mine Fødder tilbage til dine Vidnesbyrd.
60 Zan gaggauta ba zan ɓata lokaci ba in yi biyayya da umarnanka.
Jeg hastede og tøvede ikke med at holde dine Bud.
61 Ko da yake mugaye sun ɗaura ni da igiyoyi, ba zan manta da dokokinka ba.
De ugudeliges Garn omspændte mig; din Lov glemte jeg ikke.
62 Da tsakar dare nakan tashi in gode maka saboda dokokinka masu adalci.
Midt om Natten staar jeg op, at prise dig for din Retfærdigheds Domme.
63 Ni aboki ne ga duk mai tsoronka, ga duk wanda yake bin farillanka.
Jeg har Samkvem med alle dem, som frygte dig, og med dem, som holde dine Befalinger.
64 Duniya ta cika da ƙaunarka, ya Ubangiji; ka koya mini ƙa’idodinka.
Jorden er fuld af din Miskundhed, Herre! lær mig dine Skikke.
65 Ka yi wa bawanka alheri bisa ga maganarka, ya Ubangiji.
Du gjorde vel imod din Tjener, Herre! efter dit Ord.
66 Ka koya mini sani da kuma hukunci mai kyau, gama na gaskata a umarnanka.
Lær mig at faa god Sans og Forstand; thi jeg tror paa dine Bud.
67 Kafin in sha wahala na kauce, amma yanzu ina biyayya da maganarka.
Før jeg blev ydmyget, for jeg vild, men nu holder jeg dit Ord.
68 Kai nagari ne, kuma abin da kake yi yana da kyau; ka koya mini ƙa’idodinka.
Du er god og gør godt; lær mig dine Skikke!
69 Ko da yake masu fariya sun shafe ni da ƙarairayi, na kiyaye farillanka da dukan zuciyata.
De hovmodige have opspundet Løgn imod mig; men jeg vil holde dine Befalinger af ganske Hjerte.
70 Zukatansu sun yi tauri da kuma marasa tausayi amma ina farin ciki a dokarka.
Deres Hjerte er følesløst som Fedt; men jeg forlyster mig ved din Lov.
71 Ya yi kyau da na sha wahala don in koyi ƙa’idodinka.
Det var mig godt, at jeg blev ydmyget, at jeg kunde lære dine Skikke.
72 Doka daga bakinka ya fi mini daraja fiye da azurfa da zinariya guda dubu.
Din Munds Lov er mig bedre end tusinde Stykker Guld og Sølv.
73 Hannuwanka ne suka yi suka kuma siffanta ni; ka ba ni ganewa don in koyi umarnanka.
Dine Hænder have skabt mig og beredt mig; giv mig Forstand, at jeg kan lære at kende dine Bud.
74 Bari waɗanda suke tsoronka su yi farin ciki sa’ad da suke gan ni, gama na sa zuciyata a maganarka.
De, som frygte dig, skulle se mig og glæde sig; thi jeg haaber paa dit Ord.
75 Ya Ubangiji na sani, cewa dokokinka masu adalci ne, kuma cikin aminci ka hore ni.
Herre! jeg ved, at dine Domme ere Retfærdighed, og at du af Trofasthed ydmygede mig.
76 Bari ƙaunarka marar ƙarewa tă yi mini ta’aziyya, bisa ga alkawarinka ga bawanka.
Lad dog din Miskundhed være mig til Trøst efter dit Ord til din Tjener.
77 Bari tausayinka yă zo mini don in rayu, gama dokarka ce farin cikina.
Lad din Barmhjertighed komme over mig, at jeg maa leve; thi din Lov er min Lyst.
78 Bari masu girman kai su sha kunya saboda abubuwa marasa kyau da suke yi mini ba dalili; amma zan yi tunani a kan farillanka.
Lad de hovmodige beskæmmes, thi uden Skel have de forurettet mig; men jeg vil grunde paa dine Befalinger.
79 Bari waɗanda suke tsoronka su juya gare ni, waɗanda suka gane da farillanka.
Lad dem vende tilbage til mig, som frygte dig, og som kende dine Vidnesbyrd.
80 Bari zuciyata ta kasance marar abin zargi wajen ƙa’idodinka, don kada in sha kunya.
Lad mit Hjerte være fuldkomment efter dine Skikke, at jeg ikke skal beskæmmes.
81 Raina ya tafke da marmari don cetonka, amma na sa zuciyata a maganarka.
Min Sjæl forsmægter af Længsel efter din Frelse; jeg haaber paa dit Ord.
82 Idanuna sun gaji, suna jiran alkawarinka; Na ce, “Yaushe za ka ta’azantar da ni?”
Mine Øjne forsmægtede af Længsel efter dit Ord, idet jeg sagde: Naar vil du trøste mig?
83 Ko da yake ni kamar salkar ruwan inabi ne a cikin hayaƙi, ban manta da ƙa’idodinka ba.
Thi jeg var ligesom en Læderflaske i Røg; dine Skikke glemte jeg ikke.
84 Har yaushe bawanka zai yi ta jira? Yaushe za ka hukunta masu tsananta mini?
Hvor mange ere vel din Tjeners Dage? naar vil du holde Dom over dem, som forfølge mig?
85 Masu girman kai sun haƙa mini rami, sun ƙetare dokarka.
De hovmodige grove Grave for mig, og de skikke sig ikke efter din Lov.
86 Dukan umarnanka abin dogara ne; ka taimake ni, gama mutane suna tsananta mini ba dalili.
Alle dine Bud ere Trofasthed; uden Grund forfølger man mig; hjælp mig!
87 Sun kusa gama da ni a duniya, amma ban bar bin farillanka ba.
De havde paa et lidet nær ødelagt mig i Landet; men jeg forlod ikke dine Befalinger.
88 Ka kiyaye raina bisa ga ƙaunarka, zan kuwa yi biyayya da farillan bakinka.
Hold mig i Live efter din Miskundhed, saa vil jeg bevare din Munds Vidnesbyrd.
89 Maganarka, ya Ubangiji madawwamiya ce; tana nan daram a cikin sammai.
Herre! dit Ord bestaar evindelig i Himlene.
90 Amincinka yana cin gaba cikin dukan zamanai; ka kafa duniya ta kuma dawwama.
Din Trofasthed varer fra Slægt til Slægt; du befæstede Jorden, og den stod fast.
91 Dokokinka sun dawwama har yă zuwa yau, gama dukan abubuwa suna maka hidima.
De bestaa endnu denne Dag efter dine Domme; thi de ere alle dine Tjenere.
92 Da ba don dokarka ce farin cikina ba, da na hallaka a cikin azabana.
Dersom ikke din Lov havde været min Lyst, da var jeg omkommen udi min Elendighed.
93 Ba zan taɓa manta da farillanka ba, gama ta wurinsu ne ka kiyaye raina.
Jeg skal i Evighed ikke forglemme dine Befalinger; thi ved dem holdt du mig i Live.
94 Ka cece ni, gama ni naka ne; na yi ƙoƙarin neman farillanka.
Din er jeg; frels mig; thi jeg søger efter dine Befalinger.
95 Mugaye suna jira su hallaka ni, amma zan yi ta tunani a kan farillanka.
De ugudelige biede paa mig for at lægge mig øde; jeg vil give Agt paa dine Vidnesbyrd.
96 Ga duk cikakke na ga kāsawa; amma umarnanka ba su da iyaka.
Jeg har set Ende paa al Fuldkommenhed; men dit Bud strækker sig saare vidt.
97 Kash, ga yadda nake ƙaunar dokarka! Ina tunani a kanta dukan yini.
Hvor kær har jeg din Lov! den er min Tanke den ganske Dag.
98 Umarnanka suna sa in zama mai hikima fiye da abokan gābana, gama kullum suna tare da ni.
Dine Bud gøre mig visere end mine Fjender; thi de ere for mig evindelig.
99 Ina da ganewa sosai fiye da dukan malamaina, gama ina tunani a kan farillanka.
Jeg blev klogere end alle mine Lærere; thi dine Vidnesbyrd ere min Tanke.
100 Ina da ganewa fiye da dattawa, gama ina biyayya da farillanka.
Jeg er bleven forstandigere end de gamle; thi jeg har bevaret dine Befalinger.
101 Na kiyaye ƙafafuna daga kowace muguwar hanya domin in yi biyayya da maganarka.
Jeg holdt mine Fødder tilbage fra al Ondskabens Sti, at jeg kunde holde dit Ord.
102 Ban rabu da dokokinka ba, gama kai da kanka ne ka koya mini.
Jeg afveg ikke fra dine Domme; thi du har lært mig det.
103 Ɗanɗanon maganarka akwai zaki, sun ma fi zuma zaki a bakina!
Hvor vare dine Ord søde for min Gane, mere end Honning for min Mund.
104 Na sami ganewa daga farillanka; saboda haka ina ƙin kowace hanyar da ba daidai ba.
Jeg er bleven forstandig af dine Befalinger; derfor hader jeg al Løgnens Sti.
105 Maganarka fitila ce ga ƙafafuna haske kuma a kan hanyata.
Dit Ord er en Lygte for min Fod og et Lys paa min Sti.
106 Na yi rantsuwa na kuma tabbatar da shi, cewa zan bi dokokinka masu adalci.
Jeg har svoret og holdt det, at jeg vilde bevare din Retfærdigheds Domme.
107 Na sha wahala sosai; ka kiyaye raina, ya Ubangiji, bisa ga maganarka.
Jeg er saare plaget; Herre! hold mig i Live efter dit Ord.
108 Ka karɓi yabon bakina da nake yi da yardar rai, ya Ubangiji, ka kuwa koya mini dokokinka.
Lad min Munds frivillige Ofre behage dig, Herre! og lær mig dine Domme.
109 Ko da yake kullum ina riƙe da raina a hannuwana, ba zan manta da dokarka ba.
Jeg gaar altid med Livet i Hænderne; dog har jeg ikke glemt din Lov.
110 Mugaye sun kafa mini tarko, amma ban kauce daga farillanka ba.
De ugudelige lagde Snarer for mig; dog for jeg ikke vild fra dine Befalinger.
111 Farillanka su ne gādona har abada; su ne farin cikin zuciyata.
Jeg fik dine Vidnesbyrd til Arv evindelig; thi de ere mit Hjertes Glæde.
112 Zuciyata ta shirya a kan kiyaye ƙa’idodinka har ƙarshe.
Jeg bøjede mit Hjerte til at gøre efter dine Skikke evindelig indtil Enden.
113 Na ƙi mutane masu baki biyu, amma ina ƙauna dokarka.
De tvesindede hader jeg; men din Lov elsker jeg.
114 Kai ne mafakata da garkuwata; na sa zuciyata a maganarka.
Du er mit Skjul og mit Skjold; jeg haaber paa dit Ord.
115 Ku rabu da ni, ku masu aikata mugunta, don in kiyaye umarnan Allahna!
Viger fra mig, I onde! og jeg vil bevare min Guds Bud.
116 Ka raya ni bisa ga alkawarinka, zan kuwa rayu; kada ka bari a gwale sa zuciyata.
Ophold mig efter dit Ord, at jeg maa leve, og lad mig ikke blive til Skamme med mit Haab!
117 Ka riƙe ni za a kuma cece ni; kullayaumi zan ɗauka ƙa’idodinka da muhimmanci.
Styrk mig, at jeg maa blive frelst, og jeg vil altid se hen til dine Skikke.
118 Ka ki dukan waɗanda suka kauce daga ƙa’idodinka, gama yaudararsu banza ne.
Du forkaster alle dem, som fare vild fra dine Skikke; thi deres Svig er Løgn.
119 Dukan mugayen duniya ka zubar kamar datti; saboda haka nake ƙaunar farillanka.
Du lod alle de ugudelige paa Jorden svinde bort som Skum; derfor elsker jeg dine Vidnesbyrd.
120 Naman jikina na rawan jiki don tsoronka; na cika da tsoron dokokinka.
Af Frygt for dig gyste min Krop, og jeg frygtede for dine Domme.
121 Na aikata abin da yake mai adalci da kuma daidai; kada ka ni a hannun masu danne ni.
Jeg gjorde Ret og Retfærdighed; du vil ikke overgive mig til dem, som gøre mig Vold!
122 Ka tabbatar da lafiyar bawanka; kada ka bar masu girman kai su danne ni.
Vær Borgen for din Tjener, ham til Bedste; lad de hovmodige ikke gøre mig Vold.
123 Idanuna sun gaji, da jiran cetonka, da jiran alkawarinka mai adalci.
Mine Øjne forsmægte af Længsel efter din Frelse og efter din Retfærdigheds Ord.
124 Ka yi da bawanka bisa ga ƙaunarka ka kuma koya mini ƙa’idodinka.
Gør med din Tjener efter din Miskundhed, og lær mig dine Skikke!
125 Ni bawanka ne, ka ba ni fahimi don in gane farillanka.
Jeg er din Tjener; undervis mig, at jeg maa kende dine Vidnesbyrd.
126 Lokaci ya yi da za ka yi wani abu, ya Ubangiji; ana karya dokarka.
Det er Tid, at Herren gør noget; de have brudt din Lov.
127 Saboda ina ƙaunar umarnanka fiye da zinariya, kai, fiye da zinariya zalla,
Derfor elsker jeg dine Bud mere end Guld og mere end fint Guld.
128 saboda kuma ina lura da dukan farillanka da kyau, na ƙi kowace hanyar da ba daidai ba.
Derfor holder jeg alle dine Befalinger om alle Ting for at være rette; jeg hader al Løgnens Vej.
129 Farillanka masu banmamaki ne; saboda haka nake yin biyayya da su.
Dine Vidnesbyrd ere underfulde; derfor bevarer min Sjæl dem.
130 Fassarar maganganunka sukan ba da haske; sukan ba da ganewa ga marar ilimi.
Dine Ords Aabenbaring spreder Lys og gør de enfoldige forstandige.
131 Ina hakkin da bakina a buɗe, ina marmarin umarnanka.
Jeg oplod min Mund og higede; thi jeg havde Længsel efter dine Bud.
132 Ka juye wurina ka kuma yi mini jinƙai, yadda kullum ka yi wa waɗanda suke ƙaunar sunanka.
Vend dig til mig, og vær mig naadig efter din Vis imod dem, der elske dit Navn.
133 Ka bi da sawuna bisa ga maganarka; kada ka bar zunubi yă mallake ni.
Befæst mine Trin ved dit Ord, og lad ingen Uret herske over mig!
134 Ka fanshe ni daga mutane masu danniya, don in yi biyayya da farillanka.
Udløs mig af Menneskers Vold, saa vil jeg holde dine Befalinger.
135 Ka sa fuskarka ta haskaka a kan bawanka ka kuma koya mini ƙa’idodinka.
Lad dit Ansigt lyse over din Tjener, og lær mig dine Skikke!
136 Hawaye suna malalowa daga idanuna kamar rafi, gama ba a biyayya da dokarka.
Der nedflød Vandstrømme af mine Øjne, fordi man ikke holdt din Lov.
137 Mai adalci ne kai, ya Ubangiji, dokokinka kuma daidai ne.
Du er retfærdig, Herre! og dine Domme ere retvise.
138 Farillan da ka shimfiɗa masu adalci ne; su kuma abin dogara ne ƙwarai.
Du har sat dine Vidnesbyrd som Retfærdighed og Trofasthed overmaade.
139 Kishina ya cinye ni ɗungum, gama abokan gābana sun yi biris da maganganunka.
Min Nidkærhed har lagt mig øde; thi mine Modstandere have glemt dine Ord.
140 An gwada alkawuranka sarai, bawanka kuwa yana ƙaunarsu.
Dit Ord er saare lutret, og din Tjener elsker det.
141 Ko da yake ni ba kome ba ne an kuwa rena ni, ba na manta da farillanka.
Jeg er liden og foragtet; men jeg glemmer ikke dine Befalinger.
142 Adalcinka dawwammame ne dokar kuma gaskiya ce.
Din Retfærdighed er Ret evindelig, og din Lov er Sandhed.
143 Wahala da damuwa suna a kaina, amma umarnanka su ne farin cikina.
Angest og Trængsel ramte mig; dine Bud ere min Lyst.
144 Farillanka daidai ne har abada; ka ba ni ganewa don in rayu.
Dine Vidnesbyrd ere Ret evindelig; undervis mig, saa lever jeg.
145 Na yi kira da dukan zuciyata; ka amsa mini, ya Ubangiji, zan kuwa yi biyayya da ƙa’idodinka.
Jeg har raabt af ganske Hjerte; bønhør mig, Herre! jeg vil bevare dine Skikke.
146 Na yi kira gare ka; ka cece ni zan kuwa kiyaye farillanka.
Jeg har raabt til dig; frels mig, og jeg vil holde fast ved dine Vidnesbyrd.
147 Na tashi kafin fitowar rana na kuma yi kukan neman taimako; na sa zuciyata a maganarka.
Jeg kom aarle i Daggry og raabte; jeg har haabet paa dit Ord.
148 Ban rufe idanuna ba dukan dare, don in yi tunani a kan alkawuranka.
Mine Øjne vare vaagne før Nattevagterne for at grunde paa dit Ord.
149 Ka ji muryata bisa ga ƙaunarka; ka kiyaye raina, ya Ubangiji, bisa ga dokokinka.
Hør min Røst efter din Miskundhed; Herre! hold mig i Live efter dine Domme;
150 Waɗanda suke ƙirƙiro mugayen dabaru suna nan kusa, amma suna nesa da dokarka.
De nærmede sig, som jage efter Skændselsgerninger; de vare langt borte fra din Lov.
151 Duk da haka kana kusa, ya Ubangiji, kuma dukan umarnanka gaskiya ne.
Nær er du, o Herre! og alle dine Bud ere Sandhed.
152 Tun tuni na koyi daga farillanka cewa ka kafa su su kasance har abada.
Jeg har forlængst hentet Kundskab af dine Vidnesbyrd; thi du har grundfæstet dem evindelig.
153 Ka dubi wahalata ka cece ni, gama ban manta da dokarka ba.
Se min Elendighed, og udfri mig; thi din Lov har jeg ikke glemt.
154 Ka kāre manufata ka kuma fanshe ni, ka cece rai na kamar yadda ka alkawarta!
Udfør min Sag, og genløs mig; hold mig i Live efter dit Ord.
155 Ceto yana nesa da mugaye, gama ba sa neman ƙa’idodinka.
Frelsen er fjern fra de ugudelige; thi de søge ikke dine Skikke.
156 Tausayinka da girma yake, ya Ubangiji; ka kiyaye raina bisa ga dokokinka.
Stor er din Barmhjertighed, o Herre! hold mig i Live efter dine Domme!
157 Maƙiya masu yawa ne suke tsananta mini, amma ban rabu da farillanka ba.
Mine Forfølgere og Modstandere ere mange; jeg har ikke bøjet mig fra dine Vidnesbyrd.
158 Na dubi marasa aminci da ƙyama, gama ba sa yin biyayya da maganarka.
Jeg har set de troløse og væmmedes ved dem; thi de holde ikke dit Ord.
159 Dubi yadda nake ƙaunar farillanka; ka kiyaye raina, ya Ubangiji, bisa ga ƙaunarka.
Se, hvor jeg har elsket dine Befalinger; Herre! hold mig i Live efter din Miskundhed.
160 Dukan maganganunka gaskiya ne; dukan dokokinka masu adalci madawwami ne.
Summen af dit Ord er Sandhed, og evig er al din Retfærdigheds Dom.
161 Masu mulki suna tsananta mini ba dalili, amma zuciyata na rawan jiki game da maganarka.
Fyrster forfulgte mig uden Aarsag, men mit Hjerte frygtede for dit Ord.
162 Ina farin ciki da alkawarinka kamar yadda wani kan sami ganima mai girma.
Jeg glæder mig over dit Ord som den, der finder et stort Bytte.
163 Na ƙi ina kuma ƙyamar ƙarya amma ina ƙaunar dokarka.
Jeg hader Løgn og har Vederstyggelighed dertil; din Lov elsker jeg.
164 Sau bakwai a rana ina yabonka saboda dokokinka masu adalci.
Jeg lovede dig syv Gange om Dagen for din Retfærdigheds Dommes Skyld.
165 Waɗanda suke ƙaunar dokarka suna da babban salama, kuma babu abin da zai sa su yi tuntuɓe.
Der er stor Fred for dem, som elske din Lov, og der er ikke Anstød for dem.
166 Ina jiran cetonka, ya Ubangiji, ina kuma bin umarnanka.
Jeg ventede paa din Frelse, Herre! og jeg udførte dine Bud.
167 Ina biyayya da farillanka, gama ina ƙaunarsu ƙwarai.
Min Sjæl holdt dine Vidnesbyrd, og jeg elskede dem saare.
168 Ina biyayya da farillanka da kuma koyarwarka, gama dukan hanyoyina sanannu ne gare ka.
Jeg holdt dine Befalinger og dine Vidnesbyrd; thi alle mine Veje ere aabenbare for dig.
169 Bari kukata ta zo gare ka, ya Ubangiji; ka ba ni ganewa bisa ga maganarka.
Lad mit Raab komme nær for dit Ansigt, Herre! og undervis mig efter dit Ord!
170 Bari roƙona yă zo gabanka; ka cece ni bisa ga alkawarinka.
Lad min ydmyge Begæring komme for dit Ansigt; fri mig efter dit Ord!
171 Bari leɓunana su cika da yabonka, gama ka koya mini ƙa’idodinka.
Mine Læber skulle udgyde Lovsang; thi du lærer mig dine Skikke.
172 Bari harshena yă rera game da maganarka, gama dukan umarnanka masu adalci ne.
Min Tunge skal genlyde af dit Ord; thi alle dine Bud ere Retfærdighed.
173 Bari hannunka yă kasance a shirye don yă taimake ni, gama na zaɓi farillanka.
Lad din Haand være mig til Hjælp; thi jeg har udvalgt dine Befalinger.
174 Ina marmarin cetonka, ya Ubangiji, dokarka kuwa ita ce farin cikina.
Jeg har Længsel efter din Frelse, Herre! og din Lov er min Lyst.
175 Bari in rayu don in yabe ka, bari kuma dokokinka su raya ni.
Maatte min Sjæl dog leve og love dig, og dine Domme hjælpe mig!
176 Na kauce kamar ɓatacciyar tunkiya. Ka nemi bawanka, gama ban manta da umarnanka ba.
Jeg har faret vild; opsøg din Tjener som det fortabte Faar; thi dine Bud har jeg ikke glemt.

< Zabura 119 >