< Zabura 118 >

1 Ku gode wa Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.
Tacker Herranom, ty han är mild, och hans godhet varar evinnerliga.
2 Bari Isra’ila yă ce, “Ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.”
Nu säge Israel: Hans godhet varar evinnerliga.
3 Bari gidan Haruna yă ce, “Ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.”
Nu säge Aarons hus: Hans godhet varar evinnerliga.
4 Bari waɗanda suke tsoron Ubangiji su ce, “Ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.”
Nu säge de som Herran frukta: Hans godhet varar evinnerliga.
5 Cikin azabata na yi kuka ga Ubangiji, ya kuwa amsa ta wurin’yantar da ni.
Uti ångest åkallade jag Herran; och Herren bönhörde mig, och tröste mig.
6 Ubangiji yana tare da ni; ba zan ji tsoro ba. Me mutum zai yi mini?
Herren är med mig, derföre fruktar jag mig intet; hvad kunna menniskor göra mig?
7 Ubangiji yana tare da ni; shi ne mai taimakona. Zan yi nasara a kan abokan gābana.
Herren är med mig, till att hjelpa mig; och jag vill lust se på mina fiendar.
8 Ya fi kyau in nemi mafaka a wurin Ubangiji da in dogara ga mutum.
Det är godt att förtrösta på Herran, och icke förlåta sig på menniskor.
9 Ya fi kyau in nemi mafaka a wurin Ubangiji da in dogara ga sarakuna.
Det är godt att förtrösta uppå Herran, och icke förlåta sig på Förstar.
10 Dukan al’ummai sun kewaye ni, amma a cikin sunan Ubangiji na hallaka su.
Alle Hedningar belägga mig; men i Herrans Namn vill jag förgöra dem.
11 Sun kewaye ni a kowane gefe, amma a cikin sunan Ubangiji na hallaka su.
De kringhvärfva mig på alla sidor; men i Herrans Namn vill jag nederlägga dem.
12 Sun rufe ni kamar ƙudan zuma, amma suka mutu nan da nan kamar ƙayayyuwa masu cin wuta; a cikin sunan Ubangiji na hallaka su.
De omlägga mig såsom bi, de släcka såsom eld i törne; men i Herrans Namn vill jag förgöra dem.
13 An ture ni baya na kusa fāɗuwa, amma Ubangiji ya taimake ni.
Man stöter mig, att jag falla skall; men Herren hjelper mig.
14 Ubangiji ne ƙarfina da waƙata; ya zama mai cetona.
Herren är min magt, och min psalm; och är min salighet.
15 Sowa ta farin ciki da nasara sun fito a cikin tentunan adalai, “Hannun dama na Ubangiji ya aikata manyan abubuwa!
Man sjunger med glädje om seger uti de rättfärdigas hyddom; Herrans högra hand behåller segren.
16 An ɗaga hannun dama na Ubangiji sama; hannun dama na Ubangiji ya aikata manyan abubuwa!”
Herrans högra hand är upphöjd; Herrans högra hand behåller segren.
17 Ba zan mutu ba amma zan rayu, zan kuwa yi shelar abin da Ubangiji ya yi.
Jag skall icke dö, utan lefva, och förkunna Herrans gerningar.
18 Ubangiji ya hore ni sosai, amma bai ba da ni ga mutuwa ba.
Herren näpser mig väl; men han gifver mig icke dödenom.
19 Buɗe mini ƙofofin adalci; zan shiga in kuma yi godiya ga Ubangiji.
Upplåter mig rättfärdighetenes portar, att jag må der ingå, och tacka Herranom.
20 Wannan ne ƙofar Ubangiji inda adalai za su shiga.
Det är Herrans port, de rättfärdige skola der ingå.
21 Zan yi maka godiya, domin ka amsa mini; ka zama mai cetona.
Jag tackar dig, att du näpste mig, och halp mig.
22 Zabura Dutsen da magina suka ƙi ya zama mai amfani;
Den stenen, som byggningsmännerna förkastade, är till en hörnsten vorden.
23 Ubangiji ne ya yi haka, kuma abu mai daraja ne a idanunmu.
Det är skedt af Herranom, och är ett under för vår ögon.
24 Wannan ita ce ranar da Ubangiji ya yi; bari mu yi farin ciki mu kuma yi murna a cikinta.
Detta är den dagen, den Herren gör; låt oss på honom fröjdas och glädjas.
25 Ya Ubangiji, ka cece mu; Ya Ubangiji, ka ba mu nasara.
O! Herre, hjelp; o! Herre, låt väl gå.
26 Mai albarka ne shi mai zuwa cikin sunan Ubangiji. Daga gidan Ubangiji muna sa muku albarka.
Lofvad vare den som kommer i Herrans Namn; vi välsigne eder, som af Herrans hus ären.
27 Ubangiji shi ne Allah ya kuma sa haskensa ya haskaka a kanmu. Da kwanoni a hannunmu, muka shiga jerin gwanon biki ku kai su ƙahoni na bagade.
Herren är Gud, den oss upplyser; pryder högtidena med löf, allt intill hornen på altaret.
28 Kai ne Allahna, zan kuwa yi maka godiya; kai ne Allahna, zan kuwa ɗaukaka ka.
Du äst min Gud, och jag tackar dig; min Gud, jag vill prisa dig.
29 Ku gode wa Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.
Tacker Herranom, ty han är mild, och hans godhet varar evinnerliga.

< Zabura 118 >