< Zabura 118 >

1 Ku gode wa Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.
Mshukuruni Bwana, kwa kuwa ni mwema; upendo wake wadumu milele.
2 Bari Isra’ila yă ce, “Ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.”
Israeli na aseme sasa: “Upendo wake wadumu milele.”
3 Bari gidan Haruna yă ce, “Ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.”
Nyumba ya Aroni na iseme sasa: “Upendo wake wadumu milele.”
4 Bari waɗanda suke tsoron Ubangiji su ce, “Ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.”
Wote wamchao Bwana na waseme sasa: “Upendo wake wadumu milele.”
5 Cikin azabata na yi kuka ga Ubangiji, ya kuwa amsa ta wurin’yantar da ni.
Wakati wa maumivu yangu makuu nilimlilia Bwana, naye akanijibu kwa kuniweka huru.
6 Ubangiji yana tare da ni; ba zan ji tsoro ba. Me mutum zai yi mini?
Bwana yuko pamoja nami, sitaogopa. Mwanadamu anaweza kunitenda nini?
7 Ubangiji yana tare da ni; shi ne mai taimakona. Zan yi nasara a kan abokan gābana.
Bwana yuko pamoja nami, yeye ni msaidizi wangu. Nitawatazama adui zangu wakiwa wameshindwa.
8 Ya fi kyau in nemi mafaka a wurin Ubangiji da in dogara ga mutum.
Ni bora kumkimbilia Bwana kuliko kumtumainia mwanadamu.
9 Ya fi kyau in nemi mafaka a wurin Ubangiji da in dogara ga sarakuna.
Ni bora kumkimbilia Bwana kuliko kuwatumainia wakuu.
10 Dukan al’ummai sun kewaye ni, amma a cikin sunan Ubangiji na hallaka su.
Mataifa yote yalinizunguka, lakini kwa jina la Bwana naliwakatilia mbali.
11 Sun kewaye ni a kowane gefe, amma a cikin sunan Ubangiji na hallaka su.
Walinizunguka pande zote, lakini kwa jina la Bwana naliwakatilia mbali.
12 Sun rufe ni kamar ƙudan zuma, amma suka mutu nan da nan kamar ƙayayyuwa masu cin wuta; a cikin sunan Ubangiji na hallaka su.
Walinizunguka kama kundi la nyuki, lakini walikufa haraka kama miiba iteketeayo; kwa jina la Bwana naliwakatilia mbali.
13 An ture ni baya na kusa fāɗuwa, amma Ubangiji ya taimake ni.
Nilisukumwa nyuma karibu kuanguka, lakini Bwana alinisaidia.
14 Ubangiji ne ƙarfina da waƙata; ya zama mai cetona.
Bwana ni nguvu yangu na wimbo wangu, yeye amefanyika wokovu wangu.
15 Sowa ta farin ciki da nasara sun fito a cikin tentunan adalai, “Hannun dama na Ubangiji ya aikata manyan abubuwa!
Sauti za shangwe na ushindi zinavuma hemani mwa wenye haki: “Mkono wa kuume wa Bwana umetenda mambo makuu!
16 An ɗaga hannun dama na Ubangiji sama; hannun dama na Ubangiji ya aikata manyan abubuwa!”
Mkono wa kuume wa Bwana umeinuliwa juu, mkono wa kuume wa Bwana umetenda mambo makuu!”
17 Ba zan mutu ba amma zan rayu, zan kuwa yi shelar abin da Ubangiji ya yi.
Sitakufa, bali nitaishi, nami nitatangaza yale Bwana aliyoyatenda.
18 Ubangiji ya hore ni sosai, amma bai ba da ni ga mutuwa ba.
Bwana ameniadhibu vikali, lakini hakuniacha nife.
19 Buɗe mini ƙofofin adalci; zan shiga in kuma yi godiya ga Ubangiji.
Nifungulie malango ya haki, nami nitaingia na kumshukuru Bwana.
20 Wannan ne ƙofar Ubangiji inda adalai za su shiga.
Hili ni lango la Bwana ambalo wenye haki wanaweza kuliingia.
21 Zan yi maka godiya, domin ka amsa mini; ka zama mai cetona.
Nitakushukuru, kwa kuwa ulinijibu, umekuwa wokovu wangu.
22 Zabura Dutsen da magina suka ƙi ya zama mai amfani;
Jiwe walilolikataa waashi, limekuwa jiwe kuu la pembeni.
23 Ubangiji ne ya yi haka, kuma abu mai daraja ne a idanunmu.
Bwana ametenda hili, nalo ni la kushangaza machoni petu.
24 Wannan ita ce ranar da Ubangiji ya yi; bari mu yi farin ciki mu kuma yi murna a cikinta.
Hii ndiyo siku Bwana aliyoifanya, tushangilie na kufurahi ndani yake.
25 Ya Ubangiji, ka cece mu; Ya Ubangiji, ka ba mu nasara.
Ee Bwana, tuokoe, Ee Bwana, utujalie mafanikio.
26 Mai albarka ne shi mai zuwa cikin sunan Ubangiji. Daga gidan Ubangiji muna sa muku albarka.
Heri yule ajaye kwa jina la Bwana. Kutoka nyumba ya Bwana tunakubariki.
27 Ubangiji shi ne Allah ya kuma sa haskensa ya haskaka a kanmu. Da kwanoni a hannunmu, muka shiga jerin gwanon biki ku kai su ƙahoni na bagade.
Bwana ndiye Mungu, naye ametuangazia nuru yake. Mkiwa na matawi mkononi, unganeni kwenye maandamano ya sikukuu hadi kwenye pembe za madhabahu.
28 Kai ne Allahna, zan kuwa yi maka godiya; kai ne Allahna, zan kuwa ɗaukaka ka.
Wewe ni Mungu wangu, nitakushukuru, wewe ni Mungu wangu, nitakutukuza.
29 Ku gode wa Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.
Mshukuruni Bwana kwa kuwa ni mwema; upendo wake wadumu milele.

< Zabura 118 >