< Zabura 118 >
1 Ku gode wa Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.
ALABAD á Jehová, porque es bueno; porque para siempre [es] su misericordia.
2 Bari Isra’ila yă ce, “Ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.”
Diga ahora Israel: Que para siempre [es] su misericordia.
3 Bari gidan Haruna yă ce, “Ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.”
Diga ahora la casa de Aarón: Que para siempre [es] su misericordia.
4 Bari waɗanda suke tsoron Ubangiji su ce, “Ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.”
Digan ahora los que temen á Jehová: Que para siempre [es] su misericordia.
5 Cikin azabata na yi kuka ga Ubangiji, ya kuwa amsa ta wurin’yantar da ni.
Desde la angustia invoqué á JAH; y respondióme JAH, [poniéndome] en anchura.
6 Ubangiji yana tare da ni; ba zan ji tsoro ba. Me mutum zai yi mini?
Jehová está por mí: no temeré lo que me pueda hacer el hombre.
7 Ubangiji yana tare da ni; shi ne mai taimakona. Zan yi nasara a kan abokan gābana.
Jehová está por mí entre los que me ayudan: por tanto yo veré [mi deseo] en los que me aborrecen.
8 Ya fi kyau in nemi mafaka a wurin Ubangiji da in dogara ga mutum.
Mejor es esperar en Jehová que esperar en hombre.
9 Ya fi kyau in nemi mafaka a wurin Ubangiji da in dogara ga sarakuna.
Mejor es esperar en Jehová que esperar en príncipes.
10 Dukan al’ummai sun kewaye ni, amma a cikin sunan Ubangiji na hallaka su.
Todas las gentes me cercaron: en nombre de Jehová, que yo los romperé.
11 Sun kewaye ni a kowane gefe, amma a cikin sunan Ubangiji na hallaka su.
Cercáronme y asediáronme: en nombre de Jehová, que yo los romperé.
12 Sun rufe ni kamar ƙudan zuma, amma suka mutu nan da nan kamar ƙayayyuwa masu cin wuta; a cikin sunan Ubangiji na hallaka su.
Cercáronme como abejas; fueron apagados como fuegos de espinos: en nombre de Jehová, que yo los romperé.
13 An ture ni baya na kusa fāɗuwa, amma Ubangiji ya taimake ni.
Empujásteme con violencia para que cayese: empero ayudóme Jehová.
14 Ubangiji ne ƙarfina da waƙata; ya zama mai cetona.
Mi fortaleza y mi canción es JAH; y él me ha sido por salud.
15 Sowa ta farin ciki da nasara sun fito a cikin tentunan adalai, “Hannun dama na Ubangiji ya aikata manyan abubuwa!
Voz de júbilo y de salvación hay en las tiendas de los justos: la diestra de Jehová hace proezas.
16 An ɗaga hannun dama na Ubangiji sama; hannun dama na Ubangiji ya aikata manyan abubuwa!”
La diestra de Jehová sublime: la diestra de Jehová hace valentías.
17 Ba zan mutu ba amma zan rayu, zan kuwa yi shelar abin da Ubangiji ya yi.
No moriré, sino que viviré, y contaré las obras de JAH.
18 Ubangiji ya hore ni sosai, amma bai ba da ni ga mutuwa ba.
Castigóme gravemente JAH: mas no me entregó á la muerte.
19 Buɗe mini ƙofofin adalci; zan shiga in kuma yi godiya ga Ubangiji.
Abridme las puertas de la justicia: entraré por ellas, alabaré á JAH.
20 Wannan ne ƙofar Ubangiji inda adalai za su shiga.
Esta puerta de Jehová, por ella entrarán los justos.
21 Zan yi maka godiya, domin ka amsa mini; ka zama mai cetona.
Te alabaré, porque me has oído, y me fuiste por salud.
22 Zabura Dutsen da magina suka ƙi ya zama mai amfani;
La piedra que desecharon los edificadores, ha venido á ser cabeza del ángulo.
23 Ubangiji ne ya yi haka, kuma abu mai daraja ne a idanunmu.
De parte de Jehová es esto: es maravilla en nuestros ojos.
24 Wannan ita ce ranar da Ubangiji ya yi; bari mu yi farin ciki mu kuma yi murna a cikinta.
Este es el día que hizo Jehová: nos gozaremos y alegraremos en él.
25 Ya Ubangiji, ka cece mu; Ya Ubangiji, ka ba mu nasara.
Oh Jehová, salva ahora, te ruego: oh Jehová, ruégote hagas prosperar ahora.
26 Mai albarka ne shi mai zuwa cikin sunan Ubangiji. Daga gidan Ubangiji muna sa muku albarka.
Bendito el que viene en nombre de Jehová: desde la casa de Jehová os bendecimos.
27 Ubangiji shi ne Allah ya kuma sa haskensa ya haskaka a kanmu. Da kwanoni a hannunmu, muka shiga jerin gwanon biki ku kai su ƙahoni na bagade.
Dios es Jehová que nos ha resplandecido: atad víctimas con cuerdas á los cuernos del altar.
28 Kai ne Allahna, zan kuwa yi maka godiya; kai ne Allahna, zan kuwa ɗaukaka ka.
Mi Dios eres tú, y á ti alabaré: Dios mío, á ti ensalzaré.
29 Ku gode wa Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.
Alabad á Jehová porque es bueno; porque para siempre [es] su misericordia.