< Zabura 118 >

1 Ku gode wa Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.
Alabád a Jehová, porque es bueno; porque para siempre es su misericordia.
2 Bari Isra’ila yă ce, “Ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.”
Diga ahora Israel: Que para siempre es su misericordia.
3 Bari gidan Haruna yă ce, “Ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.”
Digan ahora la casa de Aarón: Que para siempre es su misericordia.
4 Bari waɗanda suke tsoron Ubangiji su ce, “Ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.”
Digan ahora los que temen a Jehová: Que para siempre es su misericordia.
5 Cikin azabata na yi kuka ga Ubangiji, ya kuwa amsa ta wurin’yantar da ni.
Desde la angustia llamé a Jehová; y Jehová me respondió con anchura.
6 Ubangiji yana tare da ni; ba zan ji tsoro ba. Me mutum zai yi mini?
Jehová es por mí: no temeré lo que me haga el hombre.
7 Ubangiji yana tare da ni; shi ne mai taimakona. Zan yi nasara a kan abokan gābana.
Jehová es por mí entre los que me ayudan: por tanto yo veré venganza en los que me aborrecen.
8 Ya fi kyau in nemi mafaka a wurin Ubangiji da in dogara ga mutum.
Mejor es esperar en Jehová, que esperar en hombre.
9 Ya fi kyau in nemi mafaka a wurin Ubangiji da in dogara ga sarakuna.
Mejor es esperar en Jehová, que esperar en príncipes.
10 Dukan al’ummai sun kewaye ni, amma a cikin sunan Ubangiji na hallaka su.
Todas las gentes me cercaron: en nombre de Jehová, que yo los talaré.
11 Sun kewaye ni a kowane gefe, amma a cikin sunan Ubangiji na hallaka su.
Cercáronme, y tornáronme a cercar: en nombre de Jehová, que yo los talaré.
12 Sun rufe ni kamar ƙudan zuma, amma suka mutu nan da nan kamar ƙayayyuwa masu cin wuta; a cikin sunan Ubangiji na hallaka su.
Cercáronme como abejas, fueron apagados como fuego de espinos: en nombre de Jehová, que yo los talaré.
13 An ture ni baya na kusa fāɗuwa, amma Ubangiji ya taimake ni.
Rempujando me rempujaste para que cayese: mas Jehová me ayudó.
14 Ubangiji ne ƙarfina da waƙata; ya zama mai cetona.
Mi fortaleza y mi canción es Jehová; y él me ha sido por salud.
15 Sowa ta farin ciki da nasara sun fito a cikin tentunan adalai, “Hannun dama na Ubangiji ya aikata manyan abubuwa!
Voz de jubilación y de salud hay en las tiendas de los justos: la diestra de Jehová hace valentías.
16 An ɗaga hannun dama na Ubangiji sama; hannun dama na Ubangiji ya aikata manyan abubuwa!”
La diestra de Jehová sublime: la diestra de Jehová hace valentías.
17 Ba zan mutu ba amma zan rayu, zan kuwa yi shelar abin da Ubangiji ya yi.
No moriré, mas viviré; y contaré las obras de Jehová.
18 Ubangiji ya hore ni sosai, amma bai ba da ni ga mutuwa ba.
Castigando me castigó Jehová: mas no me entregó a la muerte.
19 Buɗe mini ƙofofin adalci; zan shiga in kuma yi godiya ga Ubangiji.
Abrídme las puertas de la justicia: entraré por ellas, alabaré a Jehová.
20 Wannan ne ƙofar Ubangiji inda adalai za su shiga.
Esta puerta de Jehová, los justos entrarán por ella.
21 Zan yi maka godiya, domin ka amsa mini; ka zama mai cetona.
Alabarte he; porque me oíste; y me fuiste por salud.
22 Zabura Dutsen da magina suka ƙi ya zama mai amfani;
La piedra que desecharon los edificadores, ha sido por cabeza de esquina.
23 Ubangiji ne ya yi haka, kuma abu mai daraja ne a idanunmu.
De parte de Jehová es esto, y es maravilla en nuestros ojos.
24 Wannan ita ce ranar da Ubangiji ya yi; bari mu yi farin ciki mu kuma yi murna a cikinta.
Este es el día que hizo Jehová: gozarnos hemos y alegrarnos hemos en él.
25 Ya Ubangiji, ka cece mu; Ya Ubangiji, ka ba mu nasara.
Ruégote, o! Jehová, salva ahora: ruégote, o! Jehová, haz ahora prosperar.
26 Mai albarka ne shi mai zuwa cikin sunan Ubangiji. Daga gidan Ubangiji muna sa muku albarka.
Bendito el que viene en nombre de Jehová: os bendecimos desde la casa de Jehová.
27 Ubangiji shi ne Allah ya kuma sa haskensa ya haskaka a kanmu. Da kwanoni a hannunmu, muka shiga jerin gwanon biki ku kai su ƙahoni na bagade.
Dios es Jehová, que nos ha resplandecido: atád víctimas con cuerdas a los cuernos del altar.
28 Kai ne Allahna, zan kuwa yi maka godiya; kai ne Allahna, zan kuwa ɗaukaka ka.
Dios mío eres tú, y a ti alabaré: Dios mío, a ti ensalzaré.
29 Ku gode wa Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.
Alabád a Jehová, porque es bueno; porque para siempre es su misericordia.

< Zabura 118 >