< Zabura 118 >

1 Ku gode wa Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.
Oh zahvaljujte se Gospodu, ker je dober, ker njegovo usmiljenje traja večno.
2 Bari Isra’ila yă ce, “Ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.”
Naj sedaj reče Izrael, da njegovo usmiljenje traja večno.
3 Bari gidan Haruna yă ce, “Ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.”
Naj sedaj reče Aronova hiša, da njegovo usmiljenje traja večno.
4 Bari waɗanda suke tsoron Ubangiji su ce, “Ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.”
Naj sedaj rečejo tisti, ki se bojijo Gospoda, da njegovo usmiljenje traja večno.
5 Cikin azabata na yi kuka ga Ubangiji, ya kuwa amsa ta wurin’yantar da ni.
V tegobi sem klical h Gospodu; Gospod mi je odgovoril in me postavil na velik kraj.
6 Ubangiji yana tare da ni; ba zan ji tsoro ba. Me mutum zai yi mini?
Gospod je na moji strani; ne bom se bal, kaj mi more storiti človek?
7 Ubangiji yana tare da ni; shi ne mai taimakona. Zan yi nasara a kan abokan gābana.
Gospod jemlje moj delež s tistimi, ki mi pomagajo, zato bom videl svojo željo na tistih, ki me sovražijo.
8 Ya fi kyau in nemi mafaka a wurin Ubangiji da in dogara ga mutum.
Bolje je zaupati v Gospoda, kakor zaupanje polagati v človeka.
9 Ya fi kyau in nemi mafaka a wurin Ubangiji da in dogara ga sarakuna.
Bolje je zaupati v Gospoda, kakor zaupanje polagati v prince.
10 Dukan al’ummai sun kewaye ni, amma a cikin sunan Ubangiji na hallaka su.
Vsi narodi so me obkrožili, toda uničil jih bom v Gospodovem imenu.
11 Sun kewaye ni a kowane gefe, amma a cikin sunan Ubangiji na hallaka su.
Obkrožili so me; da, obkrožili so me, toda uničil jih bom v Gospodovem imenu.
12 Sun rufe ni kamar ƙudan zuma, amma suka mutu nan da nan kamar ƙayayyuwa masu cin wuta; a cikin sunan Ubangiji na hallaka su.
Obkrožili so me kakor čebele; pogašeni so kakor ogenj iz trnja, kajti uničil jih bom v Gospodovem imenu.
13 An ture ni baya na kusa fāɗuwa, amma Ubangiji ya taimake ni.
Kruto si me sunil, da bi lahko padel, toda Gospod mi je pomagal.
14 Ubangiji ne ƙarfina da waƙata; ya zama mai cetona.
Gospod je moja moč in pesem in postal je rešitev moje duše.
15 Sowa ta farin ciki da nasara sun fito a cikin tentunan adalai, “Hannun dama na Ubangiji ya aikata manyan abubuwa!
Glas veselja in rešitve duš je v šotorskih svetiščih pravičnih; Gospodova desnica dela hrabro.
16 An ɗaga hannun dama na Ubangiji sama; hannun dama na Ubangiji ya aikata manyan abubuwa!”
Gospodova desnica je vzvišena, Gospodova desnica dela hrabro.
17 Ba zan mutu ba amma zan rayu, zan kuwa yi shelar abin da Ubangiji ya yi.
Ne bom umrl, temveč živel in oznanjal Gospodova dela.
18 Ubangiji ya hore ni sosai, amma bai ba da ni ga mutuwa ba.
Gospod me je boleče okaral, toda ni me izročil smrti.
19 Buɗe mini ƙofofin adalci; zan shiga in kuma yi godiya ga Ubangiji.
Odprite mi velika vrata pravičnosti; šel bom vanje in bom hvalil Gospoda,
20 Wannan ne ƙofar Ubangiji inda adalai za su shiga.
ta Gospodova velika vrata, v katera bodo vstopali pravični.
21 Zan yi maka godiya, domin ka amsa mini; ka zama mai cetona.
Hvalil te bom, kajti slišal si me in postal si rešitev moje duše.
22 Zabura Dutsen da magina suka ƙi ya zama mai amfani;
Kamen, ki so ga graditelji odklonili, je postal glava vogalnemu kamnu.
23 Ubangiji ne ya yi haka, kuma abu mai daraja ne a idanunmu.
To je Gospodovo delo, to je čudovito v naših očeh.
24 Wannan ita ce ranar da Ubangiji ya yi; bari mu yi farin ciki mu kuma yi murna a cikinta.
To je dan, ki ga je naredil Gospod; veselili se bomo in bili veseli v njem.
25 Ya Ubangiji, ka cece mu; Ya Ubangiji, ka ba mu nasara.
Reši sedaj, rotim te, oh Gospod. Oh Gospod, rotim te, pošlji uspevanje sedaj.
26 Mai albarka ne shi mai zuwa cikin sunan Ubangiji. Daga gidan Ubangiji muna sa muku albarka.
Blagoslovljen bodi, kdor prihaja v Gospodovem imenu. Blagoslavljamo vas iz Gospodove hiše.
27 Ubangiji shi ne Allah ya kuma sa haskensa ya haskaka a kanmu. Da kwanoni a hannunmu, muka shiga jerin gwanon biki ku kai su ƙahoni na bagade.
Bog je Gospod, ki nam je pokazal svetlobo. Žrtev povežite z vrvmi, celó k oltarnim rogovom.
28 Kai ne Allahna, zan kuwa yi maka godiya; kai ne Allahna, zan kuwa ɗaukaka ka.
Ti si moj Bog in tebe bom hvalil; ti si moj Bog, poviševal te bom.
29 Ku gode wa Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.
Oh zahvaljujte se Gospodu, ker je dober, kajti njegovo usmiljenje traja večno.

< Zabura 118 >