< Zabura 118 >

1 Ku gode wa Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.
Аллилуия. Славьте Господа, ибо Он благ, ибо вовек милость Его.
2 Bari Isra’ila yă ce, “Ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.”
Да скажет ныне дом Израилев: Он благ, ибо вовек милость Его.
3 Bari gidan Haruna yă ce, “Ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.”
Да скажет ныне дом Ааронов: Он благ, ибо вовек милость Его.
4 Bari waɗanda suke tsoron Ubangiji su ce, “Ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.”
Да скажут ныне боящиеся Господа: Он благ, ибо вовек милость Его.
5 Cikin azabata na yi kuka ga Ubangiji, ya kuwa amsa ta wurin’yantar da ni.
Из тесноты воззвал я к Господу, - и услышал меня, и на пространное место вывел меня Господь.
6 Ubangiji yana tare da ni; ba zan ji tsoro ba. Me mutum zai yi mini?
Господь за меня - не устрашусь: что сделает мне человек?
7 Ubangiji yana tare da ni; shi ne mai taimakona. Zan yi nasara a kan abokan gābana.
Господь мне помощник: буду смотреть на врагов моих.
8 Ya fi kyau in nemi mafaka a wurin Ubangiji da in dogara ga mutum.
Лучше уповать на Господа, нежели надеяться на человека.
9 Ya fi kyau in nemi mafaka a wurin Ubangiji da in dogara ga sarakuna.
Лучше уповать на Господа, нежели надеяться на князей.
10 Dukan al’ummai sun kewaye ni, amma a cikin sunan Ubangiji na hallaka su.
Все народы окружили меня, но именем Господним я низложил их;
11 Sun kewaye ni a kowane gefe, amma a cikin sunan Ubangiji na hallaka su.
обступили меня, окружили меня, но именем Господним я низложил их;
12 Sun rufe ni kamar ƙudan zuma, amma suka mutu nan da nan kamar ƙayayyuwa masu cin wuta; a cikin sunan Ubangiji na hallaka su.
окружили меня, как пчелы сот, и угасли, как огонь в терне: именем Господним я низложил их.
13 An ture ni baya na kusa fāɗuwa, amma Ubangiji ya taimake ni.
Сильно толкнули меня, чтобы я упал, но Господь поддержал меня.
14 Ubangiji ne ƙarfina da waƙata; ya zama mai cetona.
Господь - сила моя и песнь; Он соделался моим спасением.
15 Sowa ta farin ciki da nasara sun fito a cikin tentunan adalai, “Hannun dama na Ubangiji ya aikata manyan abubuwa!
Глас радости и спасения в жилищах праведников: десница Господня творит силу!
16 An ɗaga hannun dama na Ubangiji sama; hannun dama na Ubangiji ya aikata manyan abubuwa!”
Десница Господня высока, десница Господня творит силу!
17 Ba zan mutu ba amma zan rayu, zan kuwa yi shelar abin da Ubangiji ya yi.
Не умру, но буду жить и возвещать дела Господни.
18 Ubangiji ya hore ni sosai, amma bai ba da ni ga mutuwa ba.
Строго наказал меня Господь, но смерти не предал меня.
19 Buɗe mini ƙofofin adalci; zan shiga in kuma yi godiya ga Ubangiji.
Отворите мне врата правды; войду в них, прославлю Господа.
20 Wannan ne ƙofar Ubangiji inda adalai za su shiga.
Вот врата Господа; праведные войдут в них.
21 Zan yi maka godiya, domin ka amsa mini; ka zama mai cetona.
Славлю Тебя, что Ты услышал меня и соделался моим спасением.
22 Zabura Dutsen da magina suka ƙi ya zama mai amfani;
Камень, который отвергли строители, соделался главою угла:
23 Ubangiji ne ya yi haka, kuma abu mai daraja ne a idanunmu.
это - от Господа, и есть дивно в очах наших.
24 Wannan ita ce ranar da Ubangiji ya yi; bari mu yi farin ciki mu kuma yi murna a cikinta.
Сей день сотворил Господь: возрадуемся и возвеселимся в оный!
25 Ya Ubangiji, ka cece mu; Ya Ubangiji, ka ba mu nasara.
О, Господи, спаси же! О, Господи, споспешествуй же!
26 Mai albarka ne shi mai zuwa cikin sunan Ubangiji. Daga gidan Ubangiji muna sa muku albarka.
Благословен грядущий во имя Господне! Благословляем вас из дома Господня.
27 Ubangiji shi ne Allah ya kuma sa haskensa ya haskaka a kanmu. Da kwanoni a hannunmu, muka shiga jerin gwanon biki ku kai su ƙahoni na bagade.
Бог - Господь, и осиял нас; вяжите вервями жертву, ведите к рогам жертвенника.
28 Kai ne Allahna, zan kuwa yi maka godiya; kai ne Allahna, zan kuwa ɗaukaka ka.
Ты Бог мой: буду славить Тебя; Ты Бог мой: буду превозносить Тебя, буду славить Тебя, ибо Ты услышал меня и соделался моим спасением.
29 Ku gode wa Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.
Славьте Господа, ибо Он благ, ибо вовек милость Его.

< Zabura 118 >