< Zabura 118 >

1 Ku gode wa Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.
Pris Herren, for han er god, hans miskunnhet varer evindelig!
2 Bari Isra’ila yă ce, “Ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.”
Israel sie: Hans miskunnhet varer evindelig!
3 Bari gidan Haruna yă ce, “Ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.”
Arons hus sie: Hans miskunnhet varer evindelig!
4 Bari waɗanda suke tsoron Ubangiji su ce, “Ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.”
De som frykter Herren, sie: Hans miskunnhet varer evindelig!
5 Cikin azabata na yi kuka ga Ubangiji, ya kuwa amsa ta wurin’yantar da ni.
Ut av trengselen kalte jeg på Herren; Herren svarte mig og førte mig ut i fritt rum.
6 Ubangiji yana tare da ni; ba zan ji tsoro ba. Me mutum zai yi mini?
Herren er med mig, jeg frykter ikke; hvad skulde et menneske gjøre mig?
7 Ubangiji yana tare da ni; shi ne mai taimakona. Zan yi nasara a kan abokan gābana.
Herren er med mig, den som hjelper mig, og jeg skal se med lyst på dem som hater mig.
8 Ya fi kyau in nemi mafaka a wurin Ubangiji da in dogara ga mutum.
Det er bedre å sette sin lit til Herren enn å stole på mennesker.
9 Ya fi kyau in nemi mafaka a wurin Ubangiji da in dogara ga sarakuna.
Det er bedre å ta sin tilflukt til Herren enn å stole på fyrster.
10 Dukan al’ummai sun kewaye ni, amma a cikin sunan Ubangiji na hallaka su.
Alle hedninger omringer mig; i Herrens navn skal jeg hugge dem ned.
11 Sun kewaye ni a kowane gefe, amma a cikin sunan Ubangiji na hallaka su.
De omgir mig, ja, de omringer mig; i Herrens navn skal jeg hugge dem ned.
12 Sun rufe ni kamar ƙudan zuma, amma suka mutu nan da nan kamar ƙayayyuwa masu cin wuta; a cikin sunan Ubangiji na hallaka su.
De omgir mig som bier, de slukner som ild i tornebusker; i Herrens navn skal jeg hugge dem ned.
13 An ture ni baya na kusa fāɗuwa, amma Ubangiji ya taimake ni.
Hårdt støtte du mig forat jeg skulde falle; men Herren hjalp mig.
14 Ubangiji ne ƙarfina da waƙata; ya zama mai cetona.
Herren er min styrke og lovsang, og han blev mig til frelse.
15 Sowa ta farin ciki da nasara sun fito a cikin tentunan adalai, “Hannun dama na Ubangiji ya aikata manyan abubuwa!
Det høres fryderop om frelse i de rettferdiges telt; Herrens høire hånd gjør storverk.
16 An ɗaga hannun dama na Ubangiji sama; hannun dama na Ubangiji ya aikata manyan abubuwa!”
Herrens høire hånd ophøier, Herrens høire hånd gjør storverk.
17 Ba zan mutu ba amma zan rayu, zan kuwa yi shelar abin da Ubangiji ya yi.
Jeg skal ikke dø, men leve og fortelle Herrens gjerninger.
18 Ubangiji ya hore ni sosai, amma bai ba da ni ga mutuwa ba.
Hårdt tuktet Herren mig, men til døden overgav han mig ikke.
19 Buɗe mini ƙofofin adalci; zan shiga in kuma yi godiya ga Ubangiji.
Lukk op rettferdighets porter for mig! Jeg vil gå inn gjennem dem, jeg vil prise Herren.
20 Wannan ne ƙofar Ubangiji inda adalai za su shiga.
Dette er Herrens port; de rettferdige skal gå inn gjennem den.
21 Zan yi maka godiya, domin ka amsa mini; ka zama mai cetona.
Jeg vil prise dig fordi du svarte mig og blev mig til frelse.
22 Zabura Dutsen da magina suka ƙi ya zama mai amfani;
Den sten som bygningsmennene forkastet, er blitt hovedhjørnesten.
23 Ubangiji ne ya yi haka, kuma abu mai daraja ne a idanunmu.
Av Herren er dette gjort, det er underfullt i våre øine.
24 Wannan ita ce ranar da Ubangiji ya yi; bari mu yi farin ciki mu kuma yi murna a cikinta.
Dette er dagen som Herren har gjort; la oss fryde oss og glede oss på den!
25 Ya Ubangiji, ka cece mu; Ya Ubangiji, ka ba mu nasara.
Å Herre, frels dog! Å Herre, la det dog lykkes!
26 Mai albarka ne shi mai zuwa cikin sunan Ubangiji. Daga gidan Ubangiji muna sa muku albarka.
Velsignet være han som kommer i Herrens navn! Vi velsigner eder fra Herrens hus.
27 Ubangiji shi ne Allah ya kuma sa haskensa ya haskaka a kanmu. Da kwanoni a hannunmu, muka shiga jerin gwanon biki ku kai su ƙahoni na bagade.
Herren er Gud, og han lot det bli lyst for oss. Bind høitidsofferet med rep like inn til alterets horn!
28 Kai ne Allahna, zan kuwa yi maka godiya; kai ne Allahna, zan kuwa ɗaukaka ka.
Du er min Gud, og jeg vil love dig, min Gud, jeg vil ophøie dig.
29 Ku gode wa Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.
Pris Herren, for han er god, hans miskunnhet varer evindelig.

< Zabura 118 >