< Zabura 118 >

1 Ku gode wa Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.
Danket dem HERRN, denn er ist freundlich, ja, ewiglich währt seine Gnade!
2 Bari Isra’ila yă ce, “Ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.”
So bekenne denn Israel: »Ja, ewiglich währt seine Gnade!«
3 Bari gidan Haruna yă ce, “Ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.”
So bekenne denn Aarons Haus: »Ja, ewiglich währt seine Gnade!«
4 Bari waɗanda suke tsoron Ubangiji su ce, “Ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.”
So mögen denn alle Gottesfürcht’gen bekennen: »Ja, ewiglich währt seine Gnade!«
5 Cikin azabata na yi kuka ga Ubangiji, ya kuwa amsa ta wurin’yantar da ni.
Aus meiner Bedrängnis rief ich zum HERRN: da hat der HERR mich erhört, mir weiten Raum geschafft.
6 Ubangiji yana tare da ni; ba zan ji tsoro ba. Me mutum zai yi mini?
Ist der HERR für mich, so fürchte ich nichts: was können Menschen mir tun?
7 Ubangiji yana tare da ni; shi ne mai taimakona. Zan yi nasara a kan abokan gābana.
Tritt der HERR für mich zu meiner Hilfe ein, so werde ich siegreich jubeln über meine Feinde.
8 Ya fi kyau in nemi mafaka a wurin Ubangiji da in dogara ga mutum.
Besser ist’s auf den HERRN vertrauen als auf Menschen sich verlassen;
9 Ya fi kyau in nemi mafaka a wurin Ubangiji da in dogara ga sarakuna.
besser ist’s auf den HERRN vertrauen als auf Fürsten sich verlassen.
10 Dukan al’ummai sun kewaye ni, amma a cikin sunan Ubangiji na hallaka su.
Die Heidenvölker alle hatten mich umringt: im Namen des HERRN, so vertilgte ich sie;
11 Sun kewaye ni a kowane gefe, amma a cikin sunan Ubangiji na hallaka su.
sie hatten mich umringt, umzingelt: im Namen des HERRN, so vertilgte ich sie;
12 Sun rufe ni kamar ƙudan zuma, amma suka mutu nan da nan kamar ƙayayyuwa masu cin wuta; a cikin sunan Ubangiji na hallaka su.
sie hatten mich umringt wie Bienenschwärme; schnell wie ein Dornenfeuer sind sie erloschen: im Namen des HERRN, so vertilgte ich sie.
13 An ture ni baya na kusa fāɗuwa, amma Ubangiji ya taimake ni.
Man hat mich hart gestoßen, damit ich fallen sollte, doch der HERR hat mir geholfen.
14 Ubangiji ne ƙarfina da waƙata; ya zama mai cetona.
Meine Stärke und mein Lobpreis ist der HERR, und er ist mein Retter geworden.
15 Sowa ta farin ciki da nasara sun fito a cikin tentunan adalai, “Hannun dama na Ubangiji ya aikata manyan abubuwa!
Jubel und Siegeslieder erschallen in den Zelten der Gerechten: »Die Hand des HERRN schafft mächtige Taten,
16 An ɗaga hannun dama na Ubangiji sama; hannun dama na Ubangiji ya aikata manyan abubuwa!”
die Hand des HERRN erhöht, die Hand des HERRN schafft mächtige Taten!«
17 Ba zan mutu ba amma zan rayu, zan kuwa yi shelar abin da Ubangiji ya yi.
Ich werde nicht sterben, nein, ich werde leben und die Taten des HERRN verkünden.
18 Ubangiji ya hore ni sosai, amma bai ba da ni ga mutuwa ba.
Der HERR hat mich hart gezüchtigt, doch dem Tode mich nicht preisgegeben.
19 Buɗe mini ƙofofin adalci; zan shiga in kuma yi godiya ga Ubangiji.
Öffnet mir die Tore der Gerechtigkeit: ich will durch sie eingehn, dem HERRN zu danken. –
20 Wannan ne ƙofar Ubangiji inda adalai za su shiga.
Dies ist das Tor des HERRN: Gerechte dürfen hier eingehn. –
21 Zan yi maka godiya, domin ka amsa mini; ka zama mai cetona.
Ich danke dir, daß du mich erhört hast und bist mir ein Retter geworden.
22 Zabura Dutsen da magina suka ƙi ya zama mai amfani;
Der Stein, den die Bauleute verworfen haben, der ist zum Eckstein geworden;
23 Ubangiji ne ya yi haka, kuma abu mai daraja ne a idanunmu.
vom HERRN ist dies geschehn, in unsern Augen ein Wunder!
24 Wannan ita ce ranar da Ubangiji ya yi; bari mu yi farin ciki mu kuma yi murna a cikinta.
Dies ist der Tag, den der HERR gemacht hat: laßt uns jubeln und fröhlich an ihm sein! –
25 Ya Ubangiji, ka cece mu; Ya Ubangiji, ka ba mu nasara.
Ach hilf doch, HERR, ach, HERR, laß wohl gelingen! –
26 Mai albarka ne shi mai zuwa cikin sunan Ubangiji. Daga gidan Ubangiji muna sa muku albarka.
Gesegnet sei, der da kommt im Namen des HERRN! Wir segnen euch vom Hause des HERRN aus.
27 Ubangiji shi ne Allah ya kuma sa haskensa ya haskaka a kanmu. Da kwanoni a hannunmu, muka shiga jerin gwanon biki ku kai su ƙahoni na bagade.
Der HERR ist Gott, er hat uns Licht gegeben: schlinget den Reigen, mit Zweigen (geschmückt), bis an die Hörner des Altars!
28 Kai ne Allahna, zan kuwa yi maka godiya; kai ne Allahna, zan kuwa ɗaukaka ka.
Du bist mein Gott, ich will dir danken; mein Gott, ich will dich erheben!
29 Ku gode wa Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.
Danket dem HERRN, denn er ist freundlich, ja, ewiglich währt seine Gnade.

< Zabura 118 >