< Zabura 118 >

1 Ku gode wa Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.
Danket dem HERRN; denn er ist freundlich, und seine Güte währet ewiglich.
2 Bari Isra’ila yă ce, “Ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.”
Es sage nun Israel: Seine Güte währet ewiglich.
3 Bari gidan Haruna yă ce, “Ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.”
Es sage nun das Haus Aaron: Seine Güte währet ewiglich.
4 Bari waɗanda suke tsoron Ubangiji su ce, “Ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.”
Es sagen nun, die den HERRN fürchten: Seine Güte währet ewiglich.
5 Cikin azabata na yi kuka ga Ubangiji, ya kuwa amsa ta wurin’yantar da ni.
In der Angst rief ich den HERRN an, und der HERR erhörte mich und tröstete mich.
6 Ubangiji yana tare da ni; ba zan ji tsoro ba. Me mutum zai yi mini?
Der HERR ist mit mir, darum fürchte ich mich nicht; was können mir Menschen tun?
7 Ubangiji yana tare da ni; shi ne mai taimakona. Zan yi nasara a kan abokan gābana.
Der HERR ist mit mir, mir zu helfen; und ich will meine Lust sehen an meinen Feinden.
8 Ya fi kyau in nemi mafaka a wurin Ubangiji da in dogara ga mutum.
Es ist gut, auf den HERRN zu vertrauen, und nicht sich verlassen auf Menschen.
9 Ya fi kyau in nemi mafaka a wurin Ubangiji da in dogara ga sarakuna.
Es ist gut auf den HERRN vertrauen und nicht sich verlassen auf Fürsten.
10 Dukan al’ummai sun kewaye ni, amma a cikin sunan Ubangiji na hallaka su.
Alle Heiden umgeben mich; aber im Namen des HERRN will ich sie zerhauen.
11 Sun kewaye ni a kowane gefe, amma a cikin sunan Ubangiji na hallaka su.
Sie umgeben mich allenthalben; aber im Namen des HERRN will ich sie zerhauen.
12 Sun rufe ni kamar ƙudan zuma, amma suka mutu nan da nan kamar ƙayayyuwa masu cin wuta; a cikin sunan Ubangiji na hallaka su.
Sie umgeben mich wie Bienen; aber sie erlöschen wie Feuer in Dornen; im Namen des HERRN will ich sie zerhauen.
13 An ture ni baya na kusa fāɗuwa, amma Ubangiji ya taimake ni.
Man stößt mich, daß ich fallen soll; aber der HERR hilft mir.
14 Ubangiji ne ƙarfina da waƙata; ya zama mai cetona.
Der HERR ist meine Macht und mein Psalm und ist mein Heil.
15 Sowa ta farin ciki da nasara sun fito a cikin tentunan adalai, “Hannun dama na Ubangiji ya aikata manyan abubuwa!
Man singt mit Freuden vom Sieg in den Hütten der Gerechten: “Die Rechte des HERRN behält den Sieg;
16 An ɗaga hannun dama na Ubangiji sama; hannun dama na Ubangiji ya aikata manyan abubuwa!”
die Rechte des HERRN ist erhöht; die Rechte des HERRN behält den Sieg!”
17 Ba zan mutu ba amma zan rayu, zan kuwa yi shelar abin da Ubangiji ya yi.
Ich werde nicht sterben, sondern leben und des HERRN Werke verkündigen.
18 Ubangiji ya hore ni sosai, amma bai ba da ni ga mutuwa ba.
Der HERR züchtigt mich wohl; aber er gibt mich dem Tode nicht.
19 Buɗe mini ƙofofin adalci; zan shiga in kuma yi godiya ga Ubangiji.
Tut mir auf die Tore der Gerechtigkeit, daß ich dahin eingehe und dem HERRN danke.
20 Wannan ne ƙofar Ubangiji inda adalai za su shiga.
Das ist das Tor des HERRN; die Gerechten werden dahin eingehen.
21 Zan yi maka godiya, domin ka amsa mini; ka zama mai cetona.
Ich danke dir, daß du mich demütigst und hilfst mir.
22 Zabura Dutsen da magina suka ƙi ya zama mai amfani;
Der Stein, den die Bauleute verworfen haben, ist zum Eckstein geworden.
23 Ubangiji ne ya yi haka, kuma abu mai daraja ne a idanunmu.
Das ist vom HERRN geschehen und ist ein Wunder vor unsern Augen.
24 Wannan ita ce ranar da Ubangiji ya yi; bari mu yi farin ciki mu kuma yi murna a cikinta.
Dies ist der Tag, den der HERR macht; lasset uns freuen und fröhlich darinnen sein.
25 Ya Ubangiji, ka cece mu; Ya Ubangiji, ka ba mu nasara.
O HERR, hilf! o HERR, laß wohl gelingen!
26 Mai albarka ne shi mai zuwa cikin sunan Ubangiji. Daga gidan Ubangiji muna sa muku albarka.
Gelobt sei, der da kommt im Namen des HERRN! Wir segnen euch, die ihr vom Hause des HERRN seid.
27 Ubangiji shi ne Allah ya kuma sa haskensa ya haskaka a kanmu. Da kwanoni a hannunmu, muka shiga jerin gwanon biki ku kai su ƙahoni na bagade.
der HERR ist Gott, der uns erleuchtet. Schmücket das Fest mit Maien bis an die Hörner des Altars!
28 Kai ne Allahna, zan kuwa yi maka godiya; kai ne Allahna, zan kuwa ɗaukaka ka.
Du bist mein Gott, und ich danke dir; mein Gott, ich will dich preisen.
29 Ku gode wa Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.
Danket dem HERRN; denn er ist freundlich, und sein Güte währet ewiglich.

< Zabura 118 >