< Zabura 118 >
1 Ku gode wa Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.
Preiset [O. Danket] Jehova! denn er ist gut, denn seine Güte währt ewiglich.
2 Bari Isra’ila yă ce, “Ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.”
Es sage doch Israel: denn seine Güte währt ewiglich.
3 Bari gidan Haruna yă ce, “Ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.”
Es sage doch das Haus Aaron: denn seine Güte währt ewiglich.
4 Bari waɗanda suke tsoron Ubangiji su ce, “Ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.”
Es sagen doch, die Jehova fürchten: denn seine Güte währt ewiglich.
5 Cikin azabata na yi kuka ga Ubangiji, ya kuwa amsa ta wurin’yantar da ni.
Aus der Bedrängnis rief ich zu Jah; Jah erhörte mich und setzte mich in einen weiten Raum.
6 Ubangiji yana tare da ni; ba zan ji tsoro ba. Me mutum zai yi mini?
Jehova ist für mich, ich werde mich nicht fürchten; was sollte der Mensch mir tun?
7 Ubangiji yana tare da ni; shi ne mai taimakona. Zan yi nasara a kan abokan gābana.
Jehova ist für mich unter meinen Helfern, [S. die Anm. zu Ps. 54,4] und ich werde meine Lust sehen an meinen Hassern.
8 Ya fi kyau in nemi mafaka a wurin Ubangiji da in dogara ga mutum.
Es ist besser, auf Jehova zu trauen, als sich zu verlassen auf den Menschen.
9 Ya fi kyau in nemi mafaka a wurin Ubangiji da in dogara ga sarakuna.
Es ist besser, auf Jehova zu trauen, als sich zu verlassen auf Fürsten.
10 Dukan al’ummai sun kewaye ni, amma a cikin sunan Ubangiji na hallaka su.
Alle Nationen hatten mich umringt; gewiß, im Namen Jehovas vertilgte ich sie.
11 Sun kewaye ni a kowane gefe, amma a cikin sunan Ubangiji na hallaka su.
Sie hatten mich umringt, ja, mich umringt; gewiß, im Namen Jehovas vertilgte ich sie.
12 Sun rufe ni kamar ƙudan zuma, amma suka mutu nan da nan kamar ƙayayyuwa masu cin wuta; a cikin sunan Ubangiji na hallaka su.
Sie hatten mich umringt wie Bienen; sie sind erloschen wie Dornenfeuer; gewiß, im Namen Jehovas vertilgte ich sie.
13 An ture ni baya na kusa fāɗuwa, amma Ubangiji ya taimake ni.
Hart hast du mich gestoßen, um mich zu Fall zu bringen; aber Jehova hat mir geholfen.
14 Ubangiji ne ƙarfina da waƙata; ya zama mai cetona.
Meine Stärke und mein Gesang ist Jah, und er ist mir zur Rettung geworden.
15 Sowa ta farin ciki da nasara sun fito a cikin tentunan adalai, “Hannun dama na Ubangiji ya aikata manyan abubuwa!
Die Stimme des Jubels und der Rettung ist in den Zelten der Gerechten; die Rechte Jehovas tut mächtige Taten. [Eig. Mächtiges]
16 An ɗaga hannun dama na Ubangiji sama; hannun dama na Ubangiji ya aikata manyan abubuwa!”
Die Rechte Jehovas ist erhoben, die Rechte Jehovas tut mächtige Taten. [Eig. Mächtiges]
17 Ba zan mutu ba amma zan rayu, zan kuwa yi shelar abin da Ubangiji ya yi.
Ich werde nicht sterben, sondern leben und die Taten Jahs erzählen.
18 Ubangiji ya hore ni sosai, amma bai ba da ni ga mutuwa ba.
Hart [O. Wohl] hat mich Jah gezüchtigt, aber dem Tode hat er mich nicht übergeben.
19 Buɗe mini ƙofofin adalci; zan shiga in kuma yi godiya ga Ubangiji.
Öffnet mir die Tore der Gerechtigkeit: ich will durch sie eingehen, Jah will ich preisen. [O. danken; so auch v 21. 28. 29]
20 Wannan ne ƙofar Ubangiji inda adalai za su shiga.
Dies ist das Tor Jehovas: Die Gerechten werden durch dasselbe eingehen.
21 Zan yi maka godiya, domin ka amsa mini; ka zama mai cetona.
Ich will dich preisen, denn [O. daß] du hast mich erhört und bist mir zur Rettung geworden.
22 Zabura Dutsen da magina suka ƙi ya zama mai amfani;
Der Stein, den die Bauleute verworfen haben, ist zum Eckstein [W. Haupt der Ecke, d. h. Eck- und Hauptstein; ein Ausdruck, der nur hier vorkommt] geworden.
23 Ubangiji ne ya yi haka, kuma abu mai daraja ne a idanunmu.
Von Jehova ist dies geschehen; wunderbar ist es [O. er] in unseren Augen.
24 Wannan ita ce ranar da Ubangiji ya yi; bari mu yi farin ciki mu kuma yi murna a cikinta.
Dies ist der Tag, den Jehova gemacht hat; frohlocken wir und freuen wir uns in ihm.
25 Ya Ubangiji, ka cece mu; Ya Ubangiji, ka ba mu nasara.
Bitte, Jehova, rette doch! bitte, Jehova, gib doch Wohlfahrt!
26 Mai albarka ne shi mai zuwa cikin sunan Ubangiji. Daga gidan Ubangiji muna sa muku albarka.
Gesegnet, der da kommt im Namen Jehovas! Von dem Hause Jehovas aus haben wir euch gesegnet. [O. segnen wir euch]
27 Ubangiji shi ne Allah ya kuma sa haskensa ya haskaka a kanmu. Da kwanoni a hannunmu, muka shiga jerin gwanon biki ku kai su ƙahoni na bagade.
Jehova ist Gott, [El] und er hat uns Licht gegeben; bindet das Festopfer mit Stricken bis an die [O. und führet es bis zu den] Hörner des Altars.
28 Kai ne Allahna, zan kuwa yi maka godiya; kai ne Allahna, zan kuwa ɗaukaka ka.
Du bist mein Gott [El, ] und ich will dich preisen; mein Gott, ich will dich erheben.
29 Ku gode wa Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.
Preiset Jehova! denn er ist gut, denn seine Güte währt ewiglich.