< Zabura 118 >

1 Ku gode wa Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.
Rendez hommage au Seigneur, car il est bon, car sa grâce est éternelle.
2 Bari Isra’ila yă ce, “Ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.”
Qu’ainsi donc dise Israël, car sa grâce est éternelle;
3 Bari gidan Haruna yă ce, “Ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.”
qu’ainsi dise la maison d’Aaron, car sa grâce est éternelle;
4 Bari waɗanda suke tsoron Ubangiji su ce, “Ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.”
qu’ainsi disent ceux qui révèrent le Seigneur, car sa grâce est éternelle.
5 Cikin azabata na yi kuka ga Ubangiji, ya kuwa amsa ta wurin’yantar da ni.
Du fond de ma détresse j’ai invoqué l’Eternel: il m’a répondu en me mettant au large.
6 Ubangiji yana tare da ni; ba zan ji tsoro ba. Me mutum zai yi mini?
L’Eternel est avec moi, je ne crains rien: les hommes, que pourraient-ils contre moi?
7 Ubangiji yana tare da ni; shi ne mai taimakona. Zan yi nasara a kan abokan gābana.
L’Eternel est pour moi, avec ceux qui m’assistent; aussi me repaîtrai-je de la vue de mes haïsseurs.
8 Ya fi kyau in nemi mafaka a wurin Ubangiji da in dogara ga mutum.
Mieux vaut s’abriter en l’Eternel que de mettre sa confiance dans les hommes.
9 Ya fi kyau in nemi mafaka a wurin Ubangiji da in dogara ga sarakuna.
Mieux vaut s’abriter en l’Eternel que de mettre sa confiance dans les grands.
10 Dukan al’ummai sun kewaye ni, amma a cikin sunan Ubangiji na hallaka su.
Que tous les peuples m’enveloppent: au nom du Seigneur, je les taille en pièces.
11 Sun kewaye ni a kowane gefe, amma a cikin sunan Ubangiji na hallaka su.
Qu’ils m’entourent, qu’ils me cernent de toutes parts: au nom du Seigneur, je les taille en pièces.
12 Sun rufe ni kamar ƙudan zuma, amma suka mutu nan da nan kamar ƙayayyuwa masu cin wuta; a cikin sunan Ubangiji na hallaka su.
Qu’ils m’entourent comme des abeilles, soient brûlants comme un feu de broussailles: au nom du Seigneur, je les taille en pièces.
13 An ture ni baya na kusa fāɗuwa, amma Ubangiji ya taimake ni.
On m’a violemment poussé pour me faire tomber, mais l’Eternel m’a prêté assistance.
14 Ubangiji ne ƙarfina da waƙata; ya zama mai cetona.
Il est ma force et ma gloire, l’Eternel il a été un sauveur pour moi.
15 Sowa ta farin ciki da nasara sun fito a cikin tentunan adalai, “Hannun dama na Ubangiji ya aikata manyan abubuwa!
Le son des chants de joie et de salut retentit dans les tentes des justes: la droite de l’Eternel procure la victoire.
16 An ɗaga hannun dama na Ubangiji sama; hannun dama na Ubangiji ya aikata manyan abubuwa!”
La droite de l’Eternel est sublime: la droite de l’Eternel procure la victoire.
17 Ba zan mutu ba amma zan rayu, zan kuwa yi shelar abin da Ubangiji ya yi.
Je ne mourrai point, mais je vivrai, pour proclamer les œuvres du Seigneur.
18 Ubangiji ya hore ni sosai, amma bai ba da ni ga mutuwa ba.
Dieu m’avait durement éprouvé, mais il ne m’a point livré en proie à la mort.
19 Buɗe mini ƙofofin adalci; zan shiga in kuma yi godiya ga Ubangiji.
Ouvrez-moi les portes du salut, je veux les franchir, rendre hommage au Seigneur.
20 Wannan ne ƙofar Ubangiji inda adalai za su shiga.
Voici la porte de l’Eternel, les justes la franchiront!
21 Zan yi maka godiya, domin ka amsa mini; ka zama mai cetona.
Je te rends grâce pour m’avoir exaucé, tu as été mon sauveur.
22 Zabura Dutsen da magina suka ƙi ya zama mai amfani;
La pierre qu’ont dédaignée les architectes, elle est devenue la plus précieuse des pierres d’angle.
23 Ubangiji ne ya yi haka, kuma abu mai daraja ne a idanunmu.
C’Est l’Eternel qui l’a voulu ainsi, cela paraît merveilleux à nos yeux.
24 Wannan ita ce ranar da Ubangiji ya yi; bari mu yi farin ciki mu kuma yi murna a cikinta.
Ce jour, le Seigneur l’a préparé, consacrons-le par notre joie, par notre allégresse.
25 Ya Ubangiji, ka cece mu; Ya Ubangiji, ka ba mu nasara.
De grâce, Eternel, secours-nous; de grâce, Eternel, donne-nous le succès.
26 Mai albarka ne shi mai zuwa cikin sunan Ubangiji. Daga gidan Ubangiji muna sa muku albarka.
Béni soit celui qui vient au nom de l’Eternel! nous vous saluons du fond de la maison de l’Eternel.
27 Ubangiji shi ne Allah ya kuma sa haskensa ya haskaka a kanmu. Da kwanoni a hannunmu, muka shiga jerin gwanon biki ku kai su ƙahoni na bagade.
L’Eternel est le Dieu tout-puissant, il nous éclaire de sa lumière. Attachez la victime par des liens tout contre les angles de l’autel.
28 Kai ne Allahna, zan kuwa yi maka godiya; kai ne Allahna, zan kuwa ɗaukaka ka.
Tu es mon Dieu, je te rends hommage, mon Dieu, je veux t’exalter.
29 Ku gode wa Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.
Rendez hommage au Seigneur, car il est bon, car sa grâce dure éternellement.

< Zabura 118 >