< Zabura 118 >
1 Ku gode wa Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.
Give ye thanks to Jehovah, For good, for to the age [is] His kindness.
2 Bari Isra’ila yă ce, “Ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.”
I pray you, let Israel say, That, to the age [is] His kindness.
3 Bari gidan Haruna yă ce, “Ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.”
I pray you, let the house of Aaron say, That, to the age [is] His kindness.
4 Bari waɗanda suke tsoron Ubangiji su ce, “Ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.”
I pray you, let those fearing Jehovah say, That, to the age [is] His kindness.
5 Cikin azabata na yi kuka ga Ubangiji, ya kuwa amsa ta wurin’yantar da ni.
From the straitness I called Jah, Jah answered me in a broad place.
6 Ubangiji yana tare da ni; ba zan ji tsoro ba. Me mutum zai yi mini?
Jehovah [is] for me, I do not fear what man doth to me.
7 Ubangiji yana tare da ni; shi ne mai taimakona. Zan yi nasara a kan abokan gābana.
Jehovah [is] for me among my helpers, And I — I look on those hating me.
8 Ya fi kyau in nemi mafaka a wurin Ubangiji da in dogara ga mutum.
Better to take refuge in Jehovah than to trust in man,
9 Ya fi kyau in nemi mafaka a wurin Ubangiji da in dogara ga sarakuna.
Better to take refuge in Jehovah, Than to trust in princes.
10 Dukan al’ummai sun kewaye ni, amma a cikin sunan Ubangiji na hallaka su.
All nations have compassed me about, In the name of Jehovah I surely cut them off.
11 Sun kewaye ni a kowane gefe, amma a cikin sunan Ubangiji na hallaka su.
They have compassed me about, Yea, they have compassed me about, In the name of Jehovah I surely cut them off.
12 Sun rufe ni kamar ƙudan zuma, amma suka mutu nan da nan kamar ƙayayyuwa masu cin wuta; a cikin sunan Ubangiji na hallaka su.
They compassed me about as bees, They have been extinguished as a fire of thorns, In the name of Jehovah I surely cut them off.
13 An ture ni baya na kusa fāɗuwa, amma Ubangiji ya taimake ni.
Thou hast sorely thrust me to fall, And Jehovah hath helped me.
14 Ubangiji ne ƙarfina da waƙata; ya zama mai cetona.
My strength and song [is] Jah, And He is to me for salvation.
15 Sowa ta farin ciki da nasara sun fito a cikin tentunan adalai, “Hannun dama na Ubangiji ya aikata manyan abubuwa!
A voice of singing and salvation, [Is] in the tents of the righteous, The right hand of Jehovah is doing valiantly.
16 An ɗaga hannun dama na Ubangiji sama; hannun dama na Ubangiji ya aikata manyan abubuwa!”
The right hand of Jehovah is exalted, The right hand of Jehovah is doing valiantly.
17 Ba zan mutu ba amma zan rayu, zan kuwa yi shelar abin da Ubangiji ya yi.
I do not die, but live, And recount the works of Jah,
18 Ubangiji ya hore ni sosai, amma bai ba da ni ga mutuwa ba.
Jah hath sorely chastened me, And to death hath not given me up.
19 Buɗe mini ƙofofin adalci; zan shiga in kuma yi godiya ga Ubangiji.
Open ye to me gates of righteousness, I enter into them — I thank Jah.
20 Wannan ne ƙofar Ubangiji inda adalai za su shiga.
This [is] the gate to Jehovah, The righteous enter into it.
21 Zan yi maka godiya, domin ka amsa mini; ka zama mai cetona.
I thank Thee, for Thou hast answered me, And art to me for salvation.
22 Zabura Dutsen da magina suka ƙi ya zama mai amfani;
A stone the builders refused Hath become head of a corner.
23 Ubangiji ne ya yi haka, kuma abu mai daraja ne a idanunmu.
From Jehovah hath this been, It [is] wonderful in our eyes,
24 Wannan ita ce ranar da Ubangiji ya yi; bari mu yi farin ciki mu kuma yi murna a cikinta.
This [is] the day Jehovah hath made, We rejoice and are glad in it.
25 Ya Ubangiji, ka cece mu; Ya Ubangiji, ka ba mu nasara.
I beseech Thee, O Jehovah, save, I pray Thee, I beseech Thee, O Jehovah, prosper, I pray Thee.
26 Mai albarka ne shi mai zuwa cikin sunan Ubangiji. Daga gidan Ubangiji muna sa muku albarka.
Blessed [is] he who is coming In the name of Jehovah, We blessed you from the house of Jehovah,
27 Ubangiji shi ne Allah ya kuma sa haskensa ya haskaka a kanmu. Da kwanoni a hannunmu, muka shiga jerin gwanon biki ku kai su ƙahoni na bagade.
God [is] Jehovah, and He giveth to us light, Direct ye the festal-sacrifice with cords, Unto the horns of the altar.
28 Kai ne Allahna, zan kuwa yi maka godiya; kai ne Allahna, zan kuwa ɗaukaka ka.
My God Thou [art], and I confess Thee, My God, I exalt Thee.
29 Ku gode wa Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.
Give ye thanks to Jehovah, For good, for to the age, [is] His kindness!