< Zabura 118 >

1 Ku gode wa Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.
Give thanks to the Lord for his goodness, his kindness endures forever.
2 Bari Isra’ila yă ce, “Ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.”
Let the house of Israel now say: his kindness endures forever.
3 Bari gidan Haruna yă ce, “Ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.”
Let the house of Aaron now say: his kindness endures forever.
4 Bari waɗanda suke tsoron Ubangiji su ce, “Ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.”
Let those who fear the Lord now say: his kindness endures forever.
5 Cikin azabata na yi kuka ga Ubangiji, ya kuwa amsa ta wurin’yantar da ni.
Out of straits I called on the Lord, the Lord answered and gave me room.
6 Ubangiji yana tare da ni; ba zan ji tsoro ba. Me mutum zai yi mini?
The Lord is mine; I am fearless. What can mere people do to me?
7 Ubangiji yana tare da ni; shi ne mai taimakona. Zan yi nasara a kan abokan gābana.
The Lord is mine, as my help: I shall feast my eyes on my foes.
8 Ya fi kyau in nemi mafaka a wurin Ubangiji da in dogara ga mutum.
It is better to hide in the Lord than to trust in mortals.
9 Ya fi kyau in nemi mafaka a wurin Ubangiji da in dogara ga sarakuna.
It is better to hide in the Lord than to put any trust in princes.
10 Dukan al’ummai sun kewaye ni, amma a cikin sunan Ubangiji na hallaka su.
Everywhere heathen swarmed round me; in the name of the Lord I cut them down.
11 Sun kewaye ni a kowane gefe, amma a cikin sunan Ubangiji na hallaka su.
They swarmed, swarmed around me; in the name of the Lord I cut them down,
12 Sun rufe ni kamar ƙudan zuma, amma suka mutu nan da nan kamar ƙayayyuwa masu cin wuta; a cikin sunan Ubangiji na hallaka su.
they swarmed around me like bees, they blazed like a fire of thorns: in the name of the Lord I cut them down.
13 An ture ni baya na kusa fāɗuwa, amma Ubangiji ya taimake ni.
Sore they pushed me, to make me fall; but the Lord gave me his help.
14 Ubangiji ne ƙarfina da waƙata; ya zama mai cetona.
The Lord is my strength and my song, and he is become my salvation.
15 Sowa ta farin ciki da nasara sun fito a cikin tentunan adalai, “Hannun dama na Ubangiji ya aikata manyan abubuwa!
Hark! In the tents of the righteous glad cries of victory are ringing. The hand of the Lord has wrought bravely,
16 An ɗaga hannun dama na Ubangiji sama; hannun dama na Ubangiji ya aikata manyan abubuwa!”
the hand of the Lord is exalted, the hand of the Lord has wrought bravely.
17 Ba zan mutu ba amma zan rayu, zan kuwa yi shelar abin da Ubangiji ya yi.
I shall not die: nay, I shall live, to declare the works of the Lord.
18 Ubangiji ya hore ni sosai, amma bai ba da ni ga mutuwa ba.
Though the Lord has chastened me sore, he has not given me over to death. (The Procession arrives at the Temple)
19 Buɗe mini ƙofofin adalci; zan shiga in kuma yi godiya ga Ubangiji.
“Open to me the gates of victory. I would enter therein and give thanks to the Lord.” (The Welcome)
20 Wannan ne ƙofar Ubangiji inda adalai za su shiga.
“This is the gate of the Lord: the righteous may enter therein;”
21 Zan yi maka godiya, domin ka amsa mini; ka zama mai cetona.
I thank you because you have heard me, and are become my salvation.
22 Zabura Dutsen da magina suka ƙi ya zama mai amfani;
The stone which the builders despised is become the head-stone of the corner.
23 Ubangiji ne ya yi haka, kuma abu mai daraja ne a idanunmu.
This has been wrought by the Lord; it is marvelous in our eyes.
24 Wannan ita ce ranar da Ubangiji ya yi; bari mu yi farin ciki mu kuma yi murna a cikinta.
This day is the Lord’s own creation: in it let us joy and be glad.
25 Ya Ubangiji, ka cece mu; Ya Ubangiji, ka ba mu nasara.
O Lord, save us, we pray, O Lord, prosper, we pray.
26 Mai albarka ne shi mai zuwa cikin sunan Ubangiji. Daga gidan Ubangiji muna sa muku albarka.
Blessed the one who enters in the name of the Lord. From the house of the Lord we bless you.
27 Ubangiji shi ne Allah ya kuma sa haskensa ya haskaka a kanmu. Da kwanoni a hannunmu, muka shiga jerin gwanon biki ku kai su ƙahoni na bagade.
The Lord is God, he has given us light. Wreathe the dance with boughs, till they touch the horns of the altar.
28 Kai ne Allahna, zan kuwa yi maka godiya; kai ne Allahna, zan kuwa ɗaukaka ka.
You are my God, I will thank you; O my God, I will exalt you.
29 Ku gode wa Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.
Give thanks to the Lord for his goodness: his kindness endures forever.

< Zabura 118 >