< Zabura 118 >

1 Ku gode wa Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.
O give thanks to the LORD, for he is good; For his kindness endureth for ever!
2 Bari Isra’ila yă ce, “Ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.”
Let Israel now say, His kindness endureth for ever!
3 Bari gidan Haruna yă ce, “Ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.”
Let the house of Aaron now say, His goodness endureth for ever!
4 Bari waɗanda suke tsoron Ubangiji su ce, “Ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.”
Let all who fear the LORD say, His kindness endureth for ever!
5 Cikin azabata na yi kuka ga Ubangiji, ya kuwa amsa ta wurin’yantar da ni.
I called upon the LORD in distress; He heard, and set me in a wide place.
6 Ubangiji yana tare da ni; ba zan ji tsoro ba. Me mutum zai yi mini?
The LORD is on my side, I will not fear: What can man do to me?
7 Ubangiji yana tare da ni; shi ne mai taimakona. Zan yi nasara a kan abokan gābana.
The LORD is my helper; I shall see my desire upon my enemies.
8 Ya fi kyau in nemi mafaka a wurin Ubangiji da in dogara ga mutum.
It is better to trust in the LORD Than to put confidence in man;
9 Ya fi kyau in nemi mafaka a wurin Ubangiji da in dogara ga sarakuna.
It is better to trust in the LORD Than to put confidence in princes.
10 Dukan al’ummai sun kewaye ni, amma a cikin sunan Ubangiji na hallaka su.
All the nations beset me around, But in the name of the LORD I destroyed them.
11 Sun kewaye ni a kowane gefe, amma a cikin sunan Ubangiji na hallaka su.
They beset me on every side; But in the name of the LORD I destroyed them.
12 Sun rufe ni kamar ƙudan zuma, amma suka mutu nan da nan kamar ƙayayyuwa masu cin wuta; a cikin sunan Ubangiji na hallaka su.
They beset me around like bees; They were quenched like the fire of thorns, For in the name of the LORD I destroyed them.
13 An ture ni baya na kusa fāɗuwa, amma Ubangiji ya taimake ni.
Thou didst assail me with violence to bring me down! But the LORD was my support.
14 Ubangiji ne ƙarfina da waƙata; ya zama mai cetona.
The LORD is my glory and my song; For to him I owe my salvation.
15 Sowa ta farin ciki da nasara sun fito a cikin tentunan adalai, “Hannun dama na Ubangiji ya aikata manyan abubuwa!
The voice of joy and salvation is in the habitations of the righteous: “The right hand of the LORD doeth valiantly;
16 An ɗaga hannun dama na Ubangiji sama; hannun dama na Ubangiji ya aikata manyan abubuwa!”
The right hand of the LORD is exalted; The right hand of the LORD doeth valiantly.”
17 Ba zan mutu ba amma zan rayu, zan kuwa yi shelar abin da Ubangiji ya yi.
I shall not die, but live, And declare the deeds of the LORD.
18 Ubangiji ya hore ni sosai, amma bai ba da ni ga mutuwa ba.
The LORD hath sorely chastened me, But he hath not given me over to death.
19 Buɗe mini ƙofofin adalci; zan shiga in kuma yi godiya ga Ubangiji.
Open to me the gates of righteousness, That I may go in, and praise the LORD!
20 Wannan ne ƙofar Ubangiji inda adalai za su shiga.
This is the gate of the LORD, Through which the righteous enter.
21 Zan yi maka godiya, domin ka amsa mini; ka zama mai cetona.
I praise thee that thou hast heard me, And hast been my salvation.
22 Zabura Dutsen da magina suka ƙi ya zama mai amfani;
“The stone which the builders rejected Hath become the chief corner-stone.
23 Ubangiji ne ya yi haka, kuma abu mai daraja ne a idanunmu.
This is the LORD'S doing; It is marvellous in our eyes!
24 Wannan ita ce ranar da Ubangiji ya yi; bari mu yi farin ciki mu kuma yi murna a cikinta.
This is the day which the LORD hath made; Let us rejoice and be glad in it!
25 Ya Ubangiji, ka cece mu; Ya Ubangiji, ka ba mu nasara.
Hear, O LORD! and bless us! Hear, O LORD! and send us prosperity!”
26 Mai albarka ne shi mai zuwa cikin sunan Ubangiji. Daga gidan Ubangiji muna sa muku albarka.
“Blessed be he that cometh in the name of the LORD! We bless you from the house of the LORD.”
27 Ubangiji shi ne Allah ya kuma sa haskensa ya haskaka a kanmu. Da kwanoni a hannunmu, muka shiga jerin gwanon biki ku kai su ƙahoni na bagade.
“Jehovah is God, he hath shone upon us: Bind the sacrifice with cords to the horns of the altar!”
28 Kai ne Allahna, zan kuwa yi maka godiya; kai ne Allahna, zan kuwa ɗaukaka ka.
Thou art my God, and I will praise thee; Thou art my God, and I will exalt thee!
29 Ku gode wa Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.
O give thanks to the LORD, for he is good; For his kindness endureth for ever!

< Zabura 118 >