< Zabura 118 >
1 Ku gode wa Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.
O give praise to the Lord, for he is good: for his mercy is unchanging for ever.
2 Bari Isra’ila yă ce, “Ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.”
Let Israel now say, that his mercy is unchanging for ever.
3 Bari gidan Haruna yă ce, “Ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.”
Let the house of Aaron now say, that his mercy is unchanging for ever.
4 Bari waɗanda suke tsoron Ubangiji su ce, “Ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.”
Let all worshippers of the Lord now say, that his mercy is unchanging for ever.
5 Cikin azabata na yi kuka ga Ubangiji, ya kuwa amsa ta wurin’yantar da ni.
I made my prayer to the Lord in my trouble: and the Lord gave me an answer, and put me in a wide place.
6 Ubangiji yana tare da ni; ba zan ji tsoro ba. Me mutum zai yi mini?
The Lord is on my side; I will have no fear: what is man able to do to me?
7 Ubangiji yana tare da ni; shi ne mai taimakona. Zan yi nasara a kan abokan gābana.
The Lord is my great helper: I will see my desire against my haters.
8 Ya fi kyau in nemi mafaka a wurin Ubangiji da in dogara ga mutum.
It is better to have faith in the Lord than to put one's hope in man.
9 Ya fi kyau in nemi mafaka a wurin Ubangiji da in dogara ga sarakuna.
It is better to have faith in the Lord than to put one's hope in rulers.
10 Dukan al’ummai sun kewaye ni, amma a cikin sunan Ubangiji na hallaka su.
All the nations have come round me; but in the name of the Lord I will have them cut down.
11 Sun kewaye ni a kowane gefe, amma a cikin sunan Ubangiji na hallaka su.
They are round me, yes, they are all about me; but in the name of the Lord I will have them cut down.
12 Sun rufe ni kamar ƙudan zuma, amma suka mutu nan da nan kamar ƙayayyuwa masu cin wuta; a cikin sunan Ubangiji na hallaka su.
They are round me like bees; but they are put out like a fire among thorns; for in the name of the Lord I will have them cut down.
13 An ture ni baya na kusa fāɗuwa, amma Ubangiji ya taimake ni.
I have been hard pushed by you, so that I might have a fall: but the Lord was my helper.
14 Ubangiji ne ƙarfina da waƙata; ya zama mai cetona.
The Lord is my strength and my song; he has become my salvation.
15 Sowa ta farin ciki da nasara sun fito a cikin tentunan adalai, “Hannun dama na Ubangiji ya aikata manyan abubuwa!
The sound of joy and salvation is in the tents of the upright; the right hand of the Lord does works of power.
16 An ɗaga hannun dama na Ubangiji sama; hannun dama na Ubangiji ya aikata manyan abubuwa!”
The right hand of the Lord is lifted up; the right hand of the Lord does works of power.
17 Ba zan mutu ba amma zan rayu, zan kuwa yi shelar abin da Ubangiji ya yi.
Life and not death will be my part, and I will give out the story of the works of the Lord.
18 Ubangiji ya hore ni sosai, amma bai ba da ni ga mutuwa ba.
The hand of Jah has been hard on me; but he has not given me up to death.
19 Buɗe mini ƙofofin adalci; zan shiga in kuma yi godiya ga Ubangiji.
Let the doors of righteousness be open to me; I will go in and give praise to the Lord.
20 Wannan ne ƙofar Ubangiji inda adalai za su shiga.
This is the door of the Lord's house; the workers of righteousness will go in through it.
21 Zan yi maka godiya, domin ka amsa mini; ka zama mai cetona.
I will give you praise, for you have given me an answer, and have become my salvation.
22 Zabura Dutsen da magina suka ƙi ya zama mai amfani;
The stone which the builders put on one side has become the chief stone of the building.
23 Ubangiji ne ya yi haka, kuma abu mai daraja ne a idanunmu.
This is the Lord's doing; it is a wonder in our eyes.
24 Wannan ita ce ranar da Ubangiji ya yi; bari mu yi farin ciki mu kuma yi murna a cikinta.
This is the day which the Lord has made; we will be full of joy and delight in it.
25 Ya Ubangiji, ka cece mu; Ya Ubangiji, ka ba mu nasara.
Send salvation now, O Lord; Lord, send us your blessing.
26 Mai albarka ne shi mai zuwa cikin sunan Ubangiji. Daga gidan Ubangiji muna sa muku albarka.
A blessing be on him who comes in the name of the Lord; we give you blessing from the house of the Lord.
27 Ubangiji shi ne Allah ya kuma sa haskensa ya haskaka a kanmu. Da kwanoni a hannunmu, muka shiga jerin gwanon biki ku kai su ƙahoni na bagade.
The Lord is God, and he has given us light; let the holy dance be ordered with branches, even up to the horns of the altar.
28 Kai ne Allahna, zan kuwa yi maka godiya; kai ne Allahna, zan kuwa ɗaukaka ka.
You are my God, and I will give you praise; my God, and I will give honour to your name.
29 Ku gode wa Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.
O give praise to the Lord, for he is good: for his mercy is unchanging for ever.