< Zabura 118 >
1 Ku gode wa Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.
Priser Herren; thi han er god; thi hans Miskundhed er evindelig.
2 Bari Isra’ila yă ce, “Ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.”
Israel sige: Hans Miskundhed er evindelig.
3 Bari gidan Haruna yă ce, “Ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.”
De af Arons Hus sige: Hans Miskundhed er evindelig.
4 Bari waɗanda suke tsoron Ubangiji su ce, “Ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.”
De, som frygte Herren, sige: Hans Miskundhed er evindelig.
5 Cikin azabata na yi kuka ga Ubangiji, ya kuwa amsa ta wurin’yantar da ni.
I Trængselen kaldte jeg paa Herren; Herren bønhørte mig i det fri.
6 Ubangiji yana tare da ni; ba zan ji tsoro ba. Me mutum zai yi mini?
Herren er med mig, jeg vil ikke frygte, hvad kan et Menneske gøre mig?
7 Ubangiji yana tare da ni; shi ne mai taimakona. Zan yi nasara a kan abokan gābana.
Herren er med mig, han er min Hjælper; og jeg skal se min Glæde paa mine Avindsmænd.
8 Ya fi kyau in nemi mafaka a wurin Ubangiji da in dogara ga mutum.
Det er bedre at sætte Lid til Herren end at forlade sig paa Mennesker.
9 Ya fi kyau in nemi mafaka a wurin Ubangiji da in dogara ga sarakuna.
Det er bedre at sætte Lid til Herren end at forlade sig paa Fyrster.
10 Dukan al’ummai sun kewaye ni, amma a cikin sunan Ubangiji na hallaka su.
Alle Hedninger have omringet mig; i Herrens Navn vil jeg nedhugge dem.
11 Sun kewaye ni a kowane gefe, amma a cikin sunan Ubangiji na hallaka su.
De have omringet mig, ja, de have omringet mig; i Herrens Navn vil jeg nedhugge dem.
12 Sun rufe ni kamar ƙudan zuma, amma suka mutu nan da nan kamar ƙayayyuwa masu cin wuta; a cikin sunan Ubangiji na hallaka su.
De have omringet mig som Bier, de ere udslukte som Ild i Torne; i Herrens Navn vil jeg nedhugge dem.
13 An ture ni baya na kusa fāɗuwa, amma Ubangiji ya taimake ni.
Du stødte mig haardt, at jeg skulde falde; men Herren hjalp mig.
14 Ubangiji ne ƙarfina da waƙata; ya zama mai cetona.
Herren er min Styrke og min Sang, og han blev mig til Frelse.
15 Sowa ta farin ciki da nasara sun fito a cikin tentunan adalai, “Hannun dama na Ubangiji ya aikata manyan abubuwa!
Fryds og Frelses Røst er i de retfærdiges Telte; Herrens højre Haand skaber Kraft.
16 An ɗaga hannun dama na Ubangiji sama; hannun dama na Ubangiji ya aikata manyan abubuwa!”
Herrens højre Haand er ophøjet, Herrens højre Haand skaber Kraft.
17 Ba zan mutu ba amma zan rayu, zan kuwa yi shelar abin da Ubangiji ya yi.
Jeg skal ikke dø, men jeg skal leve, og jeg skal fortælle Herrens Gerninger.
18 Ubangiji ya hore ni sosai, amma bai ba da ni ga mutuwa ba.
Herren tugtede mig vel, men gav mig ikke hen i Døden.
19 Buɗe mini ƙofofin adalci; zan shiga in kuma yi godiya ga Ubangiji.
Lader Retfærdigheds Porte op for mig, jeg vil gaa ind ad dem, jeg vil takke Herren.
20 Wannan ne ƙofar Ubangiji inda adalai za su shiga.
Denne er Herrens Port, de retfærdige skulle gaa ind ad den.
21 Zan yi maka godiya, domin ka amsa mini; ka zama mai cetona.
Jeg vil takke dig; thi du bønhørte mig, og du blev mig til Frelse.
22 Zabura Dutsen da magina suka ƙi ya zama mai amfani;
Den Sten, som Bygningsmændene forkastede, er bleven til en Hovedhjørnesten.
23 Ubangiji ne ya yi haka, kuma abu mai daraja ne a idanunmu.
Af Herren er dette sket, det er underligt for vore Øjne.
24 Wannan ita ce ranar da Ubangiji ya yi; bari mu yi farin ciki mu kuma yi murna a cikinta.
Denne er Dagen, som Herren har beredt; lader os fryde og glæde os paa den!
25 Ya Ubangiji, ka cece mu; Ya Ubangiji, ka ba mu nasara.
Kære Herre! frels dog; kære Herre! lad det dog lykkes.
26 Mai albarka ne shi mai zuwa cikin sunan Ubangiji. Daga gidan Ubangiji muna sa muku albarka.
Velsignet være den, som kommer i Herrens Navn; vi velsigne eder fra Herrens Hus.
27 Ubangiji shi ne Allah ya kuma sa haskensa ya haskaka a kanmu. Da kwanoni a hannunmu, muka shiga jerin gwanon biki ku kai su ƙahoni na bagade.
Herren er Gud, og han lod lyse for os; binder Højtidsofferet med Reb, indtil det bringes til Alterets Horn.
28 Kai ne Allahna, zan kuwa yi maka godiya; kai ne Allahna, zan kuwa ɗaukaka ka.
Du er min Gud, og jeg vil takke dig; min Gud, jeg vil ophøje dig.
29 Ku gode wa Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.
Priser Herren; thi han er god; thi hans Miskundhed varer evindelig.