< Zabura 116 >

1 Ina ƙaunar Ubangiji, gama ya ji muryata; ya ji kukata ta neman jinƙai.
He entregado mi amor al Señor porque escuchó la voz de mi clamor y mi oración.
2 Domin ya juye kunnensa gare ni, zan kira gare shi muddin ina da rai.
Ha permitido que mi oración venga ante él, y le invocaré él todos mis días.
3 Igiyoyin mutuwa sun shaƙe ni, wahalar kabari sun zo a kaina; na cika da wahala da ɓacin rai. (Sheol h7585)
Las redes de la muerte me rodeaban, y los dolores del inframundo me tenían agarrado; Estaba lleno de problemas y tristezas. (Sheol h7585)
4 Sai na kira ga sunan Ubangiji na ce, “Ya Ubangiji, ka cece ni!”
Entonces oré al Señor, diciendo: Señor, saca mi alma de la angustia.
5 Ubangiji mai alheri ne da kuma mai adalci; Allahnmu yana cike da tausayi.
El Señor está lleno de gracia y justicia; Verdaderamente, él es un Dios de misericordia.
6 Ubangiji yana tsare masu tawali’u; sa’ad da nake cikin tsananin bukata, ya cece ni.
El Señor guarda a los humildes; Fui humillado, y él fue mi salvador.
7 Ka kwantar da hankali, ya raina, gama Ubangiji mai alheri ne a gare ka.
Vuelve a tu descanso, oh mi alma; porque el Señor te ha dado tu recompensa.
8 Gama kai, ya Ubangiji, ka ceci raina daga mutuwa, idanuna daga hawaye, ƙafafuna daga tuntuɓe,
Has quitado mi alma del poder de la muerte, para que mis ojos no lloren, y mis pies no caigan.
9 don in iya tafiya a gaban Ubangiji a ƙasar masu rai.
Iré delante de Jehová en la tierra de los vivientes.
10 Na gaskata, saboda haka na ce, “An azabtar da ni ƙwarai.”
Todavía tenía fe, aunque dije, estoy en un gran problema;
11 Kuma cikin rikicewana na ce, “Dukan mutane maƙaryata ne.”
Aunque dije en mi temor, Todos los hombres son falsos.
12 Yaya zan sāka wa Ubangiji saboda dukan alherinsa gare ni?
¿Qué le daré al Señor por todas las cosas buenas que él ha hecho por mí?
13 Zan daga kwaf na ceto in kuma kira ga sunan Ubangiji.
Tomaré la copa de la salvación y alabaré el nombre del Señor.
14 Zan cika alkawurana ga Ubangiji a gaban dukan mutanensa.
Haré la ofrenda de mi juramento a Jehová, aun delante de todo su pueblo.
15 Abu mai daraja a gaban Ubangiji shi ne mutuwar tsarkakansa.
Querido a los ojos del Señor es la muerte de sus santos.
16 Ya Ubangiji, da gaske ni bawanka ne; ni bawanka ne, ɗan baiwarka; ka’yantar da ni daga sarƙoƙi.
Oh Señor, verdaderamente yo soy tu siervo; Yo soy tu siervo, el hijo de tu sierva; por ti mis cuerdas han sido rotas.
17 Zan yi hadayar godiya gare ka in kuma kira bisa sunan Ubangiji.
Te daré una ofrenda de alabanza, y haré mi oración en el nombre del Señor.
18 Zan cika alkawurana ga Ubangiji a gaban dukan mutanensa,
Haré las ofrendas de mi juramento, aun delante de todo su pueblo;
19 a filayen gidan Ubangiji, a tsakiyarki, ya Urushalima. Yabi Ubangiji.
En la casa del Señor, incluso en Jerusalén. Alabado sea el Señor.

< Zabura 116 >