< Zabura 116 >

1 Ina ƙaunar Ubangiji, gama ya ji muryata; ya ji kukata ta neman jinƙai.
Amé a Jehová, porque ha oído mi voz: mis ruegos.
2 Domin ya juye kunnensa gare ni, zan kira gare shi muddin ina da rai.
Porque ha inclinado su oído a mí; y en mis días le llamaré,
3 Igiyoyin mutuwa sun shaƙe ni, wahalar kabari sun zo a kaina; na cika da wahala da ɓacin rai. (Sheol h7585)
Rodeáronme los dolores de la muerte, las angustias del sepulcro me hallaron: angustia y dolor había hallado: (Sheol h7585)
4 Sai na kira ga sunan Ubangiji na ce, “Ya Ubangiji, ka cece ni!”
Y llamé el nombre de Jehová: Escapa ahora mi alma, o! Jehová.
5 Ubangiji mai alheri ne da kuma mai adalci; Allahnmu yana cike da tausayi.
Clemente es Jehová y justo, y misericordioso nuestro Dios.
6 Ubangiji yana tsare masu tawali’u; sa’ad da nake cikin tsananin bukata, ya cece ni.
Guarda a los sencillos Jehová: yo estaba debilitado y salvóme.
7 Ka kwantar da hankali, ya raina, gama Ubangiji mai alheri ne a gare ka.
Vuelve, o! alma mía, a tu reposo; porque Jehová te ha hecho bien.
8 Gama kai, ya Ubangiji, ka ceci raina daga mutuwa, idanuna daga hawaye, ƙafafuna daga tuntuɓe,
Porque has librado mi alma de la muerte, mis ojos de las lágrimas, mis pies del rempujón.
9 don in iya tafiya a gaban Ubangiji a ƙasar masu rai.
Andaré delante de Jehová en las tierras de los vivos.
10 Na gaskata, saboda haka na ce, “An azabtar da ni ƙwarai.”
Creí, por tanto hablé: y fui afligido en gran manera.
11 Kuma cikin rikicewana na ce, “Dukan mutane maƙaryata ne.”
Y dije en mi apresuramiento: Todo hombre es mentiroso.
12 Yaya zan sāka wa Ubangiji saboda dukan alherinsa gare ni?
¿Qué pagaré a Jehová por todos sus beneficios sobre mí?
13 Zan daga kwaf na ceto in kuma kira ga sunan Ubangiji.
El vaso de saludes tomaré; e invocaré el nombre de Jehová.
14 Zan cika alkawurana ga Ubangiji a gaban dukan mutanensa.
Ahora pagaré mis votos a Jehová delante de todo su pueblo.
15 Abu mai daraja a gaban Ubangiji shi ne mutuwar tsarkakansa.
Estimada es en los ojos de Jehová la muerte de sus piadosos.
16 Ya Ubangiji, da gaske ni bawanka ne; ni bawanka ne, ɗan baiwarka; ka’yantar da ni daga sarƙoƙi.
Así es, o! Jehová; porque yo soy tu siervo, yo soy tu siervo, hijo de tu sierva, tú rompiste mis prisiones.
17 Zan yi hadayar godiya gare ka in kuma kira bisa sunan Ubangiji.
A ti sacrificaré sacrificio de alabanza; y el nombre de Jehová invocaré.
18 Zan cika alkawurana ga Ubangiji a gaban dukan mutanensa,
Ahora pagaré mis votos a Jehová delante de todo su pueblo;
19 a filayen gidan Ubangiji, a tsakiyarki, ya Urushalima. Yabi Ubangiji.
En los patios de la casa de Jehová; en medio de ti, o! Jerusalem. Alelu- Jah.

< Zabura 116 >