< Zabura 116 >
1 Ina ƙaunar Ubangiji, gama ya ji muryata; ya ji kukata ta neman jinƙai.
Eu amo Yahweh, porque ele ouve minha voz, e meus gritos de misericórdia.
2 Domin ya juye kunnensa gare ni, zan kira gare shi muddin ina da rai.
Porque ele virou seus ouvidos para mim, portanto, eu o convocarei enquanto eu viver.
3 Igiyoyin mutuwa sun shaƙe ni, wahalar kabari sun zo a kaina; na cika da wahala da ɓacin rai. (Sheol )
As cordas da morte me cercaram, as dores do Sheol se apoderaram de mim. Eu encontrei problemas e tristezas. (Sheol )
4 Sai na kira ga sunan Ubangiji na ce, “Ya Ubangiji, ka cece ni!”
Então eu invoquei o nome de Yahweh: “Yahweh, eu te imploro, entrega minha alma”.
5 Ubangiji mai alheri ne da kuma mai adalci; Allahnmu yana cike da tausayi.
Yahweh é gracioso e justo. Sim, nosso Deus é misericordioso.
6 Ubangiji yana tsare masu tawali’u; sa’ad da nake cikin tsananin bukata, ya cece ni.
Yahweh preserva o simples. Fui trazido para baixo, e ele me salvou.
7 Ka kwantar da hankali, ya raina, gama Ubangiji mai alheri ne a gare ka.
Volte para o seu descanso, minha alma, pois Yahweh tem lidado generosamente com você.
8 Gama kai, ya Ubangiji, ka ceci raina daga mutuwa, idanuna daga hawaye, ƙafafuna daga tuntuɓe,
Pois você entregou minha alma da morte, meus olhos das lágrimas, e meus pés de cair.
9 don in iya tafiya a gaban Ubangiji a ƙasar masu rai.
Eu caminharei diante de Yahweh na terra dos vivos.
10 Na gaskata, saboda haka na ce, “An azabtar da ni ƙwarai.”
Eu acreditava, portanto disse, “Eu estava muito aflito”.
11 Kuma cikin rikicewana na ce, “Dukan mutane maƙaryata ne.”
Eu disse na minha pressa, “Todas as pessoas são mentirosas”.
12 Yaya zan sāka wa Ubangiji saboda dukan alherinsa gare ni?
O que darei a Iavé por todos os benefícios que ele tem para comigo?
13 Zan daga kwaf na ceto in kuma kira ga sunan Ubangiji.
Vou pegar a taça da salvação e invocarei o nome de Yahweh.
14 Zan cika alkawurana ga Ubangiji a gaban dukan mutanensa.
Pagarei meus votos a Javé, sim, na presença de todo o seu povo.
15 Abu mai daraja a gaban Ubangiji shi ne mutuwar tsarkakansa.
Preciosa aos olhos de Yahweh é a morte de seus santos.
16 Ya Ubangiji, da gaske ni bawanka ne; ni bawanka ne, ɗan baiwarka; ka’yantar da ni daga sarƙoƙi.
Yahweh, verdadeiramente eu sou seu servo. Eu sou seu criado, o filho de sua criada. Vocês me libertaram de minhas correntes.
17 Zan yi hadayar godiya gare ka in kuma kira bisa sunan Ubangiji.
Vou oferecer a vocês o sacrifício de ação de graças, e invocará o nome de Yahweh.
18 Zan cika alkawurana ga Ubangiji a gaban dukan mutanensa,
Pagarei meus votos a Javé, sim, na presença de todo o seu povo,
19 a filayen gidan Ubangiji, a tsakiyarki, ya Urushalima. Yabi Ubangiji.
nos tribunais da casa de Yahweh, no meio de você, Jerusalém. Louvado seja Yah!