< Zabura 116 >

1 Ina ƙaunar Ubangiji, gama ya ji muryata; ya ji kukata ta neman jinƙai.
alleluia dilexi quoniam exaudiet Dominus vocem orationis meae
2 Domin ya juye kunnensa gare ni, zan kira gare shi muddin ina da rai.
quia inclinavit aurem suam mihi et in diebus meis invocabo te
3 Igiyoyin mutuwa sun shaƙe ni, wahalar kabari sun zo a kaina; na cika da wahala da ɓacin rai. (Sheol h7585)
circumdederunt me dolores mortis pericula inferni invenerunt me tribulationem et dolorem inveni (Sheol h7585)
4 Sai na kira ga sunan Ubangiji na ce, “Ya Ubangiji, ka cece ni!”
et nomen Domini invocavi o Domine libera animam meam
5 Ubangiji mai alheri ne da kuma mai adalci; Allahnmu yana cike da tausayi.
misericors Dominus et iustus et Deus noster miseretur
6 Ubangiji yana tsare masu tawali’u; sa’ad da nake cikin tsananin bukata, ya cece ni.
custodiens parvulos Dominus humiliatus sum et liberavit me
7 Ka kwantar da hankali, ya raina, gama Ubangiji mai alheri ne a gare ka.
convertere anima mea in requiem tuam quia Dominus benefecit tibi
8 Gama kai, ya Ubangiji, ka ceci raina daga mutuwa, idanuna daga hawaye, ƙafafuna daga tuntuɓe,
quia eripuit animam meam de morte oculos meos a lacrimis pedes meos a lapsu
9 don in iya tafiya a gaban Ubangiji a ƙasar masu rai.
placebo Domino in regione vivorum
10 Na gaskata, saboda haka na ce, “An azabtar da ni ƙwarai.”
alleluia credidi propter quod locutus sum ego autem humiliatus sum nimis
11 Kuma cikin rikicewana na ce, “Dukan mutane maƙaryata ne.”
ego dixi in excessu meo omnis homo mendax
12 Yaya zan sāka wa Ubangiji saboda dukan alherinsa gare ni?
quid retribuam Domino pro omnibus quae retribuit mihi
13 Zan daga kwaf na ceto in kuma kira ga sunan Ubangiji.
calicem salutaris accipiam et nomen Domini invocabo
14 Zan cika alkawurana ga Ubangiji a gaban dukan mutanensa.
vota mea Domino reddam coram omni populo eius
15 Abu mai daraja a gaban Ubangiji shi ne mutuwar tsarkakansa.
pretiosa in conspectu Domini mors sanctorum eius
16 Ya Ubangiji, da gaske ni bawanka ne; ni bawanka ne, ɗan baiwarka; ka’yantar da ni daga sarƙoƙi.
o Domine quia ego servus tuus ego servus tuus et filius ancillae tuae disrupisti vincula mea
17 Zan yi hadayar godiya gare ka in kuma kira bisa sunan Ubangiji.
tibi sacrificabo hostiam laudis et in nomine Domini invocabo
18 Zan cika alkawurana ga Ubangiji a gaban dukan mutanensa,
vota mea Domino reddam in conspectu omnis populi eius
19 a filayen gidan Ubangiji, a tsakiyarki, ya Urushalima. Yabi Ubangiji.
in atriis domus Domini in medio tui Hierusalem

< Zabura 116 >