< Zabura 116 >

1 Ina ƙaunar Ubangiji, gama ya ji muryata; ya ji kukata ta neman jinƙai.
Alleluja. [Dilexi, quoniam exaudiet Dominus vocem orationis meæ.
2 Domin ya juye kunnensa gare ni, zan kira gare shi muddin ina da rai.
Quia inclinavit aurem suam mihi, et in diebus meis invocabo.
3 Igiyoyin mutuwa sun shaƙe ni, wahalar kabari sun zo a kaina; na cika da wahala da ɓacin rai. (Sheol h7585)
Circumdederunt me dolores mortis; et pericula inferni invenerunt me. Tribulationem et dolorem inveni, (Sheol h7585)
4 Sai na kira ga sunan Ubangiji na ce, “Ya Ubangiji, ka cece ni!”
et nomen Domini invocavi: o Domine, libera animam meam.
5 Ubangiji mai alheri ne da kuma mai adalci; Allahnmu yana cike da tausayi.
Misericors Dominus et justus, et Deus noster miseretur.
6 Ubangiji yana tsare masu tawali’u; sa’ad da nake cikin tsananin bukata, ya cece ni.
Custodiens parvulos Dominus; humiliatus sum, et liberavit me.
7 Ka kwantar da hankali, ya raina, gama Ubangiji mai alheri ne a gare ka.
Convertere, anima mea, in requiem tuam, quia Dominus benefecit tibi:
8 Gama kai, ya Ubangiji, ka ceci raina daga mutuwa, idanuna daga hawaye, ƙafafuna daga tuntuɓe,
quia eripuit animam meam de morte, oculos meos a lacrimis, pedes meos a lapsu.
9 don in iya tafiya a gaban Ubangiji a ƙasar masu rai.
Placebo Domino in regione vivorum.]
10 Na gaskata, saboda haka na ce, “An azabtar da ni ƙwarai.”
Alleluja. [Credidi, propter quod locutus sum; ego autem humiliatus sum nimis.
11 Kuma cikin rikicewana na ce, “Dukan mutane maƙaryata ne.”
Ego dixi in excessu meo: Omnis homo mendax.
12 Yaya zan sāka wa Ubangiji saboda dukan alherinsa gare ni?
Quid retribuam Domino pro omnibus quæ retribuit mihi?
13 Zan daga kwaf na ceto in kuma kira ga sunan Ubangiji.
Calicem salutaris accipiam, et nomen Domini invocabo.
14 Zan cika alkawurana ga Ubangiji a gaban dukan mutanensa.
Vota mea Domino reddam coram omni populo ejus.
15 Abu mai daraja a gaban Ubangiji shi ne mutuwar tsarkakansa.
Pretiosa in conspectu Domini mors sanctorum ejus.
16 Ya Ubangiji, da gaske ni bawanka ne; ni bawanka ne, ɗan baiwarka; ka’yantar da ni daga sarƙoƙi.
O Domine, quia ego servus tuus; ego servus tuus, et filius ancillæ tuæ. Dirupisti vincula mea:
17 Zan yi hadayar godiya gare ka in kuma kira bisa sunan Ubangiji.
tibi sacrificabo hostiam laudis, et nomen Domini invocabo.
18 Zan cika alkawurana ga Ubangiji a gaban dukan mutanensa,
Vota mea Domino reddam in conspectu omnis populi ejus;
19 a filayen gidan Ubangiji, a tsakiyarki, ya Urushalima. Yabi Ubangiji.
in atriis domus Domini, in medio tui, Jerusalem.]

< Zabura 116 >