< Zabura 116 >

1 Ina ƙaunar Ubangiji, gama ya ji muryata; ya ji kukata ta neman jinƙai.
Das ist mir lieb, daß der HERR meine Stimme und mein Flehen hört.
2 Domin ya juye kunnensa gare ni, zan kira gare shi muddin ina da rai.
Denn er neigte sein Ohr zu mir; darum will ich mein Leben lang ihn anrufen.
3 Igiyoyin mutuwa sun shaƙe ni, wahalar kabari sun zo a kaina; na cika da wahala da ɓacin rai. (Sheol h7585)
Stricke des Todes hatten mich umfangen, und Ängste der Hölle hatten mich getroffen; ich kam in Jammer und Not. (Sheol h7585)
4 Sai na kira ga sunan Ubangiji na ce, “Ya Ubangiji, ka cece ni!”
Aber ich rief an den Namen des HERRN: O HERR, errette mein Seele!
5 Ubangiji mai alheri ne da kuma mai adalci; Allahnmu yana cike da tausayi.
Der HERR ist gnädig und gerecht, und unser Gott ist barmherzig.
6 Ubangiji yana tsare masu tawali’u; sa’ad da nake cikin tsananin bukata, ya cece ni.
Der HERR behütet die Einfältigen; wenn ich unterliege, so hilft er mir.
7 Ka kwantar da hankali, ya raina, gama Ubangiji mai alheri ne a gare ka.
Sei nun wieder zufrieden, meine Seele; denn der HERR tut dir Gutes.
8 Gama kai, ya Ubangiji, ka ceci raina daga mutuwa, idanuna daga hawaye, ƙafafuna daga tuntuɓe,
Denn du hast meine Seele aus dem Tode gerissen, meine Augen von den Tränen, meinen Fuß vom Gleiten.
9 don in iya tafiya a gaban Ubangiji a ƙasar masu rai.
Ich werde wandeln vor dem HERRN im Lande der Lebendigen.
10 Na gaskata, saboda haka na ce, “An azabtar da ni ƙwarai.”
Ich glaube, darum rede ich; ich werde aber sehr geplagt.
11 Kuma cikin rikicewana na ce, “Dukan mutane maƙaryata ne.”
Ich sprach in meinem Zagen: Alle Menschen sind Lügner.
12 Yaya zan sāka wa Ubangiji saboda dukan alherinsa gare ni?
Wie soll ich dem HERRN vergelten alle seine Wohltat, die er an mir tut?
13 Zan daga kwaf na ceto in kuma kira ga sunan Ubangiji.
Ich will den Kelch des Heils nehmen und des HERRN Namen predigen.
14 Zan cika alkawurana ga Ubangiji a gaban dukan mutanensa.
Ich will mein Gelübde dem HERRN bezahlen vor allem seinem Volk.
15 Abu mai daraja a gaban Ubangiji shi ne mutuwar tsarkakansa.
Der Tod seiner Heiligen ist wertgehalten vor dem HERRN.
16 Ya Ubangiji, da gaske ni bawanka ne; ni bawanka ne, ɗan baiwarka; ka’yantar da ni daga sarƙoƙi.
O HERR, ich bin dein Knecht; ich bin dein Knecht, deiner Magd Sohn. Du hast meine Bande zerrissen.
17 Zan yi hadayar godiya gare ka in kuma kira bisa sunan Ubangiji.
Dir will ich Dank opfern und des HERRN Namen predigen.
18 Zan cika alkawurana ga Ubangiji a gaban dukan mutanensa,
Ich will meine Gelübde dem HERRN bezahlen vor allem seinem Volk,
19 a filayen gidan Ubangiji, a tsakiyarki, ya Urushalima. Yabi Ubangiji.
in den Höfen am Hause des HERRN, in dir Jerusalem. Halleluja!

< Zabura 116 >