< Zabura 116 >
1 Ina ƙaunar Ubangiji, gama ya ji muryata; ya ji kukata ta neman jinƙai.
Ich liebe Jehova; denn er hörte meine Stimme, mein Flehen;
2 Domin ya juye kunnensa gare ni, zan kira gare shi muddin ina da rai.
denn er hat zu mir geneigt sein Ohr; und ich will ihn anrufen in allen meinen Tagen.
3 Igiyoyin mutuwa sun shaƙe ni, wahalar kabari sun zo a kaina; na cika da wahala da ɓacin rai. (Sheol )
Es umfingen mich die Bande des Todes, und die Bedrängnisse des Scheols erreichten mich; ich fand Drangsal und Kummer. (Sheol )
4 Sai na kira ga sunan Ubangiji na ce, “Ya Ubangiji, ka cece ni!”
Und ich rief an den Namen Jehovas: Bitte, Jehova, errette meine Seele!
5 Ubangiji mai alheri ne da kuma mai adalci; Allahnmu yana cike da tausayi.
Gnädig ist Jehova und gerecht, und unser Gott ist barmherzig.
6 Ubangiji yana tsare masu tawali’u; sa’ad da nake cikin tsananin bukata, ya cece ni.
Jehova bewahrt die Einfältigen; ich war elend, und er hat mich gerettet.
7 Ka kwantar da hankali, ya raina, gama Ubangiji mai alheri ne a gare ka.
Kehre wieder, meine Seele, zu deiner Ruhe! Denn Jehova hat wohlgetan an dir.
8 Gama kai, ya Ubangiji, ka ceci raina daga mutuwa, idanuna daga hawaye, ƙafafuna daga tuntuɓe,
Denn du hast meine Seele errettet vom Tode, meine Augen von Tränen, meinen Fuß vom Sturz.
9 don in iya tafiya a gaban Ubangiji a ƙasar masu rai.
Ich werde wandeln vor Jehova in dem Lande der Lebendigen.
10 Na gaskata, saboda haka na ce, “An azabtar da ni ƙwarai.”
Ich glaubte, darum redete ich. Ich bin sehr gebeugt gewesen.
11 Kuma cikin rikicewana na ce, “Dukan mutane maƙaryata ne.”
Ich sprach in meiner Bestürzung: Alle Menschen sind Lügner!
12 Yaya zan sāka wa Ubangiji saboda dukan alherinsa gare ni?
Wie soll ich Jehova alle seine Wohltaten an mir vergelten?
13 Zan daga kwaf na ceto in kuma kira ga sunan Ubangiji.
Den Becher der Rettungen will ich nehmen und anrufen den Namen Jehovas.
14 Zan cika alkawurana ga Ubangiji a gaban dukan mutanensa.
Ich will Jehova meine Gelübde bezahlen, ja, in der Gegenwart seines ganzen Volkes.
15 Abu mai daraja a gaban Ubangiji shi ne mutuwar tsarkakansa.
Kostbar ist in den Augen Jehovas der Tod seiner Frommen.
16 Ya Ubangiji, da gaske ni bawanka ne; ni bawanka ne, ɗan baiwarka; ka’yantar da ni daga sarƙoƙi.
Bitte, Jehova! Denn ich bin dein Knecht; ich bin dein Knecht, der Sohn deiner Magd; gelöst hast du meine Bande.
17 Zan yi hadayar godiya gare ka in kuma kira bisa sunan Ubangiji.
Dir will ich Opfer des Lobes opfern, und anrufen den Namen Jehovas.
18 Zan cika alkawurana ga Ubangiji a gaban dukan mutanensa,
Ich will Jehova meine Gelübde bezahlen, ja, in der Gegenwart seines ganzen Volkes.
19 a filayen gidan Ubangiji, a tsakiyarki, ya Urushalima. Yabi Ubangiji.
In den Vorhöfen des Hauses Jehovas, in deiner Mitte, Jerusalem. Lobet Jehova!