< Zabura 116 >

1 Ina ƙaunar Ubangiji, gama ya ji muryata; ya ji kukata ta neman jinƙai.
Jahwe hab ich lieb, / Denn er hat meine Stimme, mein Flehn erhört.
2 Domin ya juye kunnensa gare ni, zan kira gare shi muddin ina da rai.
Ja, er hat mir sein Ohr zugeneigt; / Drum werd ich ihn auch, solang ich lebe, anrufen.
3 Igiyoyin mutuwa sun shaƙe ni, wahalar kabari sun zo a kaina; na cika da wahala da ɓacin rai. (Sheol h7585)
Mich hatten des Todes Bande umringt, / Ich fürchtete schon, ins Grab zu sinken, / Angst und Kummer erfuhr ich. (Sheol h7585)
4 Sai na kira ga sunan Ubangiji na ce, “Ya Ubangiji, ka cece ni!”
Da rief ich Jahwes Namen an: / "Ach, Jahwe, rette mein Leben!"
5 Ubangiji mai alheri ne da kuma mai adalci; Allahnmu yana cike da tausayi.
Jahwe war auch gnädig und treu, / Und es erbarmte sich unser Gott.
6 Ubangiji yana tsare masu tawali’u; sa’ad da nake cikin tsananin bukata, ya cece ni.
Schutzlose behütet Jahwe: / Drum half er mir auch, als ich elend war.
7 Ka kwantar da hankali, ya raina, gama Ubangiji mai alheri ne a gare ka.
"Kehr nun ein, meine Seele, in deine Ruh, / Denn Jahwe hat dir wohlgetan!"
8 Gama kai, ya Ubangiji, ka ceci raina daga mutuwa, idanuna daga hawaye, ƙafafuna daga tuntuɓe,
Ja, du hast meine Seele dem Tode entrissen, / Meinen Augen die Tränen getrocknet, / Meinen Fuß vor Gleiten bewahrt.
9 don in iya tafiya a gaban Ubangiji a ƙasar masu rai.
So darf ich vor Jahwe noch wandeln / In der Lebendigen Landen.
10 Na gaskata, saboda haka na ce, “An azabtar da ni ƙwarai.”
Ich sprach die Wahrheit, als ich sagte: / "Ich bin sehr niedergedrückt."
11 Kuma cikin rikicewana na ce, “Dukan mutane maƙaryata ne.”
Ich habe sogar in meiner Angst gesagt: / "Alle Menschen sind Lügner."
12 Yaya zan sāka wa Ubangiji saboda dukan alherinsa gare ni?
Wie soll ich nun aber Jahwe vergelten / All seine Wohltaten, die ich erfahren?
13 Zan daga kwaf na ceto in kuma kira ga sunan Ubangiji.
Den Becher des Heils werd ich erheben / Und Jahwes Namen anrufen.
14 Zan cika alkawurana ga Ubangiji a gaban dukan mutanensa.
Meine Gelübde werd ich Jahwe erfüllen / Frei und offen vor all seinem Volk.
15 Abu mai daraja a gaban Ubangiji shi ne mutuwar tsarkakansa.
Selten nur läßt Jahwe / Seine Frommen (frühzeitig) sterben.
16 Ya Ubangiji, da gaske ni bawanka ne; ni bawanka ne, ɗan baiwarka; ka’yantar da ni daga sarƙoƙi.
Ach Jahwe, (erhalte darum mein Leben auch ferner)! / Ich bin ja dein Knecht. / Ich bin dein Knecht, der Sohn deiner Magd. / Du hat meine Fesseln gelöst.
17 Zan yi hadayar godiya gare ka in kuma kira bisa sunan Ubangiji.
Dir will ich Dankopfer bringen / Und Jahwes Namen anrufen.
18 Zan cika alkawurana ga Ubangiji a gaban dukan mutanensa,
Meine Gelübde will ich Jahwe erfüllen / Frei und offen vor all seinem Volk.
19 a filayen gidan Ubangiji, a tsakiyarki, ya Urushalima. Yabi Ubangiji.
In den Vorhöfen des Hauses Jahwes, / In der Mitte, Jerusalem! / Lobt Jah!

< Zabura 116 >