< Zabura 116 >

1 Ina ƙaunar Ubangiji, gama ya ji muryata; ya ji kukata ta neman jinƙai.
J'aime l'Eternel, car il a exaucé ma voix, [et] mes supplications.
2 Domin ya juye kunnensa gare ni, zan kira gare shi muddin ina da rai.
Car il a incliné son oreille vers moi, c'est pourquoi je l'invoquerai durant mes jours.
3 Igiyoyin mutuwa sun shaƙe ni, wahalar kabari sun zo a kaina; na cika da wahala da ɓacin rai. (Sheol h7585)
Les cordeaux de la mort m'avaient environné, et les détresses du sépulcre m'avaient rencontré; j'avais rencontré la détresse et l'ennui. (Sheol h7585)
4 Sai na kira ga sunan Ubangiji na ce, “Ya Ubangiji, ka cece ni!”
Mais j'invoquai le Nom de l’Eternel, [en disant]: je te prie, ô Eternel! délivre mon âme.
5 Ubangiji mai alheri ne da kuma mai adalci; Allahnmu yana cike da tausayi.
L'Eternel est pitoyable et juste, et notre Dieu fait miséricorde.
6 Ubangiji yana tsare masu tawali’u; sa’ad da nake cikin tsananin bukata, ya cece ni.
L'Eternel garde les simples; j'étais devenu misérable, et il m'a sauvé.
7 Ka kwantar da hankali, ya raina, gama Ubangiji mai alheri ne a gare ka.
Mon âme, retourne en ton repos; car l'Eternel t'a fait du bien.
8 Gama kai, ya Ubangiji, ka ceci raina daga mutuwa, idanuna daga hawaye, ƙafafuna daga tuntuɓe,
Parce que tu as mis à couvert mon âme de la mort, mes yeux de pleurs, [et] mes pieds de chute.
9 don in iya tafiya a gaban Ubangiji a ƙasar masu rai.
Je marcherai en la présence de l'Eternel dans la terre des vivants.
10 Na gaskata, saboda haka na ce, “An azabtar da ni ƙwarai.”
J'ai cru, c'est pourquoi j'ai parlé; j'ai été fort affligé.
11 Kuma cikin rikicewana na ce, “Dukan mutane maƙaryata ne.”
Je disais en ma précipitation: tout homme est menteur.
12 Yaya zan sāka wa Ubangiji saboda dukan alherinsa gare ni?
Que rendrai-je à l'Eternel? tous ses bienfaits sont sur moi.
13 Zan daga kwaf na ceto in kuma kira ga sunan Ubangiji.
Je prendrai la coupe des délivrances, et j'invoquerai le Nom de l’Eternel.
14 Zan cika alkawurana ga Ubangiji a gaban dukan mutanensa.
Je rendrai maintenant mes vœux à l'Eternel, devant tout son peuple.
15 Abu mai daraja a gaban Ubangiji shi ne mutuwar tsarkakansa.
[Toute sorte] de mort des bien-aimés de l'Eternel est précieuse devant ses yeux.
16 Ya Ubangiji, da gaske ni bawanka ne; ni bawanka ne, ɗan baiwarka; ka’yantar da ni daga sarƙoƙi.
Ouï, ô Eternel! car je suis ton serviteur, je suis ton serviteur, fils de ta servante, tu as délié mes liens.
17 Zan yi hadayar godiya gare ka in kuma kira bisa sunan Ubangiji.
Je te sacrifierai des sacrifices d'actions de grâces, et j'invoquerai le Nom de l’Eternel.
18 Zan cika alkawurana ga Ubangiji a gaban dukan mutanensa,
Je rendrai maintenant mes vœux à l'Eternel, devant tout son peuple;
19 a filayen gidan Ubangiji, a tsakiyarki, ya Urushalima. Yabi Ubangiji.
Dans les parvis de la maison de l'Eternel, au milieu de toi, Jérusalem. Louez l'Eternel.

< Zabura 116 >