< Zabura 116 >

1 Ina ƙaunar Ubangiji, gama ya ji muryata; ya ji kukata ta neman jinƙai.
J’Aime que l’Eternel écoute ma voix, mes supplications,
2 Domin ya juye kunnensa gare ni, zan kira gare shi muddin ina da rai.
qu’il incline son oreille vers moi, alors que je l’invoque chaque jour de ma vie.
3 Igiyoyin mutuwa sun shaƙe ni, wahalar kabari sun zo a kaina; na cika da wahala da ɓacin rai. (Sheol h7585)
Les liens de la mort m’avaient enveloppé, les angoisses du Cheol m’avaient étreint; j’avais éprouvé détresse et douleurs. (Sheol h7585)
4 Sai na kira ga sunan Ubangiji na ce, “Ya Ubangiji, ka cece ni!”
Mais j’ai invoqué le nom du Seigneur: "Ah! de grâce, Seigneur, sauve mon âme!"
5 Ubangiji mai alheri ne da kuma mai adalci; Allahnmu yana cike da tausayi.
Clément est l’Eternel et juste, notre Dieu est compatissant.
6 Ubangiji yana tsare masu tawali’u; sa’ad da nake cikin tsananin bukata, ya cece ni.
L’Eternel protège les simples; j’étais abaissé, et il m’a porté secours.
7 Ka kwantar da hankali, ya raina, gama Ubangiji mai alheri ne a gare ka.
Reviens, ô mon âme, à ta quiétude, car l’Eternel te comble de ses bienfaits.
8 Gama kai, ya Ubangiji, ka ceci raina daga mutuwa, idanuna daga hawaye, ƙafafuna daga tuntuɓe,
Oui, tu as préservé mon âme de la mort, mes yeux des larmes, mes pieds de la chute.
9 don in iya tafiya a gaban Ubangiji a ƙasar masu rai.
Je circulerai devant le Seigneur, dans les terres des vivants.
10 Na gaskata, saboda haka na ce, “An azabtar da ni ƙwarai.”
Je suis plein de foi quand je parle, si humilié que je puisse être.
11 Kuma cikin rikicewana na ce, “Dukan mutane maƙaryata ne.”
Pourtant j’avais dit dans ma précipitation: "Tout dans l’homme est trompeur!"
12 Yaya zan sāka wa Ubangiji saboda dukan alherinsa gare ni?
Que ferai-je pour l’Eternel en retour de toutes ses bontés pour moi?
13 Zan daga kwaf na ceto in kuma kira ga sunan Ubangiji.
Je lèverai la coupe du salut, et proclamerai le nom de l’Eternel.
14 Zan cika alkawurana ga Ubangiji a gaban dukan mutanensa.
Mes vœux, je les acquitterai envers l’Eternel, à la face de tout son peuple.
15 Abu mai daraja a gaban Ubangiji shi ne mutuwar tsarkakansa.
Une chose précieuse aux regards de l’Eternel, c’est la mort de ses pieux serviteurs.
16 Ya Ubangiji, da gaske ni bawanka ne; ni bawanka ne, ɗan baiwarka; ka’yantar da ni daga sarƙoƙi.
Oh! grâce, Seigneur, car je suis ton serviteur, je suis ton serviteur, fils de ta servante: puisses-tu dénouer mes liens!
17 Zan yi hadayar godiya gare ka in kuma kira bisa sunan Ubangiji.
A toi, j’offrirai un sacrifice de reconnaissance, et je proclamerai le nom du Seigneur.
18 Zan cika alkawurana ga Ubangiji a gaban dukan mutanensa,
Mes vœux, je les acquitterai envers l’Eternel, à la face de tout son peuple,
19 a filayen gidan Ubangiji, a tsakiyarki, ya Urushalima. Yabi Ubangiji.
dans les parvis de la maison de l’Eternel, dans ton enceinte, ô Jérusalem. Alléluia!

< Zabura 116 >