< Zabura 116 >

1 Ina ƙaunar Ubangiji, gama ya ji muryata; ya ji kukata ta neman jinƙai.
J’ai aimé l’Éternel, car il a entendu ma voix, mes supplications;
2 Domin ya juye kunnensa gare ni, zan kira gare shi muddin ina da rai.
Car il a incliné son oreille vers moi, et je l’invoquerai durant mes jours.
3 Igiyoyin mutuwa sun shaƙe ni, wahalar kabari sun zo a kaina; na cika da wahala da ɓacin rai. (Sheol h7585)
Les cordeaux de la mort m’avaient environné, et les détresses du shéol m’avaient atteint; j’avais trouvé la détresse et le chagrin; (Sheol h7585)
4 Sai na kira ga sunan Ubangiji na ce, “Ya Ubangiji, ka cece ni!”
Mais j’invoquai le nom de l’Éternel: Je te prie, ô Éternel! délivre mon âme.
5 Ubangiji mai alheri ne da kuma mai adalci; Allahnmu yana cike da tausayi.
L’Éternel est plein de grâce et juste, et notre Dieu est miséricordieux.
6 Ubangiji yana tsare masu tawali’u; sa’ad da nake cikin tsananin bukata, ya cece ni.
L’Éternel garde les simples; j’étais devenu misérable, et il m’a sauvé.
7 Ka kwantar da hankali, ya raina, gama Ubangiji mai alheri ne a gare ka.
Mon âme, retourne en ton repos, car l’Éternel t’a fait du bien.
8 Gama kai, ya Ubangiji, ka ceci raina daga mutuwa, idanuna daga hawaye, ƙafafuna daga tuntuɓe,
Car tu as délivré mon âme de la mort, mes yeux de larmes, mes pieds de chute:
9 don in iya tafiya a gaban Ubangiji a ƙasar masu rai.
Je marcherai devant l’Éternel dans la terre des vivants.
10 Na gaskata, saboda haka na ce, “An azabtar da ni ƙwarai.”
J’ai cru, c’est pourquoi j’ai parlé. J’ai été fort affligé.
11 Kuma cikin rikicewana na ce, “Dukan mutane maƙaryata ne.”
Je disais en mon agitation: Tout homme est menteur.
12 Yaya zan sāka wa Ubangiji saboda dukan alherinsa gare ni?
Que rendrai-je à l’Éternel pour tous les biens qu’il m’a faits?
13 Zan daga kwaf na ceto in kuma kira ga sunan Ubangiji.
Je prendrai la coupe du salut, et j’invoquerai le nom de l’Éternel.
14 Zan cika alkawurana ga Ubangiji a gaban dukan mutanensa.
J’acquitterai mes vœux envers l’Éternel, – oui, devant tout son peuple.
15 Abu mai daraja a gaban Ubangiji shi ne mutuwar tsarkakansa.
Précieuse, aux yeux de l’Éternel, est la mort de ses saints.
16 Ya Ubangiji, da gaske ni bawanka ne; ni bawanka ne, ɗan baiwarka; ka’yantar da ni daga sarƙoƙi.
Je te prie, ô Éternel! car je suis ton serviteur; je suis ton serviteur, le fils de ta servante; tu as délié mes liens.
17 Zan yi hadayar godiya gare ka in kuma kira bisa sunan Ubangiji.
Je te sacrifierai des sacrifices d’actions de grâces, et j’invoquerai le nom de l’Éternel.
18 Zan cika alkawurana ga Ubangiji a gaban dukan mutanensa,
J’acquitterai mes vœux envers l’Éternel, – oui, devant tout son peuple,
19 a filayen gidan Ubangiji, a tsakiyarki, ya Urushalima. Yabi Ubangiji.
Dans les parvis de la maison de l’Éternel, au milieu de toi, Jérusalem. Louez Jah!

< Zabura 116 >