< Zabura 116 >

1 Ina ƙaunar Ubangiji, gama ya ji muryata; ya ji kukata ta neman jinƙai.
Je l’aime, car Yahweh entend ma voix, mes supplications.
2 Domin ya juye kunnensa gare ni, zan kira gare shi muddin ina da rai.
Car il a incliné vers moi son oreille, et toute ma vie, je l’invoquerai.
3 Igiyoyin mutuwa sun shaƙe ni, wahalar kabari sun zo a kaina; na cika da wahala da ɓacin rai. (Sheol h7585)
Les liens de la mort m’entouraient, et les angoisses du schéol m’avaient saisi; j’étais en proie à la détresse et à l’affliction. (Sheol h7585)
4 Sai na kira ga sunan Ubangiji na ce, “Ya Ubangiji, ka cece ni!”
Et j’ai invoqué le nom de Yahweh: « Yahweh, sauve mon âme! »
5 Ubangiji mai alheri ne da kuma mai adalci; Allahnmu yana cike da tausayi.
Yahweh est miséricordieux et juste, notre Dieu est compatissant.
6 Ubangiji yana tsare masu tawali’u; sa’ad da nake cikin tsananin bukata, ya cece ni.
Yahweh garde les faibles; j’étais malheureux, et il m’a sauvé.
7 Ka kwantar da hankali, ya raina, gama Ubangiji mai alheri ne a gare ka.
Mon âme, retourne à ton repos; car Yahweh te comble de biens.
8 Gama kai, ya Ubangiji, ka ceci raina daga mutuwa, idanuna daga hawaye, ƙafafuna daga tuntuɓe,
Oui, tu as sauvé mon âme de la mort, mon œil des larmes, mes pieds de la chute.
9 don in iya tafiya a gaban Ubangiji a ƙasar masu rai.
Je marcherai encore devant Yahweh, dans la terre des vivants.
10 Na gaskata, saboda haka na ce, “An azabtar da ni ƙwarai.”
J’ai confiance, alors même que je dis: « je suis malheureux à l’excès. »
11 Kuma cikin rikicewana na ce, “Dukan mutane maƙaryata ne.”
Je disais dans mon abattement: « Tout homme est menteur. »
12 Yaya zan sāka wa Ubangiji saboda dukan alherinsa gare ni?
Que rendrai-je à Yahweh pour tous ses bienfaits à mon égard!
13 Zan daga kwaf na ceto in kuma kira ga sunan Ubangiji.
J’élèverai la coupe du salut, et j’invoquerai le nom de Yahweh.
14 Zan cika alkawurana ga Ubangiji a gaban dukan mutanensa.
J’accomplirai mes vœux envers Yahweh en présence de tout son peuple.
15 Abu mai daraja a gaban Ubangiji shi ne mutuwar tsarkakansa.
Elle a du prix aux yeux de Yahweh, la mort de ses fidèles.
16 Ya Ubangiji, da gaske ni bawanka ne; ni bawanka ne, ɗan baiwarka; ka’yantar da ni daga sarƙoƙi.
Ah! Yahweh, parce que je suis ton serviteur, ton serviteur, fils de ta servante, tu as détaché mes liens.
17 Zan yi hadayar godiya gare ka in kuma kira bisa sunan Ubangiji.
Je t’offrirai un sacrifice d’actions de grâces, et j’invoquerai le nom de Yahweh.
18 Zan cika alkawurana ga Ubangiji a gaban dukan mutanensa,
J’accomplirai mes vœux envers Yahweh, en présence de tout son peuple,
19 a filayen gidan Ubangiji, a tsakiyarki, ya Urushalima. Yabi Ubangiji.
dans les parvis de la maison de Yahweh, dans ton enceinte, Jérusalem. Alleluia!

< Zabura 116 >