< Zabura 116 >
1 Ina ƙaunar Ubangiji, gama ya ji muryata; ya ji kukata ta neman jinƙai.
I love for he has heard - Yahweh voice my supplications my.
2 Domin ya juye kunnensa gare ni, zan kira gare shi muddin ina da rai.
For he has inclined ear his to me and in days my I will call out.
3 Igiyoyin mutuwa sun shaƙe ni, wahalar kabari sun zo a kaina; na cika da wahala da ɓacin rai. (Sheol )
They surrounded me - [the] cords of death and [the] distresses of Sheol they found me trouble and sorrow I found. (Sheol )
4 Sai na kira ga sunan Ubangiji na ce, “Ya Ubangiji, ka cece ni!”
And on [the] name of Yahweh I called I beg you O Yahweh deliver! life my.
5 Ubangiji mai alheri ne da kuma mai adalci; Allahnmu yana cike da tausayi.
[is] gracious Yahweh and righteous and God our [is] compassionate.
6 Ubangiji yana tsare masu tawali’u; sa’ad da nake cikin tsananin bukata, ya cece ni.
[is] protecting Simple people Yahweh I had become low and me he saved.
7 Ka kwantar da hankali, ya raina, gama Ubangiji mai alheri ne a gare ka.
Return O self my to resting place your for Yahweh he has dealt bountifully towards you.
8 Gama kai, ya Ubangiji, ka ceci raina daga mutuwa, idanuna daga hawaye, ƙafafuna daga tuntuɓe,
For you have rescued life my from death eye my from tear[s] foot my from stumbling.
9 don in iya tafiya a gaban Ubangiji a ƙasar masu rai.
I will walk about before Yahweh in [the] lands of the living.
10 Na gaskata, saboda haka na ce, “An azabtar da ni ƙwarai.”
I believed for I said I I am afflicted exceedingly.
11 Kuma cikin rikicewana na ce, “Dukan mutane maƙaryata ne.”
I I said when was hastening I every person [is] a liar.
12 Yaya zan sāka wa Ubangiji saboda dukan alherinsa gare ni?
What? will I give back to Yahweh all benefits his towards me.
13 Zan daga kwaf na ceto in kuma kira ga sunan Ubangiji.
A cup of salvation I will lift up and on [the] name of Yahweh I will call.
14 Zan cika alkawurana ga Ubangiji a gaban dukan mutanensa.
Vows my to Yahweh I will pay before please all people his.
15 Abu mai daraja a gaban Ubangiji shi ne mutuwar tsarkakansa.
[is] precious In [the] eyes of Yahweh the death of faithful [people] his.
16 Ya Ubangiji, da gaske ni bawanka ne; ni bawanka ne, ɗan baiwarka; ka’yantar da ni daga sarƙoƙi.
I beg you O Yahweh for I [am] servant your I [am] servant your [the] son of maidservant your you have loosened fetters my.
17 Zan yi hadayar godiya gare ka in kuma kira bisa sunan Ubangiji.
To you I will sacrifice a sacrifice of thanksgiving and on [the] name of Yahweh I will call.
18 Zan cika alkawurana ga Ubangiji a gaban dukan mutanensa,
Vows my to Yahweh I will pay before please all people his.
19 a filayen gidan Ubangiji, a tsakiyarki, ya Urushalima. Yabi Ubangiji.
In [the] courts of - [the] house of Yahweh in [the] midst of you O Jerusalem praise Yahweh.