< Zabura 116 >
1 Ina ƙaunar Ubangiji, gama ya ji muryata; ya ji kukata ta neman jinƙai.
I 'ahav ·affectionately love· Adonai, because he sh'ma ·hears obeys· my voice, and my cries for mercy.
2 Domin ya juye kunnensa gare ni, zan kira gare shi muddin ina da rai.
Because he has turned his ear to me, therefore I will call on him as long as I live.
3 Igiyoyin mutuwa sun shaƙe ni, wahalar kabari sun zo a kaina; na cika da wahala da ɓacin rai. (Sheol )
The cords of death surrounded me, the pains of Sheol ·Place of the dead· got a hold of me. I found trouble and sorrow. (Sheol )
4 Sai na kira ga sunan Ubangiji na ce, “Ya Ubangiji, ka cece ni!”
Then I called on Adonai’s name: “Adonai, I beg you, deliver my soul.”
5 Ubangiji mai alheri ne da kuma mai adalci; Allahnmu yana cike da tausayi.
Adonai is gracious and righteous. Yes, our God is racham ·merciful love·.
6 Ubangiji yana tsare masu tawali’u; sa’ad da nake cikin tsananin bukata, ya cece ni.
Adonai preserves the simple. I was brought low, and he saved me.
7 Ka kwantar da hankali, ya raina, gama Ubangiji mai alheri ne a gare ka.
Teshuvah ·Completely return· to your rest, my soul, for Adonai has dealt bountifully with you.
8 Gama kai, ya Ubangiji, ka ceci raina daga mutuwa, idanuna daga hawaye, ƙafafuna daga tuntuɓe,
For you have delivered my soul from death, my eyes from tears, and my feet from falling.
9 don in iya tafiya a gaban Ubangiji a ƙasar masu rai.
I will walk before Adonai in the land of the living.
10 Na gaskata, saboda haka na ce, “An azabtar da ni ƙwarai.”
I trusted, therefore I said, “I was greatly afflicted.”
11 Kuma cikin rikicewana na ce, “Dukan mutane maƙaryata ne.”
I said in my haste, “All men are liars.”
12 Yaya zan sāka wa Ubangiji saboda dukan alherinsa gare ni?
What will I give to Adonai for all his benefits toward me?
13 Zan daga kwaf na ceto in kuma kira ga sunan Ubangiji.
I will take the cup of yishu'ah ·salvation·, and call on Adonai’s name.
14 Zan cika alkawurana ga Ubangiji a gaban dukan mutanensa.
I will pay my vows to Adonai, yes, in the presence of all his people.
15 Abu mai daraja a gaban Ubangiji shi ne mutuwar tsarkakansa.
Precious in Adonai’s sight is the death of his saints.
16 Ya Ubangiji, da gaske ni bawanka ne; ni bawanka ne, ɗan baiwarka; ka’yantar da ni daga sarƙoƙi.
Adonai, truly I am your servant. I am your servant, the son of your servant. You have freed me from my chains.
17 Zan yi hadayar godiya gare ka in kuma kira bisa sunan Ubangiji.
I will offer to you the sacrifice of thanksgiving, and will call on Adonai’s name.
18 Zan cika alkawurana ga Ubangiji a gaban dukan mutanensa,
I will pay my vows to Adonai, yes, in the presence of all his people,
19 a filayen gidan Ubangiji, a tsakiyarki, ya Urushalima. Yabi Ubangiji.
in the courts of Adonai’s house, in the middle of you, Jerusalem [City of peace]. Halleluyah ·praise Yah·!