< Zabura 116 >

1 Ina ƙaunar Ubangiji, gama ya ji muryata; ya ji kukata ta neman jinƙai.
It is lovely to me that the Lord heareth my voice, my supplications.
2 Domin ya juye kunnensa gare ni, zan kira gare shi muddin ina da rai.
For he hath inclined his ear unto me: therefore throughout all my days will I call on him.
3 Igiyoyin mutuwa sun shaƙe ni, wahalar kabari sun zo a kaina; na cika da wahala da ɓacin rai. (Sheol h7585)
The bands of death had compassed me, and the pangs of the nether world had overtaken me; I had met with distress and sorrow: (Sheol h7585)
4 Sai na kira ga sunan Ubangiji na ce, “Ya Ubangiji, ka cece ni!”
I then called on the name of the Lord, I beseech thee, O Lord, release my soul.
5 Ubangiji mai alheri ne da kuma mai adalci; Allahnmu yana cike da tausayi.
Gracious is the Lord, and righteous; and our God is merciful.
6 Ubangiji yana tsare masu tawali’u; sa’ad da nake cikin tsananin bukata, ya cece ni.
The Lord preserveth the simple: I was in misery, and he helped me.
7 Ka kwantar da hankali, ya raina, gama Ubangiji mai alheri ne a gare ka.
Return, O my soul, unto thy rest; for the Lord hath dealt bountifully with thee.
8 Gama kai, ya Ubangiji, ka ceci raina daga mutuwa, idanuna daga hawaye, ƙafafuna daga tuntuɓe,
For thou hast delivered my soul from death, my eyes from tears, my feet from falling.
9 don in iya tafiya a gaban Ubangiji a ƙasar masu rai.
I will walk before the Lord in the land of life.
10 Na gaskata, saboda haka na ce, “An azabtar da ni ƙwarai.”
I believe, therefore will I speak: I was greatly afflicted;
11 Kuma cikin rikicewana na ce, “Dukan mutane maƙaryata ne.”
I indeed said in my despondency, Every man is a liar.
12 Yaya zan sāka wa Ubangiji saboda dukan alherinsa gare ni?
What shall I give in return unto the Lord for all his bounties toward me?
13 Zan daga kwaf na ceto in kuma kira ga sunan Ubangiji.
The cup of salvation will I lift up, and on the name of the Lord will I call.
14 Zan cika alkawurana ga Ubangiji a gaban dukan mutanensa.
My vows will I pay unto the Lord, yea, in the presence of all his people.
15 Abu mai daraja a gaban Ubangiji shi ne mutuwar tsarkakansa.
Grievous in the eyes of the Lord is the death of his pious ones.
16 Ya Ubangiji, da gaske ni bawanka ne; ni bawanka ne, ɗan baiwarka; ka’yantar da ni daga sarƙoƙi.
O Lord, truly am I thy servant, I am thy servant, —the son of thy handmaid: thou hast loosened my fetters.
17 Zan yi hadayar godiya gare ka in kuma kira bisa sunan Ubangiji.
Unto thee will I offer the sacrifice of thanksgiving, and on the name of the Lord will I call.
18 Zan cika alkawurana ga Ubangiji a gaban dukan mutanensa,
My vows will I pay unto the Lord, yea, in the presence of all his people,
19 a filayen gidan Ubangiji, a tsakiyarki, ya Urushalima. Yabi Ubangiji.
In the courts of the house of the Lord, in thy midst, O Jerusalem. Hallelujah.

< Zabura 116 >