< Zabura 116 >

1 Ina ƙaunar Ubangiji, gama ya ji muryata; ya ji kukata ta neman jinƙai.
Ljubim Jahvu jer čuje vapaj molitve moje:
2 Domin ya juye kunnensa gare ni, zan kira gare shi muddin ina da rai.
uho svoje prignu k meni u dan u koji ga zazvah.
3 Igiyoyin mutuwa sun shaƙe ni, wahalar kabari sun zo a kaina; na cika da wahala da ɓacin rai. (Sheol h7585)
Užeta smrti sapeše me, stegoše me zamke Podzemlja, snašla me muka i tjeskoba. (Sheol h7585)
4 Sai na kira ga sunan Ubangiji na ce, “Ya Ubangiji, ka cece ni!”
Tada zazvah ime Jahvino: “O Jahve, spasi život moj!”
5 Ubangiji mai alheri ne da kuma mai adalci; Allahnmu yana cike da tausayi.
Dobrostiv je Jahve i pravedan, pun sućuti je Bog naš.
6 Ubangiji yana tsare masu tawali’u; sa’ad da nake cikin tsananin bukata, ya cece ni.
Jahve čuva bezazlene: u nevolji bijah, on me izbavi.
7 Ka kwantar da hankali, ya raina, gama Ubangiji mai alheri ne a gare ka.
Vrati se, dušo moja, u svoj pokoj, jer Jahve je dobrotvor tvoj.
8 Gama kai, ya Ubangiji, ka ceci raina daga mutuwa, idanuna daga hawaye, ƙafafuna daga tuntuɓe,
On mi život od smrti izbavi, oči moje od suza, noge od pada.
9 don in iya tafiya a gaban Ubangiji a ƙasar masu rai.
Hodit ću pred licem Jahvinim u zemlji živih.
10 Na gaskata, saboda haka na ce, “An azabtar da ni ƙwarai.”
Ja vjerujem i kada kažem: “Nesretan sam veoma.”
11 Kuma cikin rikicewana na ce, “Dukan mutane maƙaryata ne.”
U smetenosti svojoj rekoh: “Svaki je čovjek lažac!”
12 Yaya zan sāka wa Ubangiji saboda dukan alherinsa gare ni?
Što da uzvratim Jahvi za sve što mi je učinio?
13 Zan daga kwaf na ceto in kuma kira ga sunan Ubangiji.
Uzet ću čašu spasenja i zazvat ću ime Jahvino.
14 Zan cika alkawurana ga Ubangiji a gaban dukan mutanensa.
Izvršit ću Jahvi zavjete svoje pred svim pukom njegovim.
15 Abu mai daraja a gaban Ubangiji shi ne mutuwar tsarkakansa.
Dragocjena je u očima Jahvinim smrt pobožnika njegovih.
16 Ya Ubangiji, da gaske ni bawanka ne; ni bawanka ne, ɗan baiwarka; ka’yantar da ni daga sarƙoƙi.
Jahve, tvoj sam sluga, tvoj sluga, sin sluškinje tvoje: ti si razriješio okove moje.
17 Zan yi hadayar godiya gare ka in kuma kira bisa sunan Ubangiji.
Tebi ću prinijeti žrtve zahvalne, zazvat ću ime Jahvino.
18 Zan cika alkawurana ga Ubangiji a gaban dukan mutanensa,
Izvršit ću Jahvi zavjete svoje pred svim pukom njegovim,
19 a filayen gidan Ubangiji, a tsakiyarki, ya Urushalima. Yabi Ubangiji.
u predvorjima Doma Jahvina, posred tebe, Jeruzaleme!

< Zabura 116 >