< Zabura 115 >
1 Ba gare mu ba, ya Ubangiji, ba gare mu ba amma ga sunanka yă sami ɗaukaka, saboda ƙaunarka da amincinka.
Icke åt oss, HERRE, icke åt oss, utan åt ditt namn giv äran, för din nåds, för din sannings skull.
2 Me ya sa al’ummai suke cewa, “Ina Allahnsu?”
Varför skulle hedningarna få säga: "Var är nu deras Gud?"
3 Allahnmu yana a sama; yana yin duk abin da ya ga dama.
Vår Gud är ju i himmelen; han kan göra allt vad han vill.
4 Amma gumakansu azurfa da zinariya ne, da hannuwan mutane suka yi.
Men deras avgudar äro silver och guld, verk av människohänder.
5 Suna da bakuna, amma ba sa magana, idanu, amma ba sa gani;
De hava mun och tala icke, de hava ögon och se icke,
6 suna da kunnuwa, amma ba sa ji, hanci, amma ba sa jin ƙanshi
de hava öron och höra icke, de hava näsa och lukta icke.
7 suna da hannuwa, amma ba sa iya taɓa kome, ƙafafu, amma ba sa iya tafiya; ba sa iya ce wani abu da maƙogwaronsu.
Med sina händer taga de icke, med sina fötter gå de icke; de hava intet ljud i sin strupe.
8 Masu yinsu za su zama kamar su, haka kuma zai kasance da duk wanda ya dogara da su.
De som hava gjort dem skola bliva dem lika, ja, alla som förtrösta på dem.
9 Ya gidan Isra’ila, ku dogara ga Ubangiji, shi ne mai taimakonsu da garkuwarsu.
I av Israel, förtrösten på HERREN. Ja, han är deras hjälp och sköld.
10 Ya gidan Haruna, ku dogara ga Ubangiji, shi ne mai taimakonsu da garkuwarsu.
I av Arons hus, förtrösten på HERREN. Ja, han är deras hjälp och sköld.
11 Ku da kuke tsoronsa, ku dogara ga Ubangiji, shi ne mai taimakonsu da garkuwarsu.
I som frukten HERREN, förtrösten på HERREN. Ja, han är deras hjälp och sköld.
12 Ubangiji yakan tuna da mu zai kuma albarkace mu. Zai albarkace gidan Isra’ila, zai albarkace gidan Haruna,
HERREN har tänkt på oss, han skall välsigna, han skall välsigna Israels hus, han skall välsigna Arons hus,
13 zai albarkace waɗanda suke tsoron Ubangiji, manya da ƙanana duka.
han skall välsigna dem som frukta HERREN, de små såväl som de stora.
14 Bari Ubangiji yă sa ku ƙaru, da ku da’ya’yanku.
Ja, HERREN föröke eder, seder själva och edra barn.
15 Bari Ubangiji yă albarkace ku, shi Mahalicci sama da ƙasa.
Varen välsignade av HERREN, av honom som har gjort himmel och jord.
16 Saman sammai na Ubangiji ne, amma ya ba da duniya ga mutum.
Himmelen är HERRENS himmel, och jorden har han givit åt människors barn.
17 Ba matattu ba ne masu yabon Ubangiji, waɗanda suke gangara zuwa wurin da ake shiru;
De döda prisa icke HERREN, ingen som har farit ned i det tysta.
18 mu ne masu ɗaukaka Ubangiji, yanzu da har abada kuma. Yabi Ubangiji.
Men vi, vi skola lova HERREN från nu och till evig tid. Halleluja!