< Zabura 115 >

1 Ba gare mu ba, ya Ubangiji, ba gare mu ba amma ga sunanka yă sami ɗaukaka, saboda ƙaunarka da amincinka.
Sio kwetu, Yahwe, sio kwetu, bali kwa jina lako ulete heshima, kwa ajili ya uaminifu wa agano lako na uaminifu wako.
2 Me ya sa al’ummai suke cewa, “Ina Allahnsu?”
Kwa nini mataifa yalazimike kusema, “Yuko wapi Mungu wako?”
3 Allahnmu yana a sama; yana yin duk abin da ya ga dama.
Mungu wetu aliye mbinguni; hufanya chochote apendacho.
4 Amma gumakansu azurfa da zinariya ne, da hannuwan mutane suka yi.
Sanamu za mataifa ni fedha na dhahabu, kazi ya mikono ya wanadamu.
5 Suna da bakuna, amma ba sa magana, idanu, amma ba sa gani;
Sanamu hizo zina vinywa, lakini haziongei; zina macho, lakini hazioni;
6 suna da kunnuwa, amma ba sa ji, hanci, amma ba sa jin ƙanshi
zina masikio, lakini hazisikii; zina pua lakini hazinusi.
7 suna da hannuwa, amma ba sa iya taɓa kome, ƙafafu, amma ba sa iya tafiya; ba sa iya ce wani abu da maƙogwaronsu.
Sanamu hizo zina mikono, lakini hazishiki; zina miguu, lakini haziwezi kutembea; wala haziongei kutoka viywani mwao.
8 Masu yinsu za su zama kamar su, haka kuma zai kasance da duk wanda ya dogara da su.
Wale wanao zitengeneza wanafanana nazo, vile vile yeyote anaye amini katika hizo.
9 Ya gidan Isra’ila, ku dogara ga Ubangiji, shi ne mai taimakonsu da garkuwarsu.
Israeli, amini katika Yahwe; yeye ni msaada wako na ngao yako.
10 Ya gidan Haruna, ku dogara ga Ubangiji, shi ne mai taimakonsu da garkuwarsu.
Nyumba ya Haruni, amini katika Yahwe; yeye ni msaada wako na ngao yako.
11 Ku da kuke tsoronsa, ku dogara ga Ubangiji, shi ne mai taimakonsu da garkuwarsu.
Ninyi mnao mheshumu Yahwe, mwamini yeye; yeye ni msaada wenu na ngao yenu.
12 Ubangiji yakan tuna da mu zai kuma albarkace mu. Zai albarkace gidan Isra’ila, zai albarkace gidan Haruna,
Yahwe hutukumbuka sisi na atatubariki; ataibariki familia ya Israeli; atabariki familia ya Haruni.
13 zai albarkace waɗanda suke tsoron Ubangiji, manya da ƙanana duka.
Atawabariki wale wanao muheshimu yeye, wote vijana na wazee.
14 Bari Ubangiji yă sa ku ƙaru, da ku da’ya’yanku.
Yahwe na awaongeze ninyi zaidi na zaidi, ninyi pamoja na watoto wenu.
15 Bari Ubangiji yă albarkace ku, shi Mahalicci sama da ƙasa.
Yahwe na awabariki, aliyeziumba mbingu na nchi.
16 Saman sammai na Ubangiji ne, amma ya ba da duniya ga mutum.
Mbingu ni za Yahwe; lakini nchi amewapa wanadamu.
17 Ba matattu ba ne masu yabon Ubangiji, waɗanda suke gangara zuwa wurin da ake shiru;
Wafu hawamsifu Yahwe, wala wote washukao chini kwenye ukimya;
18 mu ne masu ɗaukaka Ubangiji, yanzu da har abada kuma. Yabi Ubangiji.
bali tutamtukuza Yahwe sasa na hata milele. Msifuni Yahwe.

< Zabura 115 >