< Zabura 115 >
1 Ba gare mu ba, ya Ubangiji, ba gare mu ba amma ga sunanka yă sami ɗaukaka, saboda ƙaunarka da amincinka.
No a nosotros, oh Señor, no a nosotros, sino a tu nombre démosle gloria, por tu misericordia y tu fe inmutable.
2 Me ya sa al’ummai suke cewa, “Ina Allahnsu?”
¿Por qué dirán las naciones: Dónde está ahora su Dios?
3 Allahnmu yana a sama; yana yin duk abin da ya ga dama.
Mas nuestro Dios está en el cielo; hizo todo lo que le agradaba.
4 Amma gumakansu azurfa da zinariya ne, da hannuwan mutane suka yi.
Sus imágenes son plata y oro, obra de manos de hombres.
5 Suna da bakuna, amma ba sa magana, idanu, amma ba sa gani;
Tienen bocas, pero no voz; tienen ojos, pero no ven;
6 suna da kunnuwa, amma ba sa ji, hanci, amma ba sa jin ƙanshi
Tienen oídos, pero no oyen; tienen narices, pero no tienen olfato;
7 suna da hannuwa, amma ba sa iya taɓa kome, ƙafafu, amma ba sa iya tafiya; ba sa iya ce wani abu da maƙogwaronsu.
Tienen manos sin más no palpan. y pies sin poder de caminar; y ningún sonido sale de su garganta.
8 Masu yinsu za su zama kamar su, haka kuma zai kasance da duk wanda ya dogara da su.
Los que los hacen son como ellos; y también lo es cada uno que pone su fe en ellos.
9 Ya gidan Isra’ila, ku dogara ga Ubangiji, shi ne mai taimakonsu da garkuwarsu.
Israel, ten fe en el Señor; él es tu ayuda y tu coraza.
10 Ya gidan Haruna, ku dogara ga Ubangiji, shi ne mai taimakonsu da garkuwarsu.
Casa de Aarón, ten fe en el Señor; él es tu ayuda y tu escudo.
11 Ku da kuke tsoronsa, ku dogara ga Ubangiji, shi ne mai taimakonsu da garkuwarsu.
Adoradores del Señor, ten fe en el Señor; él es tu ayuda y tu escudo.
12 Ubangiji yakan tuna da mu zai kuma albarkace mu. Zai albarkace gidan Isra’ila, zai albarkace gidan Haruna,
El Señor nos ha tenido en cuenta y nos dará su bendición; él enviará bendiciones sobre la casa de Israel y sobre la casa de Aarón.
13 zai albarkace waɗanda suke tsoron Ubangiji, manya da ƙanana duka.
Él enviará bendiciones sobre los adoradores del Señor, sobre los pequeños y sobre los grandes.
14 Bari Ubangiji yă sa ku ƙaru, da ku da’ya’yanku.
Que el Señor les dé a ustedes y a sus hijos un mayor aumento.
15 Bari Ubangiji yă albarkace ku, shi Mahalicci sama da ƙasa.
Que tengas la bendición del Señor, que hizo el cielo y la tierra.
16 Saman sammai na Ubangiji ne, amma ya ba da duniya ga mutum.
Los cielos son del Señor; pero la tierra la ha dado a los hijos de los hombres.
17 Ba matattu ba ne masu yabon Ubangiji, waɗanda suke gangara zuwa wurin da ake shiru;
Los muertos no alaban al Señor; o aquellos que descienden al inframundo.
18 mu ne masu ɗaukaka Ubangiji, yanzu da har abada kuma. Yabi Ubangiji.
Pero alabaremos al Señor ahora y para siempre. Alabado sea el Señor.