< Zabura 115 >

1 Ba gare mu ba, ya Ubangiji, ba gare mu ba amma ga sunanka yă sami ɗaukaka, saboda ƙaunarka da amincinka.
No a nosotros, oh Yavé, No a nosotros, Sino a tu Nombre da gloria, Por tu misericordia y por tu verdad.
2 Me ya sa al’ummai suke cewa, “Ina Allahnsu?”
¿Por qué deben decir los gentiles: Dónde está su ʼElohim?
3 Allahnmu yana a sama; yana yin duk abin da ya ga dama.
Nuestro ʼElohim está en el cielo. Hizo todo lo que quiso.
4 Amma gumakansu azurfa da zinariya ne, da hannuwan mutane suka yi.
Los ídolos de ellos son de plata y oro, Obra de manos de hombres.
5 Suna da bakuna, amma ba sa magana, idanu, amma ba sa gani;
Tienen bocas, pero no hablan. Tienen ojos, pero no ven.
6 suna da kunnuwa, amma ba sa ji, hanci, amma ba sa jin ƙanshi
Tienen orejas, pero no oyen. Tienen fosas nasales, pero no perciben olor.
7 suna da hannuwa, amma ba sa iya taɓa kome, ƙafafu, amma ba sa iya tafiya; ba sa iya ce wani abu da maƙogwaronsu.
Tienen manos, pero no palpan. Tienen pies, pero no andan. No hablan con su garganta.
8 Masu yinsu za su zama kamar su, haka kuma zai kasance da duk wanda ya dogara da su.
Los que los hacen Y todos los que confían en ellos Son semejantes a ellos.
9 Ya gidan Isra’ila, ku dogara ga Ubangiji, shi ne mai taimakonsu da garkuwarsu.
¡Oh Israel, confía en Yavé! Él es tu Ayuda y Escudo.
10 Ya gidan Haruna, ku dogara ga Ubangiji, shi ne mai taimakonsu da garkuwarsu.
¡Oh casa de Aarón, confía en Yavé! Él es tu Ayuda y tu Escudo.
11 Ku da kuke tsoronsa, ku dogara ga Ubangiji, shi ne mai taimakonsu da garkuwarsu.
Los que temen a Yavé, Confíen en Yavé. Él es su Ayuda y su Escudo.
12 Ubangiji yakan tuna da mu zai kuma albarkace mu. Zai albarkace gidan Isra’ila, zai albarkace gidan Haruna,
Yavé se acordó de nosotros, Él nos bendecirá. Bendecirá a la casa de Israel, Bendecirá a la casa de Aarón.
13 zai albarkace waɗanda suke tsoron Ubangiji, manya da ƙanana duka.
Bendecirá a los que temen a Yavé, A los pequeños y a los grandes.
14 Bari Ubangiji yă sa ku ƙaru, da ku da’ya’yanku.
Yavé aumentará bendición Sobre ustedes y sobre sus hijos.
15 Bari Ubangiji yă albarkace ku, shi Mahalicci sama da ƙasa.
Benditos sean ustedes por Yavé, Quien hizo el cielo y la tierra.
16 Saman sammai na Ubangiji ne, amma ya ba da duniya ga mutum.
El cielo es el cielo de Yavé, Pero Él dio la tierra a los hijos de [los] hombres.
17 Ba matattu ba ne masu yabon Ubangiji, waɗanda suke gangara zuwa wurin da ake shiru;
No alaban los muertos a YA, Ni cualquiera que baja al silencio.
18 mu ne masu ɗaukaka Ubangiji, yanzu da har abada kuma. Yabi Ubangiji.
Pero nosotros bendecimos a YA desde ahora y para siempre. ¡Aleluya!

< Zabura 115 >