< Zabura 115 >
1 Ba gare mu ba, ya Ubangiji, ba gare mu ba amma ga sunanka yă sami ɗaukaka, saboda ƙaunarka da amincinka.
Nicht uns, HERR, nicht uns, sondern deinem Namen gib Ehre um deine Gnade und Wahrheit!
2 Me ya sa al’ummai suke cewa, “Ina Allahnsu?”
Warum sollen die Heiden sagen: Wo ist nun ihr Gott?
3 Allahnmu yana a sama; yana yin duk abin da ya ga dama.
Aber unser Gott ist im Himmel; er kann schaffen, was er will.
4 Amma gumakansu azurfa da zinariya ne, da hannuwan mutane suka yi.
Jener Götzen aber sind Silber und Gold, von Menschenhänden gemacht.
5 Suna da bakuna, amma ba sa magana, idanu, amma ba sa gani;
Sie haben Mäuler und reden nicht; sie haben Augen und sehen nicht;
6 suna da kunnuwa, amma ba sa ji, hanci, amma ba sa jin ƙanshi
sie haben Ohren und hören nicht; sie haben Nasen und riechen nicht;
7 suna da hannuwa, amma ba sa iya taɓa kome, ƙafafu, amma ba sa iya tafiya; ba sa iya ce wani abu da maƙogwaronsu.
sie haben Hände und greifen nicht; Füße haben sie und gehen nicht und reden nicht durch ihren Hals.
8 Masu yinsu za su zama kamar su, haka kuma zai kasance da duk wanda ya dogara da su.
Die solche machen, sind gleich also, und alle, die auf sie hoffen.
9 Ya gidan Isra’ila, ku dogara ga Ubangiji, shi ne mai taimakonsu da garkuwarsu.
Aber Israel hoffe auf den HERRN; der ist ihre Hilfe und Schild.
10 Ya gidan Haruna, ku dogara ga Ubangiji, shi ne mai taimakonsu da garkuwarsu.
Das Haus Aaron hoffe auf den HERRN; der ist ihre Hilfe und Schild.
11 Ku da kuke tsoronsa, ku dogara ga Ubangiji, shi ne mai taimakonsu da garkuwarsu.
Die den HERRN fürchten, hoffen auch auf den HERRN; der ist ihre Hilfe und Schild.
12 Ubangiji yakan tuna da mu zai kuma albarkace mu. Zai albarkace gidan Isra’ila, zai albarkace gidan Haruna,
Der HERR denket an uns und segnet uns. Er segnet das Haus Israel; er segnet das Haus Aaron;
13 zai albarkace waɗanda suke tsoron Ubangiji, manya da ƙanana duka.
er segnet, die den HERRN fürchten, beide Kleine und Große.
14 Bari Ubangiji yă sa ku ƙaru, da ku da’ya’yanku.
Der HERR segne euch je mehr und mehr, euch und eure Kinder!
15 Bari Ubangiji yă albarkace ku, shi Mahalicci sama da ƙasa.
Ihr seid die Gesegneten des HERRN, der Himmel und Erde gemacht hat.
16 Saman sammai na Ubangiji ne, amma ya ba da duniya ga mutum.
Der Himmel allenthalben ist des HERRN; aber die Erde hat er den Menschenkindern gegeben.
17 Ba matattu ba ne masu yabon Ubangiji, waɗanda suke gangara zuwa wurin da ake shiru;
Die Toten werden dich, HERR, nicht loben, noch die hinunterfahren in die Stille,
18 mu ne masu ɗaukaka Ubangiji, yanzu da har abada kuma. Yabi Ubangiji.
sondern wir loben den HERRN von nun an bis in Ewigkeit. Halleluja!