< Zabura 115 >

1 Ba gare mu ba, ya Ubangiji, ba gare mu ba amma ga sunanka yă sami ɗaukaka, saboda ƙaunarka da amincinka.
Nicht uns, Jehova, nicht uns, sondern deinem Namen gib Ehre, um deiner Güte, um deiner Wahrheit willen!
2 Me ya sa al’ummai suke cewa, “Ina Allahnsu?”
Warum sollen die Nationen sagen: Wo ist denn ihr Gott?
3 Allahnmu yana a sama; yana yin duk abin da ya ga dama.
Aber unser Gott ist in den Himmeln; alles was ihm wohlgefällt, tut er.
4 Amma gumakansu azurfa da zinariya ne, da hannuwan mutane suka yi.
Ihre Götzen sind Silber und Gold, ein Werk von Menschenhänden.
5 Suna da bakuna, amma ba sa magana, idanu, amma ba sa gani;
Einen Mund haben sie und reden nicht; Augen haben sie und sehen nicht;
6 suna da kunnuwa, amma ba sa ji, hanci, amma ba sa jin ƙanshi
Ohren haben sie und hören nicht; eine Nase haben sie und riechen nicht;
7 suna da hannuwa, amma ba sa iya taɓa kome, ƙafafu, amma ba sa iya tafiya; ba sa iya ce wani abu da maƙogwaronsu.
Sie haben Hände und tasten nicht, Füße, und sie gehen nicht; keinen Laut geben sie mit ihrer Kehle.
8 Masu yinsu za su zama kamar su, haka kuma zai kasance da duk wanda ya dogara da su.
Ihnen gleich sind die, die sie machen, ein jeder, der auf sie vertraut.
9 Ya gidan Isra’ila, ku dogara ga Ubangiji, shi ne mai taimakonsu da garkuwarsu.
Israel, vertraue auf Jehova! ihre Hülfe und ihr Schild ist er.
10 Ya gidan Haruna, ku dogara ga Ubangiji, shi ne mai taimakonsu da garkuwarsu.
Haus Aaron, vertrauet auf Jehova! ihre Hülfe und ihr Schild ist er.
11 Ku da kuke tsoronsa, ku dogara ga Ubangiji, shi ne mai taimakonsu da garkuwarsu.
Ihr, die ihr Jehova fürchtet, vertrauet auf Jehova! ihre Hülfe und ihr Schild ist er.
12 Ubangiji yakan tuna da mu zai kuma albarkace mu. Zai albarkace gidan Isra’ila, zai albarkace gidan Haruna,
Jehova hat unser gedacht, er wird segnen; er wird segnen das Haus Israel, segnen das Haus Aaron.
13 zai albarkace waɗanda suke tsoron Ubangiji, manya da ƙanana duka.
Er wird segnen, die Jehova fürchten, die Kleinen mit den Großen.
14 Bari Ubangiji yă sa ku ƙaru, da ku da’ya’yanku.
Jehova wird zu euch hinzufügen, zu euch und zu euren Kindern.
15 Bari Ubangiji yă albarkace ku, shi Mahalicci sama da ƙasa.
Gesegnet seid ihr von Jehova, der Himmel und Erde gemacht hat.
16 Saman sammai na Ubangiji ne, amma ya ba da duniya ga mutum.
Die Himmel sind die Himmel Jehovas, die Erde aber hat er den Menschenkindern gegeben.
17 Ba matattu ba ne masu yabon Ubangiji, waɗanda suke gangara zuwa wurin da ake shiru;
Die Toten werden Jehova [Hebr. Jah] nicht loben, noch alle, die zum Schweigen hinabfahren;
18 mu ne masu ɗaukaka Ubangiji, yanzu da har abada kuma. Yabi Ubangiji.
Wir aber, wir werden Jehova [Hebr. Jah] preisen von nun an bis in Ewigkeit. Lobet Jehova! [Hallelujah!]

< Zabura 115 >