< Zabura 115 >

1 Ba gare mu ba, ya Ubangiji, ba gare mu ba amma ga sunanka yă sami ɗaukaka, saboda ƙaunarka da amincinka.
Non point à nous, Éternel, non point à nous, mais à ton nom donne gloire, à cause de ta bonté, à cause de ta vérité.
2 Me ya sa al’ummai suke cewa, “Ina Allahnsu?”
Pourquoi diraient les nations: Où donc est leur Dieu?
3 Allahnmu yana a sama; yana yin duk abin da ya ga dama.
Notre Dieu, il est dans les cieux; il fait tout ce qu'il lui plaît.
4 Amma gumakansu azurfa da zinariya ne, da hannuwan mutane suka yi.
Leurs idoles sont de l'argent et de l'or, un ouvrage de mains d'homme.
5 Suna da bakuna, amma ba sa magana, idanu, amma ba sa gani;
Elles ont une bouche et ne parlent pas; elles ont des yeux, et ne voient pas.
6 suna da kunnuwa, amma ba sa ji, hanci, amma ba sa jin ƙanshi
Elles ont des oreilles, et n'entendent pas; elles ont un nez et ne sentent pas;
7 suna da hannuwa, amma ba sa iya taɓa kome, ƙafafu, amma ba sa iya tafiya; ba sa iya ce wani abu da maƙogwaronsu.
Des mains, et ne touchent pas; des pieds, et ne marchent pas; elles ne rendent aucun son de leur gosier.
8 Masu yinsu za su zama kamar su, haka kuma zai kasance da duk wanda ya dogara da su.
Ceux qui les font, et tous ceux qui s'y confient, leur deviendront semblables.
9 Ya gidan Isra’ila, ku dogara ga Ubangiji, shi ne mai taimakonsu da garkuwarsu.
Israël, confie-toi en l'Éternel! Il est leur aide et leur bouclier.
10 Ya gidan Haruna, ku dogara ga Ubangiji, shi ne mai taimakonsu da garkuwarsu.
Maison d'Aaron, confiez-vous en l'Éternel! Il est leur aide et leur bouclier.
11 Ku da kuke tsoronsa, ku dogara ga Ubangiji, shi ne mai taimakonsu da garkuwarsu.
Vous qui craignez l'Éternel, confiez-vous en l'Éternel! Il est leur aide et leur bouclier.
12 Ubangiji yakan tuna da mu zai kuma albarkace mu. Zai albarkace gidan Isra’ila, zai albarkace gidan Haruna,
L'Éternel s'est souvenu de nous; il bénira, il bénira la maison d'Israël; il bénira la maison d'Aaron.
13 zai albarkace waɗanda suke tsoron Ubangiji, manya da ƙanana duka.
Il bénira ceux qui craignent l'Éternel, tant les petits que les grands.
14 Bari Ubangiji yă sa ku ƙaru, da ku da’ya’yanku.
L'Éternel vous ajoutera des biens, à vous et à vos enfants.
15 Bari Ubangiji yă albarkace ku, shi Mahalicci sama da ƙasa.
Vous êtes bénis de l'Éternel, qui a fait les cieux et la terre.
16 Saman sammai na Ubangiji ne, amma ya ba da duniya ga mutum.
Quant aux cieux, les cieux sont à l'Éternel; mais il a donné la terre aux enfants des hommes.
17 Ba matattu ba ne masu yabon Ubangiji, waɗanda suke gangara zuwa wurin da ake shiru;
Les morts ne loueront point l'Éternel, ni tous ceux qui descendent au lieu du silence.
18 mu ne masu ɗaukaka Ubangiji, yanzu da har abada kuma. Yabi Ubangiji.
Mais nous, nous bénirons l'Éternel, dès maintenant et à toujours. Louez l'Éternel!

< Zabura 115 >