< Zabura 115 >

1 Ba gare mu ba, ya Ubangiji, ba gare mu ba amma ga sunanka yă sami ɗaukaka, saboda ƙaunarka da amincinka.
Non point à nous, ô Eternel! non point à nous, mais à ton Nom donne gloire pour l'amour de ta miséricorde, pour l'amour de ta vérité.
2 Me ya sa al’ummai suke cewa, “Ina Allahnsu?”
Pourquoi diraient les nations: où est maintenant leur Dieu?
3 Allahnmu yana a sama; yana yin duk abin da ya ga dama.
Certes notre Dieu est aux cieux; il fait tout ce qu'il lui plaît.
4 Amma gumakansu azurfa da zinariya ne, da hannuwan mutane suka yi.
Leurs dieux sont des [dieux] d'or et d'argent, un ouvrage des mains d'homme.
5 Suna da bakuna, amma ba sa magana, idanu, amma ba sa gani;
Ils ont une bouche, et ne parlent point; ils ont des yeux, et ne voient point;
6 suna da kunnuwa, amma ba sa ji, hanci, amma ba sa jin ƙanshi
Ils ont des oreilles, et n'entendent point; ils ont un nez, et ils n'[en] flairent point;
7 suna da hannuwa, amma ba sa iya taɓa kome, ƙafafu, amma ba sa iya tafiya; ba sa iya ce wani abu da maƙogwaronsu.
Des mains, et ils n'[en] touchent point; des pieds, et ils n'en marchent point; [et] ils ne rendent aucun son de leur gosier.
8 Masu yinsu za su zama kamar su, haka kuma zai kasance da duk wanda ya dogara da su.
Que ceux qui les font, [et] tous ceux qui s'y confient, leur soient faits semblables.
9 Ya gidan Isra’ila, ku dogara ga Ubangiji, shi ne mai taimakonsu da garkuwarsu.
Israël confie-toi en l'Eternel; il est le secours et le bouclier de ceux [qui se confient en lui].
10 Ya gidan Haruna, ku dogara ga Ubangiji, shi ne mai taimakonsu da garkuwarsu.
Maison d'Aaron, confiez-vous en l'Eternel; il est leur aide et leur bouclier.
11 Ku da kuke tsoronsa, ku dogara ga Ubangiji, shi ne mai taimakonsu da garkuwarsu.
Vous qui craignez l'Eternel, confiez-vous en l'Eternel; il est leur aide et leur bouclier.
12 Ubangiji yakan tuna da mu zai kuma albarkace mu. Zai albarkace gidan Isra’ila, zai albarkace gidan Haruna,
L'Eternel s'est souvenu de nous, il bénira, il bénira la maison d'Israël, il bénira la maison d'Aaron.
13 zai albarkace waɗanda suke tsoron Ubangiji, manya da ƙanana duka.
Il bénira ceux qui craignent l'Eternel, tant les petits que les grands.
14 Bari Ubangiji yă sa ku ƙaru, da ku da’ya’yanku.
L'Eternel ajoutera [bénédiction] sur vous, sur vous et sur vos enfants.
15 Bari Ubangiji yă albarkace ku, shi Mahalicci sama da ƙasa.
Vous êtes bénis de l'Eternel, qui a fait les cieux et la terre.
16 Saman sammai na Ubangiji ne, amma ya ba da duniya ga mutum.
Quant aux Cieux, les Cieux sont à l'Eternel; mais il a donné la terre aux enfants des hommes.
17 Ba matattu ba ne masu yabon Ubangiji, waɗanda suke gangara zuwa wurin da ake shiru;
Les morts, et tous ceux qui descendent où l'on ne dit plus mot, ne loueront point l'Eternel.
18 mu ne masu ɗaukaka Ubangiji, yanzu da har abada kuma. Yabi Ubangiji.
Mais nous, nous bénirons l'Eternel dès maintenant, et à toujours. Louez l'Eternel.

< Zabura 115 >