< Zabura 115 >
1 Ba gare mu ba, ya Ubangiji, ba gare mu ba amma ga sunanka yă sami ɗaukaka, saboda ƙaunarka da amincinka.
Pas à nous, Yahvé, pas à nous, mais que ton nom soit glorifié, pour ta bonté et pour l'amour de ta vérité.
2 Me ya sa al’ummai suke cewa, “Ina Allahnsu?”
Pourquoi les nations diraient-elles, « Où est leur Dieu, maintenant? »
3 Allahnmu yana a sama; yana yin duk abin da ya ga dama.
Mais notre Dieu est dans les cieux. Il fait ce qui lui plaît.
4 Amma gumakansu azurfa da zinariya ne, da hannuwan mutane suka yi.
Leurs idoles sont l'argent et l'or, le travail de la main de l'homme.
5 Suna da bakuna, amma ba sa magana, idanu, amma ba sa gani;
Ils ont une bouche, mais ils ne parlent pas. Ils ont des yeux, mais ils ne voient pas.
6 suna da kunnuwa, amma ba sa ji, hanci, amma ba sa jin ƙanshi
Ils ont des oreilles, mais ils n'entendent pas. Ils ont un nez, mais ils ne sentent pas.
7 suna da hannuwa, amma ba sa iya taɓa kome, ƙafafu, amma ba sa iya tafiya; ba sa iya ce wani abu da maƙogwaronsu.
Ils ont des mains, mais ils ne sentent pas. Ils ont des pieds, mais ils ne marchent pas, ils ne parlent pas non plus par la gorge.
8 Masu yinsu za su zama kamar su, haka kuma zai kasance da duk wanda ya dogara da su.
Ceux qui les font seront comme eux; oui, tous ceux qui ont confiance en eux.
9 Ya gidan Isra’ila, ku dogara ga Ubangiji, shi ne mai taimakonsu da garkuwarsu.
Israël, aie confiance en Yahvé! Il est leur aide et leur bouclier.
10 Ya gidan Haruna, ku dogara ga Ubangiji, shi ne mai taimakonsu da garkuwarsu.
Maison d'Aaron, ayez confiance en Yahvé! Il est leur aide et leur bouclier.
11 Ku da kuke tsoronsa, ku dogara ga Ubangiji, shi ne mai taimakonsu da garkuwarsu.
Vous qui craignez Yahvé, ayez confiance en Yahvé! Il est leur aide et leur bouclier.
12 Ubangiji yakan tuna da mu zai kuma albarkace mu. Zai albarkace gidan Isra’ila, zai albarkace gidan Haruna,
Yahvé se souvient de nous. Il nous bénira. Il bénira la maison d'Israël. Il bénira la maison d'Aaron.
13 zai albarkace waɗanda suke tsoron Ubangiji, manya da ƙanana duka.
Il bénira ceux qui craignent Yahvé, à la fois petites et grandes.
14 Bari Ubangiji yă sa ku ƙaru, da ku da’ya’yanku.
Que Yahvé vous augmente de plus en plus, vous et vos enfants.
15 Bari Ubangiji yă albarkace ku, shi Mahalicci sama da ƙasa.
Vous êtes bénis par Yahvé, qui a fait le ciel et la terre.
16 Saman sammai na Ubangiji ne, amma ya ba da duniya ga mutum.
Les cieux sont les cieux de l'Éternel, mais il a donné la terre aux enfants des hommes.
17 Ba matattu ba ne masu yabon Ubangiji, waɗanda suke gangara zuwa wurin da ake shiru;
Les morts ne louent pas Yahvé, ni ceux qui descendent dans le silence,
18 mu ne masu ɗaukaka Ubangiji, yanzu da har abada kuma. Yabi Ubangiji.
mais nous bénirons Yah, à partir de maintenant et pour toujours. Louez Yah!