< Zabura 115 >

1 Ba gare mu ba, ya Ubangiji, ba gare mu ba amma ga sunanka yă sami ɗaukaka, saboda ƙaunarka da amincinka.
Not unto us, O LORD! not unto us, But unto thy name, give glory, For thy mercy and thy truth's sake!
2 Me ya sa al’ummai suke cewa, “Ina Allahnsu?”
Why should the nations say, “Where is now their God?”
3 Allahnmu yana a sama; yana yin duk abin da ya ga dama.
Our God is in the heavens; He doeth whatever he pleaseth.
4 Amma gumakansu azurfa da zinariya ne, da hannuwan mutane suka yi.
Their idols are silver and gold, The work of men's hands:
5 Suna da bakuna, amma ba sa magana, idanu, amma ba sa gani;
They have mouths, but they speak not; Eyes have they, but they see not;
6 suna da kunnuwa, amma ba sa ji, hanci, amma ba sa jin ƙanshi
They have ears, but they hear not; Noses have they, but they smell not;
7 suna da hannuwa, amma ba sa iya taɓa kome, ƙafafu, amma ba sa iya tafiya; ba sa iya ce wani abu da maƙogwaronsu.
They have hands, but they handle not; They have feet, but they walk not; Nor do they speak with their throats.
8 Masu yinsu za su zama kamar su, haka kuma zai kasance da duk wanda ya dogara da su.
They who make them are like unto them; And so is every one that trusteth in them.
9 Ya gidan Isra’ila, ku dogara ga Ubangiji, shi ne mai taimakonsu da garkuwarsu.
O Israel! trust thou in the LORD! He is their help and their shield.
10 Ya gidan Haruna, ku dogara ga Ubangiji, shi ne mai taimakonsu da garkuwarsu.
O house of Aaron! trust ye in the LORD! He is their help and their shield.
11 Ku da kuke tsoronsa, ku dogara ga Ubangiji, shi ne mai taimakonsu da garkuwarsu.
Ye that fear the LORD trust in the LORD! He is their help and their shield.
12 Ubangiji yakan tuna da mu zai kuma albarkace mu. Zai albarkace gidan Isra’ila, zai albarkace gidan Haruna,
The LORD hath been mindful of us; he will bless us; He will bless the house of Israel; He will bless the house of Aaron.
13 zai albarkace waɗanda suke tsoron Ubangiji, manya da ƙanana duka.
He will bless them that fear the LORD, both small and great.
14 Bari Ubangiji yă sa ku ƙaru, da ku da’ya’yanku.
The LORD will increase you more and more, You and your children.
15 Bari Ubangiji yă albarkace ku, shi Mahalicci sama da ƙasa.
Blessed are ye of the LORD, Who made heaven and earth.
16 Saman sammai na Ubangiji ne, amma ya ba da duniya ga mutum.
The heaven is the LORD'S heaven; But the earth he hath given to the sons of men.
17 Ba matattu ba ne masu yabon Ubangiji, waɗanda suke gangara zuwa wurin da ake shiru;
The dead praise not the LORD, —No one who goeth down into silence.
18 mu ne masu ɗaukaka Ubangiji, yanzu da har abada kuma. Yabi Ubangiji.
But we will bless the LORD, From this time forth even for ever! Praise ye the LORD!

< Zabura 115 >