< Zabura 115 >

1 Ba gare mu ba, ya Ubangiji, ba gare mu ba amma ga sunanka yă sami ɗaukaka, saboda ƙaunarka da amincinka.
Not for our sake, O Lord, not for our sake, but unto thy name give glory, for the sake of thy kindness, for the sake of thy truth.
2 Me ya sa al’ummai suke cewa, “Ina Allahnsu?”
Wherefore should the nations say, Where now is their God?
3 Allahnmu yana a sama; yana yin duk abin da ya ga dama.
Whereas our God is in the heavens: whatsoever he desireth hath he done.
4 Amma gumakansu azurfa da zinariya ne, da hannuwan mutane suka yi.
Their idols are sliver and gold, the work of the hands of man.
5 Suna da bakuna, amma ba sa magana, idanu, amma ba sa gani;
A mouth they have, but speak not; eyes they have, but see not;
6 suna da kunnuwa, amma ba sa ji, hanci, amma ba sa jin ƙanshi
Ears they have, but hear not; a nose they have, but smell not.
7 suna da hannuwa, amma ba sa iya taɓa kome, ƙafafu, amma ba sa iya tafiya; ba sa iya ce wani abu da maƙogwaronsu.
They have hands, but they touch not; they have feet, but they walk not: nor do they give any utterance by their throat.
8 Masu yinsu za su zama kamar su, haka kuma zai kasance da duk wanda ya dogara da su.
Like them are those that make them, every one that trusteth in them.
9 Ya gidan Isra’ila, ku dogara ga Ubangiji, shi ne mai taimakonsu da garkuwarsu.
O Israel, trust thou in the Lord—he is their help and their shield.
10 Ya gidan Haruna, ku dogara ga Ubangiji, shi ne mai taimakonsu da garkuwarsu.
O house of Aaron, trust ye in the Lord—he is their help and their shield.
11 Ku da kuke tsoronsa, ku dogara ga Ubangiji, shi ne mai taimakonsu da garkuwarsu.
Ye that fear the Lord, trust ye in the Lord—he is their help and their shield.
12 Ubangiji yakan tuna da mu zai kuma albarkace mu. Zai albarkace gidan Isra’ila, zai albarkace gidan Haruna,
The Lord hath even been mindful of us, he will bless [us]; he will bless the house of Israel; he will bless the house of Aaron;
13 zai albarkace waɗanda suke tsoron Ubangiji, manya da ƙanana duka.
He will bless those that fear the Lord, the small together with the great.
14 Bari Ubangiji yă sa ku ƙaru, da ku da’ya’yanku.
May the Lord increase you more and more, you and your children.
15 Bari Ubangiji yă albarkace ku, shi Mahalicci sama da ƙasa.
Blessed are ye of the Lord, who made heaven and earth.
16 Saman sammai na Ubangiji ne, amma ya ba da duniya ga mutum.
The heavens are the heavens of the Lord; but the earth hath he given to the children of men.
17 Ba matattu ba ne masu yabon Ubangiji, waɗanda suke gangara zuwa wurin da ake shiru;
Not the dead can praise the Lord, nor all those that go down into the silence [of death].
18 mu ne masu ɗaukaka Ubangiji, yanzu da har abada kuma. Yabi Ubangiji.
But as for us, we will bless the Lord from this time forth and for evermore. Hallelujah.

< Zabura 115 >