< Zabura 114 >

1 Sa’ad da Isra’ila ya fito daga Masar, gidan Yaƙub daga mutane masu baƙon harshe,
En saliendo Israel de Egipto, la casa de Jacob del pueblo bárbaro,
2 Yahuda ya zama wuri mai tsarki na Allah, Isra’ila mallakarsa.
Judá fue por su santidad: Israel su señorío.
3 Teku ya kalla ya kuma gudu, Urdun ya juye da baya;
La mar vio, y huyó: el Jordán se volvió atrás.
4 duwatsu suka yi tsalle kamar raguna, tuddai kamar tumaki.
Los montes saltaron como carneros; los collados, como hijos de ovejas.
5 Me ya sa, ya teku, kika gudu, Ya Urdun, ka juya baya,
¿Qué tuviste mar, que huiste? ¿Jordán qué te volviste atrás?
6 ku duwatsu, kuka yi tsalle kamar raguna, ku tuddai, kamar tumaki?
¿Los montes saltasteis como carneros, y los collados como hijos de ovejas?
7 Ki yi rawar jiki, ya duniya, a gaban Ubangiji, a gaban Allah na Yaƙub,
A la presencia del Señor tiembla la tierra, a la presencia del Dios de Jacob.
8 wanda ya juye dutse ya zama tafki, dutse mai ƙarfi zuwa maɓulɓulan ruwa.
El cual tornó la peña en estanque de aguas, y la roca en fuente de aguas.

< Zabura 114 >