< Zabura 114 >

1 Sa’ad da Isra’ila ya fito daga Masar, gidan Yaƙub daga mutane masu baƙon harshe,
Då Israel drog ut or Egyptarland, Jakobs hus frå eit folk med framand tunga,
2 Yahuda ya zama wuri mai tsarki na Allah, Isra’ila mallakarsa.
då vart Juda hans heilagdom, Israel hans rike.
3 Teku ya kalla ya kuma gudu, Urdun ya juye da baya;
Havet såg det og flydde, Jordan drog seg attende.
4 duwatsu suka yi tsalle kamar raguna, tuddai kamar tumaki.
Fjelli hoppa som verar, haugarne som lamb.
5 Me ya sa, ya teku, kika gudu, Ya Urdun, ka juya baya,
Kva hev hendt deg, hav, at du flyr? du Jordan, at du dreg deg attende?
6 ku duwatsu, kuka yi tsalle kamar raguna, ku tuddai, kamar tumaki?
de fjell, at de hoppar som verar, de haugar som lamb?
7 Ki yi rawar jiki, ya duniya, a gaban Ubangiji, a gaban Allah na Yaƙub,
For Herrens åsyn må du skjelva, jord, for Jakobs Guds åsyn!
8 wanda ya juye dutse ya zama tafki, dutse mai ƙarfi zuwa maɓulɓulan ruwa.
Han som gjer berget til ein sjø, harde steinen til ei vatskjelda.

< Zabura 114 >